Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 1

قَدۡ أَفۡلَحَ ٱلۡمُؤۡمِنُونَ

Haqiqa muminai sun rabauta



Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 2

ٱلَّذِينَ هُمۡ فِي صَلَاتِهِمۡ خَٰشِعُونَ

(Su ne) waxanda suke masu qasqantar da kai a cikin sallarsu



Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 3

وَٱلَّذِينَ هُمۡ عَنِ ٱللَّغۡوِ مُعۡرِضُونَ

Kuma waxanda suke masu kau da kai daga yasasshiyar magana



Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 4

وَٱلَّذِينَ هُمۡ لِلزَّكَوٰةِ فَٰعِلُونَ

Kuma waxanda suke masu aiwatar da zakka



Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 5

وَٱلَّذِينَ هُمۡ لِفُرُوجِهِمۡ حَٰفِظُونَ

Kuma waxanda suke masu kiyaye farjinsu



Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 6

إِلَّا عَلَىٰٓ أَزۡوَٰجِهِمۡ أَوۡ مَا مَلَكَتۡ أَيۡمَٰنُهُمۡ فَإِنَّهُمۡ غَيۡرُ مَلُومِينَ

Sai dai ga matayensu ko kuma qwara-qwaransu, to lalle su ba abin zargi ba ne



Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 7

فَمَنِ ٱبۡتَغَىٰ وَرَآءَ ذَٰلِكَ فَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡعَادُونَ

Sannan duk wanda ya nemi (wata hanya) ba waxannan ba, to waxannan su ne masu qetare iyaka



Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 8

وَٱلَّذِينَ هُمۡ لِأَمَٰنَٰتِهِمۡ وَعَهۡدِهِمۡ رَٰعُونَ

Kuma waxanda suke masu kiyaye amanarsu da kuma alqawarinsu



Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 9

وَٱلَّذِينَ هُمۡ عَلَىٰ صَلَوَٰتِهِمۡ يُحَافِظُونَ

Kuma waxanda suke kiyaye sallolinsu



Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 10

أُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡوَٰرِثُونَ

Waxannan su ne magada



Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 11

ٱلَّذِينَ يَرِثُونَ ٱلۡفِرۡدَوۡسَ هُمۡ فِيهَا خَٰلِدُونَ

Waxanda suke gadar (Aljannar) Firdausi, su madawwama ne a cikinta



Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 12

وَلَقَدۡ خَلَقۡنَا ٱلۡإِنسَٰنَ مِن سُلَٰلَةٖ مِّن طِينٖ

Kuma haqiqa Mun halicci mutum daga tataccen tavo



Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 13

ثُمَّ جَعَلۡنَٰهُ نُطۡفَةٗ فِي قَرَارٖ مَّكِينٖ

Sannan Muka mai da shi maniyyi cikin wuri amintacce



Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 14

ثُمَّ خَلَقۡنَا ٱلنُّطۡفَةَ عَلَقَةٗ فَخَلَقۡنَا ٱلۡعَلَقَةَ مُضۡغَةٗ فَخَلَقۡنَا ٱلۡمُضۡغَةَ عِظَٰمٗا فَكَسَوۡنَا ٱلۡعِظَٰمَ لَحۡمٗا ثُمَّ أَنشَأۡنَٰهُ خَلۡقًا ءَاخَرَۚ فَتَبَارَكَ ٱللَّهُ أَحۡسَنُ ٱلۡخَٰلِقِينَ

Sannan Muka mayar da maniyyin ya zama gudan jini, sai gudan jinin ya zama tsoka, sai Muka mai da tsokar qasusuwa, sannan Muka lulluve qasusuwan da nama, sannan kuma Muka mai da shi wata halitta daban. To albarkatun Allah sun yawaita, Wanda Shi ne Mafi gwanintar masu halitta



Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 15

ثُمَّ إِنَّكُم بَعۡدَ ذَٰلِكَ لَمَيِّتُونَ

Sannan kuma lalle tabbas bayan haka za ku mutu



Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 16

ثُمَّ إِنَّكُمۡ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ تُبۡعَثُونَ

Sannan kuma haqiqa za a tashe ku ranar Alqiyama



Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 17

وَلَقَدۡ خَلَقۡنَا فَوۡقَكُمۡ سَبۡعَ طَرَآئِقَ وَمَا كُنَّا عَنِ ٱلۡخَلۡقِ غَٰفِلِينَ

Kuma haqiqa Mun halicci hanyoyi bakwai a sama da ku, ba Mu kuma zama gafalallu ba game da halittar



Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 18

وَأَنزَلۡنَا مِنَ ٱلسَّمَآءِ مَآءَۢ بِقَدَرٖ فَأَسۡكَنَّـٰهُ فِي ٱلۡأَرۡضِۖ وَإِنَّا عَلَىٰ ذَهَابِۭ بِهِۦ لَقَٰدِرُونَ

Muka kuma saukar da ruwa daga sama daidai gwargwado, sai Muka zaunar da shi a cikin qasa, kuma lalle Mu Masu iko ne a kan kawar da shi



Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 19

فَأَنشَأۡنَا لَكُم بِهِۦ جَنَّـٰتٖ مِّن نَّخِيلٖ وَأَعۡنَٰبٖ لَّكُمۡ فِيهَا فَوَٰكِهُ كَثِيرَةٞ وَمِنۡهَا تَأۡكُلُونَ

Sai Muka samar muku gonaki na dabinai da inabai da shi (ruwan), kuna kuma da kayan marmari masu yawa a cikinsu (gonakin), kuma daga gare su kuke ci



Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 20

وَشَجَرَةٗ تَخۡرُجُ مِن طُورِ سَيۡنَآءَ تَنۢبُتُ بِٱلدُّهۡنِ وَصِبۡغٖ لِّلۡأٓكِلِينَ

