Surah: Suratus Saffat

Ayah : 1

وَٱلصَّـٰٓفَّـٰتِ صَفّٗا

Ina rantsuwa da mala’iku masu yin sahu-sahu



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 2

فَٱلزَّـٰجِرَٰتِ زَجۡرٗا

Sannan da masu yi wa girgije tsawa



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 3

فَٱلتَّـٰلِيَٰتِ ذِكۡرًا

Da masu karanta maganar Allah



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 4

إِنَّ إِلَٰهَكُمۡ لَوَٰحِدٞ

Lalle Ubangiijnku tabbas Xaya ne



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 5

رَّبُّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَيۡنَهُمَا وَرَبُّ ٱلۡمَشَٰرِقِ

Ubangijin sammai da qasa da abin da yake tsakaninsu, kuma Ubangijin wuraren hudowar rana



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 6

إِنَّا زَيَّنَّا ٱلسَّمَآءَ ٱلدُّنۡيَا بِزِينَةٍ ٱلۡكَوَاكِبِ

Lalle Mun qawata sama ta kusa da ado na taurari



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 7

وَحِفۡظٗا مِّن كُلِّ شَيۡطَٰنٖ مَّارِدٖ

Da kuma tsaro daga dukkan wani shaixan mai tsaurin kai



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 8

لَّا يَسَّمَّعُونَ إِلَى ٱلۡمَلَإِ ٱلۡأَعۡلَىٰ وَيُقۡذَفُونَ مِن كُلِّ جَانِبٖ

Ba kuma za su iya jiyowa ba (daga asirin) mala’iku na sama, sai a yi ta jifan su ta kowane vangare



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 9

دُحُورٗاۖ وَلَهُمۡ عَذَابٞ وَاصِبٌ

Don kora; suna kuma da wata azaba dawwamamma



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 10

إِلَّا مَنۡ خَطِفَ ٱلۡخَطۡفَةَ فَأَتۡبَعَهُۥ شِهَابٞ ثَاقِبٞ

Sai dai wanda ya yi fautowar jin, to sai wani tauraro mai haske da quna ya biyo shi



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 11

فَٱسۡتَفۡتِهِمۡ أَهُمۡ أَشَدُّ خَلۡقًا أَم مَّنۡ خَلَقۡنَآۚ إِنَّا خَلَقۡنَٰهُم مِّن طِينٖ لَّازِبِۭ

Ka tambaye su cewa, yanzu su suka fi qarfin halitta ko kuwa waxanda a da Muka halitta? Lalle Mu Mun halicce su daga wani tavo mai danqo



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 12

بَلۡ عَجِبۡتَ وَيَسۡخَرُونَ

A’a, kai dai ka yi mamakin (ikon Allah da qaryatawarsu) ne, su kuma suna yin izgili



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 13

وَإِذَا ذُكِّرُواْ لَا يَذۡكُرُونَ

Idan kuma aka yi musu wa’azi ba sa wa’azantuwa



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 14

وَإِذَا رَأَوۡاْ ءَايَةٗ يَسۡتَسۡخِرُونَ

Idan kuma suka ga wata aya sai su tsananta ba’a



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 15

وَقَالُوٓاْ إِنۡ هَٰذَآ إِلَّا سِحۡرٞ مُّبِينٌ

Su kuma ce: “Wannan ba wani abu ba ne in ban da sihiri mabayyani



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 16

أَءِذَا مِتۡنَا وَكُنَّا تُرَابٗا وَعِظَٰمًا أَءِنَّا لَمَبۡعُوثُونَ

“Yanzu idan muka mutu muka zama qasa da qasusuwa shin da gaske za a tashe mu?



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 17

أَوَءَابَآؤُنَا ٱلۡأَوَّلُونَ

“Haka ma da iyayenmu na farko?”



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 18

قُلۡ نَعَمۡ وَأَنتُمۡ دَٰخِرُونَ

Ka ce: “Na’am, (za a tashe ku) kuna kuwa qasqantattu.”



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 19

فَإِنَّمَا هِيَ زَجۡرَةٞ وَٰحِدَةٞ فَإِذَا هُمۡ يَنظُرُونَ

To (wannan) ba wani abu ba ne sai kawai tsawa guda xaya, sai ga su suna sauraron (abin da zai faru)



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 20

وَقَالُواْ يَٰوَيۡلَنَا هَٰذَا يَوۡمُ ٱلدِّينِ

Sai su ce: “Kaitonmu!” (Sai a ce da su): “Wannan ita ce ranar sakamako



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 21

هَٰذَا يَوۡمُ ٱلۡفَصۡلِ ٱلَّذِي كُنتُم بِهِۦ تُكَذِّبُونَ

“Wannan ita ce ranar hukunci wadda kuka kasance kuna qaryatawa.”



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 22

۞ٱحۡشُرُواْ ٱلَّذِينَ ظَلَمُواْ وَأَزۡوَٰجَهُمۡ وَمَا كَانُواْ يَعۡبُدُونَ

(Za a ce da mala’iku): “Ku tattaro waxanda suka yi zalunci su da abokan haxinsu (shaixanu) da kuma abin da suka kasance suna bauta wa



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 23

مِن دُونِ ٱللَّهِ فَٱهۡدُوهُمۡ إِلَىٰ صِرَٰطِ ٱلۡجَحِيمِ

Waxanda ba Allah ba, sai ku nuna musu hanyar zuwa wutar Jahima



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 24

وَقِفُوهُمۡۖ إِنَّهُم مَّسۡـُٔولُونَ

“Kuma ku tsayar da su; don lalle za a tambaye su



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 25

مَا لَكُمۡ لَا تَنَاصَرُونَ

“Cewa: ‘Me ya sa ba kwa taimakon juna ne?’”



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 26

بَلۡ هُمُ ٱلۡيَوۡمَ مُسۡتَسۡلِمُونَ

Ba haka ba ne, su dai a yau masu miqa wuya ne



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 27

وَأَقۡبَلَ بَعۡضُهُمۡ عَلَىٰ بَعۡضٖ يَتَسَآءَلُونَ

Shashinsu kuma ya fuskanci shashi suna tambayar juna



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 28

قَالُوٓاْ إِنَّكُمۡ كُنتُمۡ تَأۡتُونَنَا عَنِ ٱلۡيَمِينِ

Suka ce: “Lalle kun kasance kuna zo mana ta damanmu[1] (don mu amince muku).”


1- Watau ta hanyar yaudara da daxin baki.


Surah: Suratus Saffat

Ayah : 29

قَالُواْ بَل لَّمۡ تَكُونُواْ مُؤۡمِنِينَ

Suka ce: “A’a, ba ku dai kasance muminai ba ne



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 30

وَمَا كَانَ لَنَا عَلَيۡكُم مِّن سُلۡطَٰنِۭۖ بَلۡ كُنتُمۡ قَوۡمٗا طَٰغِينَ

“Kuma mu ba mu da wani iko a kanku; ku dai kawai kun kasance mutane ne masu xagawa