Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 1

حمٓ

HA MIM[1]


1- Duba Suratul Baqara aya ta 1, hashiya ta 8.


Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 2

وَٱلۡكِتَٰبِ ٱلۡمُبِينِ

Na rantse da Littafi mai bayyanawa (shi ne Alqur’ani)



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 3

إِنَّآ أَنزَلۡنَٰهُ فِي لَيۡلَةٖ مُّبَٰرَكَةٍۚ إِنَّا كُنَّا مُنذِرِينَ

Lalle Mu Muka saukar da shi a cikin dare mai albarka[1]. Lalle Mu Mun kasance Masu gargaxi


1- Shi ne daren Lailatul Qadari. Duba Suratul Qadri.


Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 4

فِيهَا يُفۡرَقُ كُلُّ أَمۡرٍ حَكِيمٍ

A cikinsa ne (daren) ake fasalta kowane tabbataccen al’amari (na wannan shekara)[1]


1- Watau al’amarin da ya shafi rabon arziqi da tsawon rai da sauran abubuwa da Allah ya qaddara za su faru a wannan shekarar.


Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 5

أَمۡرٗا مِّنۡ عِندِنَآۚ إِنَّا كُنَّا مُرۡسِلِينَ

Al’amari ne (da Muke fasaltawa) daga wurinmu. Lalle Mun kasance Mu ne Masu aikowa (da manzanni)



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 6

رَحۡمَةٗ مِّن رَّبِّكَۚ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلسَّمِيعُ ٱلۡعَلِيمُ

Don rahama daga Ubangijinka. Lalle shi Mai ji ne, Masani



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 7

رَبِّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَيۡنَهُمَآۖ إِن كُنتُم مُّوقِنِينَ

Ubangijin sammai da qasa da abin da yake tsakaninsu; idan kun kasance masu sakankancewa



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 8

لَآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَ يُحۡيِۦ وَيُمِيتُۖ رَبُّكُمۡ وَرَبُّ ءَابَآئِكُمُ ٱلۡأَوَّلِينَ

Babu wani abin bauta wa da gaskiya sai Shi, Shi ne Yake rayarwa Yake kuma kashewa; (Shi ne) Ubangijinku kuma Ubangijin iyayenku na farko



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 9

بَلۡ هُمۡ فِي شَكّٖ يَلۡعَبُونَ

A’a, su dai suna cikin shakka ne, suna wasanni



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 10

فَٱرۡتَقِبۡ يَوۡمَ تَأۡتِي ٱلسَّمَآءُ بِدُخَانٖ مُّبِينٖ

Sai ka saurari ranar da sama za ta zo da hayaqi bayyananne[1]


1- Shi ne hayaqi da idanuwansu za su riqa nuna musu, shi saboda tsananin yunwa.


Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 11

يَغۡشَى ٱلنَّاسَۖ هَٰذَا عَذَابٌ أَلِيمٞ

Zai lulluve (idanuwan) mutane; wannan azaba ce mai raxaxi



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 12

رَّبَّنَا ٱكۡشِفۡ عَنَّا ٱلۡعَذَابَ إِنَّا مُؤۡمِنُونَ

(Za su ce): “Ya Ubangijinmu, Ka yaye mana wannan azaba, lalle mu masu yin imani ne.”



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 13

أَنَّىٰ لَهُمُ ٱلذِّكۡرَىٰ وَقَدۡ جَآءَهُمۡ رَسُولٞ مُّبِينٞ

Ta ina wa’azi zai amfane su, alhali kuwa haqiqa Manzo mai bayani ya zo musu?



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 14

ثُمَّ تَوَلَّوۡاْ عَنۡهُ وَقَالُواْ مُعَلَّمٞ مَّجۡنُونٌ

Sannan suka juya masa baya suka ce: “Ai wani ne ya koya masa, (kuma shi) tavavve ne



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 15

إِنَّا كَاشِفُواْ ٱلۡعَذَابِ قَلِيلًاۚ إِنَّكُمۡ عَآئِدُونَ

Lalle Mu Masu yaye muku azabar ne xan lokaci kaxan. Lalle (kuma) ku masu komawa ne



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 16

يَوۡمَ نَبۡطِشُ ٱلۡبَطۡشَةَ ٱلۡكُبۡرَىٰٓ إِنَّا مُنتَقِمُونَ

(Ka tuna) ranar da za Mu damqe su babbar damqa[1], lalle Mu Masu sakawa ne


1- Ita ce ranar yaqin Badar lokacin da Allah ya damqi manyan kafiran Makka aka karkashe su.


Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 17

۞وَلَقَدۡ فَتَنَّا قَبۡلَهُمۡ قَوۡمَ فِرۡعَوۡنَ وَجَآءَهُمۡ رَسُولٞ كَرِيمٌ

Haqiqa kuma Mun jarrabi mutanen Fir’auna tun kafin su, kuma Manzo mai karamci ya zo musu



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 18

أَنۡ أَدُّوٓاْ إِلَيَّ عِبَادَ ٱللَّهِۖ إِنِّي لَكُمۡ رَسُولٌ أَمِينٞ

(Da cewa): “Ku ba ni bayin Allah (watau Banu Isra’ila); lalle ni Manzo ne amintacce a gare ku



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 19

وَأَن لَّا تَعۡلُواْ عَلَى ٱللَّهِۖ إِنِّيٓ ءَاتِيكُم بِسُلۡطَٰنٖ مُّبِينٖ

“Kuma kada ku yi wa Allah girman kai; lalle ni zan kawo muku hujjoji mabayyana



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 20

وَإِنِّي عُذۡتُ بِرَبِّي وَرَبِّكُمۡ أَن تَرۡجُمُونِ

“Kuma lalle ni ina neman tsari na Ubangijina kuma Ubangijinku, don kada ku jefe ni



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 21

وَإِن لَّمۡ تُؤۡمِنُواْ لِي فَٱعۡتَزِلُونِ

“Idan kuma ba ku yi imani da ni ba sai ku qyale ni.”



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 22

فَدَعَا رَبَّهُۥٓ أَنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ قَوۡمٞ مُّجۡرِمُونَ

Sai ya roqi Ubangijinsa cewa: “Lalle waxannan mutane ne masu manyan laifuka.”



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 23

فَأَسۡرِ بِعِبَادِي لَيۡلًا إِنَّكُم مُّتَّبَعُونَ

Sai (aka ce masa): “Ka tafi da bayina da daddare, lalle ku za a biyo bayanku



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 24

وَٱتۡرُكِ ٱلۡبَحۡرَ رَهۡوًاۖ إِنَّهُمۡ جُندٞ مُّغۡرَقُونَ

“Kuma ka bar kogi a tsaye cak (bayan tsallakewa); lalle su runduna ne da za a nutsar.”



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 25

كَمۡ تَرَكُواْ مِن جَنَّـٰتٖ وَعُيُونٖ

Sun bar gonaki da kuma idanuwan ruwa masu yawa



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 26

وَزُرُوعٖ وَمَقَامٖ كَرِيمٖ

Da kuma shuke-shuke da wurin zama mai daraja



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 27

وَنَعۡمَةٖ كَانُواْ فِيهَا فَٰكِهِينَ

Da kuma kayan jin daxi da suka kasance masu ni’imtuwa da su



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 28

كَذَٰلِكَۖ وَأَوۡرَثۡنَٰهَا قَوۡمًا ءَاخَرِينَ

Kamar haka ne; sai Muka kuma gadar da su ga wasu mutane daban (su ne Banu Isra’ila)



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 29

فَمَا بَكَتۡ عَلَيۡهِمُ ٱلسَّمَآءُ وَٱلۡأَرۡضُ وَمَا كَانُواْ مُنظَرِينَ

Sannan (halittun) sama da na qasa ba su yi alhininsu ba, ba su kuma kasance ababen saurara wa ba



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 30

وَلَقَدۡ نَجَّيۡنَا بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ مِنَ ٱلۡعَذَابِ ٱلۡمُهِينِ

Haqiqa kuma Mun tserar da Banu Isra’ila daga azabar wulaqanci