Surah: Suratur Rum

Ayah : 1

الٓمٓ

ALIF LAM MIM[1]


1- Duba Suratul Baqara, aya ta 1, hashiya ta 8.


Surah: Suratur Rum

Ayah : 2

غُلِبَتِ ٱلرُّومُ

An yi galaba a kan Rumawa[1]


1- Watau Farisawa masu bautar wuta sun yi galaba a kan Rumawa masu bin addinin Annabi Isa () a wani yaqi da ya varke tsakaninsu.


Surah: Suratur Rum

Ayah : 3

فِيٓ أَدۡنَى ٱلۡأَرۡضِ وَهُم مِّنۢ بَعۡدِ غَلَبِهِمۡ سَيَغۡلِبُونَ

A qasa mafi kusa (da su), su kuma da sannu za su yi galaba (a kan Farisa) bayan galabar da aka yi a kansu



Surah: Suratur Rum

Ayah : 4

فِي بِضۡعِ سِنِينَۗ لِلَّهِ ٱلۡأَمۡرُ مِن قَبۡلُ وَمِنۢ بَعۡدُۚ وَيَوۡمَئِذٖ يَفۡرَحُ ٱلۡمُؤۡمِنُونَ

A cikin ‘yan tsirarun shekarun (da ba su kai goma ba). Al’amari a da can da nan gaba na Allah ne. A wannan ranar ne muminai za su yi farin ciki



Surah: Suratur Rum

Ayah : 5

بِنَصۡرِ ٱللَّهِۚ يَنصُرُ مَن يَشَآءُۖ وَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

Da samun nasar Allah (a kan Farisa). Shi Yake taimakon wanda Ya ga dama; domin kuwa Shi ne Mabuwayi, Mai rahama



Surah: Suratur Rum

Ayah : 6

وَعۡدَ ٱللَّهِۖ لَا يُخۡلِفُ ٱللَّهُ وَعۡدَهُۥ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَ ٱلنَّاسِ لَا يَعۡلَمُونَ

(Wannan ya kasance) alqawarin Allah ne; Allah ba Ya sava alqawarinsa, sai dai kuma yawancin mutane ba su san (haka) ba



Surah: Suratur Rum

Ayah : 7

يَعۡلَمُونَ ظَٰهِرٗا مِّنَ ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَا وَهُمۡ عَنِ ٱلۡأٓخِرَةِ هُمۡ غَٰفِلُونَ

Suna sanin abin da yake a sarari na rayuwar duniya ne, alhali kuwa su gafalallu ne game da lahira



Surah: Suratur Rum

Ayah : 8

أَوَلَمۡ يَتَفَكَّرُواْ فِيٓ أَنفُسِهِمۗ مَّا خَلَقَ ٱللَّهُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ وَمَا بَيۡنَهُمَآ إِلَّا بِٱلۡحَقِّ وَأَجَلٖ مُّسَمّٗىۗ وَإِنَّ كَثِيرٗا مِّنَ ٱلنَّاسِ بِلِقَآيِٕ رَبِّهِمۡ لَكَٰفِرُونَ

Yanzu ba su yi tunani a kan kansu ba? Allah bai halicci sammai da qasa da abin da yake tsakaninsu ba sai da gaskiya kuma (ya yi su zuwa) lokaci qayyadajje. Lalle mafi yawan mutane masu kafircewa ne da haxuwa da Ubangijinsu



Surah: Suratur Rum

Ayah : 9

أَوَلَمۡ يَسِيرُواْ فِي ٱلۡأَرۡضِ فَيَنظُرُواْ كَيۡفَ كَانَ عَٰقِبَةُ ٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِهِمۡۚ كَانُوٓاْ أَشَدَّ مِنۡهُمۡ قُوَّةٗ وَأَثَارُواْ ٱلۡأَرۡضَ وَعَمَرُوهَآ أَكۡثَرَ مِمَّا عَمَرُوهَا وَجَآءَتۡهُمۡ رُسُلُهُم بِٱلۡبَيِّنَٰتِۖ فَمَا كَانَ ٱللَّهُ لِيَظۡلِمَهُمۡ وَلَٰكِن كَانُوٓاْ أَنفُسَهُمۡ يَظۡلِمُونَ