Kuma (Mun halitta muku) wata bishiya da take fitowa a (dutsen) Xuri Sina’a, tana fito da man (zaitun) kuma mahaxin abinci ne



Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 21

وَإِنَّ لَكُمۡ فِي ٱلۡأَنۡعَٰمِ لَعِبۡرَةٗۖ نُّسۡقِيكُم مِّمَّا فِي بُطُونِهَا وَلَكُمۡ فِيهَا مَنَٰفِعُ كَثِيرَةٞ وَمِنۡهَا تَأۡكُلُونَ

Kuma lalle akwai izina a gare ku game da dabbobin ni’ima[1]; Muna shayar da ku daga abin da yake cikinsu[2], kuma kuna da amfani mai yawa daga gare su, daga gare su kuma kuke ci


1- Su ne raquma da shanu da tumaki da awaki.


2- Shi ne tataccen nono.


Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 22

وَعَلَيۡهَا وَعَلَى ٱلۡفُلۡكِ تُحۡمَلُونَ

A kansu da kuma a kan jirgin ruwa ake xaukar ku



Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 23

وَلَقَدۡ أَرۡسَلۡنَا نُوحًا إِلَىٰ قَوۡمِهِۦ فَقَالَ يَٰقَوۡمِ ٱعۡبُدُواْ ٱللَّهَ مَا لَكُم مِّنۡ إِلَٰهٍ غَيۡرُهُۥٓۚ أَفَلَا تَتَّقُونَ

Haqiqa kuma Mun aiko Nuhu zuwa ga mutanensa, sai ya ce: “Ya ku mutanena, ku bauta wa Allah, ba ku da wani abin bauta in ba Shi ba; me ya sa ne ba za ku yi taqawa ba.”



Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 24

فَقَالَ ٱلۡمَلَؤُاْ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ مِن قَوۡمِهِۦ مَا هَٰذَآ إِلَّا بَشَرٞ مِّثۡلُكُمۡ يُرِيدُ أَن يَتَفَضَّلَ عَلَيۡكُمۡ وَلَوۡ شَآءَ ٱللَّهُ لَأَنزَلَ مَلَـٰٓئِكَةٗ مَّا سَمِعۡنَا بِهَٰذَا فِيٓ ءَابَآئِنَا ٱلۡأَوَّلِينَ

Sai manya-manyan da suka kafirce daga mutanen nasa suka ce: “Ai wannan ba kowa ba ne face mutum irinku, yana so ne ya samu fifiko a kanku, kuma da Allah Ya ga dama da sai Ya saukar da mala’iku, mu ba mu tava jin irin wannan ba daga iyayenmu na farko



Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 25

إِنۡ هُوَ إِلَّا رَجُلُۢ بِهِۦ جِنَّةٞ فَتَرَبَّصُواْ بِهِۦ حَتَّىٰ حِينٖ

“Ba kowa ba ne shi in ban da mutum da yake da (tavin) aljan, sai ku saurara masa har zuwa wani xan lokaci.”



Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 26

قَالَ رَبِّ ٱنصُرۡنِي بِمَا كَذَّبُونِ

Ya ce: “Ubangijina Ka taimake ni game da abin da suka qaryata ni a kansa.”



Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 27

فَأَوۡحَيۡنَآ إِلَيۡهِ أَنِ ٱصۡنَعِ ٱلۡفُلۡكَ بِأَعۡيُنِنَا وَوَحۡيِنَا فَإِذَا جَآءَ أَمۡرُنَا وَفَارَ ٱلتَّنُّورُ فَٱسۡلُكۡ فِيهَا مِن كُلّٖ زَوۡجَيۡنِ ٱثۡنَيۡنِ وَأَهۡلَكَ إِلَّا مَن سَبَقَ عَلَيۡهِ ٱلۡقَوۡلُ مِنۡهُمۡۖ وَلَا تُخَٰطِبۡنِي فِي ٱلَّذِينَ ظَلَمُوٓاْ إِنَّهُم مُّغۡرَقُونَ

Sai Muka yiwo masa wahayi cewa: “Ka sassaqa jirgin ruwa a qarqashin kulawarmu da umarninmu, sannan idan umarninmu (na hallaka su) ya zo, kuma tanderu ya vuvvugo da ruwa, sai ka saka ma’aurata guda biyu daga kowane jinsi a cikinsa, da kuma iyalanka, sai wanda kalmar (halaka) ta rigaya a kansa daga cikinsu; kuma kada ka ce min komai game da waxanda suka kafirta; lalle su waxanda za a nutsar ne



Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 28

فَإِذَا ٱسۡتَوَيۡتَ أَنتَ وَمَن مَّعَكَ عَلَى ٱلۡفُلۡكِ فَقُلِ ٱلۡحَمۡدُ لِلَّهِ ٱلَّذِي نَجَّىٰنَا مِنَ ٱلۡقَوۡمِ ٱلظَّـٰلِمِينَ

“To idan kai da waxanda suke tare da kai kuka daidaita a kan jirgin, sai ka ce: “Na gode wa Allah wanda Ya tserar da mu daga mutane azzalumai.”



Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 29

وَقُل رَّبِّ أَنزِلۡنِي مُنزَلٗا مُّبَارَكٗا وَأَنتَ خَيۡرُ ٱلۡمُنزِلِينَ

Kuma ka ce: “Ubangijina Ka saukar da ni masauki mai albarka, Kai ne kuwa Fiyayyen masu saukarwa.”



Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 30

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَٰتٖ وَإِن كُنَّا لَمُبۡتَلِينَ

Lalle a game da wannan tabbas akwai ayoyi, Mu kuma haqiqa Mun kasance Masu jarrabawa ne