Shin ba za su yi tafiya a bayan qasa ba su ga yadda qarshen waxanda suka gabace su ya zama? Sun kasance sun fi su tsananin qarfi, sun kuma tona qasa suka kuma raya ta fiye da yadda su (mutanen Makka) suka raya ta, kuma manzanninsu sun zo musu da (ayoyi) bayyanannu; to Allah bai kasance Mai zaluntar su ba, sai dai su ne suka kasance suna zaluntar kawunansu



Surah: Suratur Rum

Ayah : 10

ثُمَّ كَانَ عَٰقِبَةَ ٱلَّذِينَ أَسَـٰٓـُٔواْ ٱلسُّوٓأَىٰٓ أَن كَذَّبُواْ بِـَٔايَٰتِ ٱللَّهِ وَكَانُواْ بِهَا يَسۡتَهۡزِءُونَ

Sannan kuma qarshen waxanda suka munana (ayyukansu) ya kasance mummunan (sakamako), don sun qaryata ayoyin Allah, kuma sun kasance suna yin izgili gare su



Surah: Suratur Rum

Ayah : 11

ٱللَّهُ يَبۡدَؤُاْ ٱلۡخَلۡقَ ثُمَّ يُعِيدُهُۥ ثُمَّ إِلَيۡهِ تُرۡجَعُونَ

Allah ne Yake farar halitta sannan Ya dawo da ita (bayan mutuwa), sannan kuma gare Shi za a komar da ku



Surah: Suratur Rum

Ayah : 12

وَيَوۡمَ تَقُومُ ٱلسَّاعَةُ يُبۡلِسُ ٱلۡمُجۡرِمُونَ

Kuma ranar da alqiyama za ta tashi, a wannan ranar ne masu manyan laifuka (kafirai) za su yanke qauna daga rahama



Surah: Suratur Rum

Ayah : 13

وَلَمۡ يَكُن لَّهُم مِّن شُرَكَآئِهِمۡ شُفَعَـٰٓؤُاْ وَكَانُواْ بِشُرَكَآئِهِمۡ كَٰفِرِينَ

Daga abokan tarayyar tasu kuwa ba su da wasu masu ceton su, za su ma kasance masu kafirce wa abokan tarayyar tasu



Surah: Suratur Rum

Ayah : 14

وَيَوۡمَ تَقُومُ ٱلسَّاعَةُ يَوۡمَئِذٖ يَتَفَرَّقُونَ

Kuma ranar da alqiyama za ta tashi, a wannan ranar ne (mutane) za su rarrabu[1]


1- Watau qungiya biyu, qungiyar muminai masu shiga Aljanna da ta kafirai masu shiga wuta.


Surah: Suratur Rum

Ayah : 15

فَأَمَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ فَهُمۡ فِي رَوۡضَةٖ يُحۡبَرُونَ

To amma waxanda suka yi imani suka kuma yi aiki nagari, to su kam suna cikin dausayin (Aljanna) ana faranta musu rai



Surah: Suratur Rum

Ayah : 16

وَأَمَّا ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ وَكَذَّبُواْ بِـَٔايَٰتِنَا وَلِقَآيِٕ ٱلۡأٓخِرَةِ فَأُوْلَـٰٓئِكَ فِي ٱلۡعَذَابِ مُحۡضَرُونَ

Amma kuma waxanda suka kafirta suka kuma qaryata ayoyinmu da haxuwa da ranar lahira, to waxannan za a halartar da su cikin azaba



Surah: Suratur Rum

Ayah : 17

فَسُبۡحَٰنَ ٱللَّهِ حِينَ تُمۡسُونَ وَحِينَ تُصۡبِحُونَ

To tsarki ya tabbata ga Allah yayin kuka shiga lokacin maraice, da kuma yayin da kuka wayi gari



Surah: Suratur Rum

Ayah : 18

وَلَهُ ٱلۡحَمۡدُ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَعَشِيّٗا وَحِينَ تُظۡهِرُونَ

Yabo kuma nasa ne a cikin sammai da qasa, da kuma yayin da kuka yi yammaci da kuma shigowarku lokacin azahar



Surah: Suratur Rum

Ayah : 19

يُخۡرِجُ ٱلۡحَيَّ مِنَ ٱلۡمَيِّتِ وَيُخۡرِجُ ٱلۡمَيِّتَ مِنَ ٱلۡحَيِّ وَيُحۡيِ ٱلۡأَرۡضَ بَعۡدَ مَوۡتِهَاۚ وَكَذَٰلِكَ تُخۡرَجُونَ

Yana fitar da rayayye daga matacce, Yana kuma fitar da matacce daga rayayye, kuma Yana raya qasa bayan mutuwarta. Kamar haka ne kuma za a fito da ku (daga qaburburanku)



Surah: Suratur Rum

Ayah : 20

وَمِنۡ ءَايَٰتِهِۦٓ أَنۡ خَلَقَكُم مِّن تُرَابٖ ثُمَّ إِذَآ أَنتُم بَشَرٞ تَنتَشِرُونَ

Yana daga ayoyinsa cewa Ya halicce ku daga turvaya, sannan kuma sai ga ku mutane kun warwatsu (a ko’ina)



Surah: Suratur Rum

Ayah : 21

وَمِنۡ ءَايَٰتِهِۦٓ أَنۡ خَلَقَ لَكُم مِّنۡ أَنفُسِكُمۡ أَزۡوَٰجٗا لِّتَسۡكُنُوٓاْ إِلَيۡهَا وَجَعَلَ بَيۡنَكُم مَّوَدَّةٗ وَرَحۡمَةًۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَٰتٖ لِّقَوۡمٖ يَتَفَكَّرُونَ

Yana kuma daga ayoyinsa cewa Ya halitta muku mata daga jinsinku don ku samu nutsuwa gare su, Ya kuma sanya soyayya da jin qai tsakaninku. Lalle a game da wannan tabbas akwai ayoyi ga mutane masu tunani



Surah: Suratur Rum

Ayah : 22

وَمِنۡ ءَايَٰتِهِۦ خَلۡقُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَٱخۡتِلَٰفُ أَلۡسِنَتِكُمۡ وَأَلۡوَٰنِكُمۡۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَٰتٖ لِّلۡعَٰلِمِينَ

Yana kuma daga cikin ayoyinsa halittar sammai da qasa da kuma sassavawar harsunanku da launukanku. Lalle a game da wannan tabbas akwai ayoyi ga ma’abota ilimi



Surah: Suratur Rum

Ayah : 23

وَمِنۡ ءَايَٰتِهِۦ مَنَامُكُم بِٱلَّيۡلِ وَٱلنَّهَارِ وَٱبۡتِغَآؤُكُم مِّن فَضۡلِهِۦٓۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَٰتٖ لِّقَوۡمٖ يَسۡمَعُونَ

Yana kuma daga cikin ayoyinsa barcinku da daddare da kuma rana da neman falalarsa da kuke yi. Lalle a game da wannan tabbas akwai ayoyi ga masu ji (na lura)



Surah: Suratur Rum

Ayah : 24

وَمِنۡ ءَايَٰتِهِۦ يُرِيكُمُ ٱلۡبَرۡقَ خَوۡفٗا وَطَمَعٗا وَيُنَزِّلُ مِنَ ٱلسَّمَآءِ مَآءٗ فَيُحۡيِۦ بِهِ ٱلۡأَرۡضَ بَعۡدَ مَوۡتِهَآۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَٰتٖ لِّقَوۡمٖ يَعۡقِلُونَ

Yana kuma daga cikin ayoyinsa nuna muku walqiya da Yake yi don tsoratarwa da kwaxaitarwa, Ya kuma saukar da ruwa daga sama, sai Ya raya qasa da shi bayan mutuwarta. Lalle a game da wannan tabbas akwai ayoyi ga mutane da suke hankalta



Surah: Suratur Rum

Ayah : 25

وَمِنۡ ءَايَٰتِهِۦٓ أَن تَقُومَ ٱلسَّمَآءُ وَٱلۡأَرۡضُ بِأَمۡرِهِۦۚ ثُمَّ إِذَا دَعَاكُمۡ دَعۡوَةٗ مِّنَ ٱلۡأَرۡضِ إِذَآ أَنتُمۡ تَخۡرُجُونَ

Yana kuma daga cikin ayoyinsa sama da qasa su tsaya da umarninsa. Sannan kuma yayin da Ya kira ku (don ku tashi) daga qasa sai ga ku kuna fitowa



Surah: Suratur Rum

Ayah : 26

وَلَهُۥ مَن فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۖ كُلّٞ لَّهُۥ قَٰنِتُونَ

Kuma duk waxanda suke cikin sammai da qasa nasa ne; dukkaninsu masu biyayya ne gare Shi



Surah: Suratur Rum

Ayah : 27

وَهُوَ ٱلَّذِي يَبۡدَؤُاْ ٱلۡخَلۡقَ ثُمَّ يُعِيدُهُۥ وَهُوَ أَهۡوَنُ عَلَيۡهِۚ وَلَهُ ٱلۡمَثَلُ ٱلۡأَعۡلَىٰ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ وَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡحَكِيمُ

Shi ne wanda Yake farar halittu, sannan Ya dawo da su (bayan mutuwa. Yin haka) kuwa shi ya fi sauqi a gare Shi. Kuma siffofi mafiya xaukaka sun tabbata gare Shi a cikin sammai da qasa, kuma Shi ne Mabuwayi, Mai hikima



Surah: Suratur Rum

Ayah : 28

ضَرَبَ لَكُم مَّثَلٗا مِّنۡ أَنفُسِكُمۡۖ هَل لَّكُم مِّن مَّا مَلَكَتۡ أَيۡمَٰنُكُم مِّن شُرَكَآءَ فِي مَا رَزَقۡنَٰكُمۡ فَأَنتُمۡ فِيهِ سَوَآءٞ تَخَافُونَهُمۡ كَخِيفَتِكُمۡ أَنفُسَكُمۡۚ كَذَٰلِكَ نُفَصِّلُ ٱلۡأٓيَٰتِ لِقَوۡمٖ يَعۡقِلُونَ

Ya ba ku misali daga kawunanku; shin kuna da wasu abokan tarayya daga bayinku da kuka mallaka a kan abin da Muka arzuta ku (da shi), ku da su ku zama daidai kuke game da wannan; kuna ma jin tsoron su kamar yanda kuke tsoron junanku? Kamar haka Muke rarrabe ayoyin (filla-filla) ga mutanen da suke hankalta



Surah: Suratur Rum

Ayah : 29

بَلِ ٱتَّبَعَ ٱلَّذِينَ ظَلَمُوٓاْ أَهۡوَآءَهُم بِغَيۡرِ عِلۡمٖۖ فَمَن يَهۡدِي مَنۡ أَضَلَّ ٱللَّهُۖ وَمَا لَهُم مِّن نَّـٰصِرِينَ

Ba haka ba ne, waxanda suka yi zalunci dai sun bi son ransu ne ba tare da wani ilimi ba; to wane ne zai shiryar da wanda Allah Ya vatar? Kuma ba su da wasu mataimaka



Surah: Suratur Rum

Ayah : 30

فَأَقِمۡ وَجۡهَكَ لِلدِّينِ حَنِيفٗاۚ فِطۡرَتَ ٱللَّهِ ٱلَّتِي فَطَرَ ٱلنَّاسَ عَلَيۡهَاۚ لَا تَبۡدِيلَ لِخَلۡقِ ٱللَّهِۚ ذَٰلِكَ ٱلدِّينُ ٱلۡقَيِّمُ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَ ٱلنَّاسِ لَا يَعۡلَمُونَ

To sai ka tsayar da fuskarka ga addini mai kauce wa varna. (Shi ne) asalin halittar da Allah Ya halicci mutane a kanta[1]. Ba wani canji ga halittar Allah. Wannan shi ne miqaqqen addini, sai dai kuma yawancin mutane ba su san (haka ba)


1- Watau kaxaita Allah da bauta. Addinin Musulunci shi ne addinin da ya dace da halittar xan’adam ta asali, watau fixra.