Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 1

طه

Xa Ha[1]


1- Duba Suratul Baqara, aya ta 1, hashiya ta 8.


Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 2

مَآ أَنزَلۡنَا عَلَيۡكَ ٱلۡقُرۡءَانَ لِتَشۡقَىٰٓ

Ba Mu saukar maka da Alqur’ani don ka wahala ba



Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 3

إِلَّا تَذۡكِرَةٗ لِّمَن يَخۡشَىٰ

Sai don wa’azi ga wanda zai ji tsoron (haxuwa da Allah)



Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 4

تَنزِيلٗا مِّمَّنۡ خَلَقَ ٱلۡأَرۡضَ وَٱلسَّمَٰوَٰتِ ٱلۡعُلَى

Saukakke ne daga wanda Ya halicci qasa da sammai masu xaukaka



Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 5

ٱلرَّحۡمَٰنُ عَلَى ٱلۡعَرۡشِ ٱسۡتَوَىٰ

(Allah) Mai rahama, Ya daidaita a kan Al’arshi[1]


1- Duba Suratul A’arafi, aya ta 54, hashiya ta 126.


Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 6

لَهُۥ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِي ٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَيۡنَهُمَا وَمَا تَحۡتَ ٱلثَّرَىٰ

Abin da yake sammai da qasa, da abin da yake tsakaninsu da kuma abin da yake qarqashin qasa, (duka) nasa ne



Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 7

وَإِن تَجۡهَرۡ بِٱلۡقَوۡلِ فَإِنَّهُۥ يَعۡلَمُ ٱلسِّرَّ وَأَخۡفَى

Idan kuma ka xaga murya da furuci to lalle Shi Yana sane da sirri da abin da ya fi (sirri) vuya



Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 8

ٱللَّهُ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَۖ لَهُ ٱلۡأَسۡمَآءُ ٱلۡحُسۡنَىٰ

Allah (Shi ne wanda) babu wani abin bauta da gaskiya sai Shi; Yana da sunaye mafiya kyau



Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 9

وَهَلۡ أَتَىٰكَ حَدِيثُ مُوسَىٰٓ

Shin kuwa labarin Musa ya zo maka?



Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 10

إِذۡ رَءَا نَارٗا فَقَالَ لِأَهۡلِهِ ٱمۡكُثُوٓاْ إِنِّيٓ ءَانَسۡتُ نَارٗا لَّعَلِّيٓ ءَاتِيكُم مِّنۡهَا بِقَبَسٍ أَوۡ أَجِدُ عَلَى ٱلنَّارِ هُدٗى

Lokacin da ya gano wuta sai ya ce da iyalinsa: “Ku zauna (a nan), lalle ni fa na hangi wuta, (zan je) ko na zo muku da garwashinta ko kuma in sami mai nuna mini (hanya) a wurin wutar.”



Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 11

فَلَمَّآ أَتَىٰهَا نُودِيَ يَٰمُوسَىٰٓ

To lokacin da ya zo wurinta (wato wutar), sai aka kira shi (cewa): “Ya Musa



Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 12

إِنِّيٓ أَنَا۠ رَبُّكَ فَٱخۡلَعۡ نَعۡلَيۡكَ إِنَّكَ بِٱلۡوَادِ ٱلۡمُقَدَّسِ طُوٗى

“Lalle Ni, Ni ne fa Ubangijinka, sai ka tuve takalmanka; lalle kana a tsarkakakken kwarin Xuwa ne



Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 13

وَأَنَا ٱخۡتَرۡتُكَ فَٱسۡتَمِعۡ لِمَا يُوحَىٰٓ

“Kuma Ni Na zave ka (da manzanci), sai ka ji abin da za a yiwo ma wahayi (da shi)



Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 14

إِنَّنِيٓ أَنَا ٱللَّهُ لَآ إِلَٰهَ إِلَّآ أَنَا۠ فَٱعۡبُدۡنِي وَأَقِمِ ٱلصَّلَوٰةَ لِذِكۡرِيٓ

“Lalle Ni, Ni ne Allah, babu wani abin bauta sai Ni, to ka bauta mini, kuma ka tsai da salla don tuna Ni



Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 15

إِنَّ ٱلسَّاعَةَ ءَاتِيَةٌ أَكَادُ أُخۡفِيهَا لِتُجۡزَىٰ كُلُّ نَفۡسِۭ بِمَا تَسۡعَىٰ

“Lalle alqiyama za ta zo, ina nufin voye ta ne don a saka wa kowanne rai da irin abin da yake aikatawa



Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 16

فَلَا يَصُدَّنَّكَ عَنۡهَا مَن لَّا يُؤۡمِنُ بِهَا وَٱتَّبَعَ هَوَىٰهُ فَتَرۡدَىٰ

“To kada wanda bai yi imani da ita ba ya kuma bi son ransa ya hana ka gaskata ta, sai ka hallaka



Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 17

وَمَا تِلۡكَ بِيَمِينِكَ يَٰمُوسَىٰ

“Mene ne kuma wancan yake a hannun damanka ya Musa?”



Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 18

قَالَ هِيَ عَصَايَ أَتَوَكَّؤُاْ عَلَيۡهَا وَأَهُشُّ بِهَا عَلَىٰ غَنَمِي وَلِيَ فِيهَا مَـَٔارِبُ أُخۡرَىٰ

(Musa) ya ce: “Ai sandata ce da nake jingina a kanta, ina kuma kaxo wa dabbobina ganye da ita, ina kuma da sauran wasu buqatu game da ita.”



Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 19

قَالَ أَلۡقِهَا يَٰمُوسَىٰ

(Allah) Ya ce: “Jefar da ita ya Musa.”



Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 20

فَأَلۡقَىٰهَا فَإِذَا هِيَ حَيَّةٞ تَسۡعَىٰ

Sai ya jefar da ita, sai ga ta ta zama macijiya tana ta sauri



Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 21

قَالَ خُذۡهَا وَلَا تَخَفۡۖ سَنُعِيدُهَا سِيرَتَهَا ٱلۡأُولَىٰ

Ya ce: “Kama ta, kuma kada ka ji tsoro; za Mu mai da ita kamar yadda take a da



Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 22

وَٱضۡمُمۡ يَدَكَ إِلَىٰ جَنَاحِكَ تَخۡرُجۡ بَيۡضَآءَ مِنۡ غَيۡرِ سُوٓءٍ ءَايَةً أُخۡرَىٰ

“Kuma ka haxa hannunka da kwivinka zai fito fari sal ba tare da wata cuta ba; (wannan) wata ayar ce daban



Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 23

لِنُرِيَكَ مِنۡ ءَايَٰتِنَا ٱلۡكُبۡرَى

“Domin Mu nuna maka irin manya-manyan ayoyinmu



Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 24

ٱذۡهَبۡ إِلَىٰ فِرۡعَوۡنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ

“Ka tafi wurin Fir’auna don kuwa lalle ya qetare iyaka.”



Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 25

قَالَ رَبِّ ٱشۡرَحۡ لِي صَدۡرِي

(Musa) ya ce: “Ubangijina Ka buxe mini qirjina[1]


1- Watau ya cire masa in’ina da take damun sa.


Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 26

وَيَسِّرۡ لِيٓ أَمۡرِي

“Kuma Ka sauqaqa mini lamarina



Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 27

وَٱحۡلُلۡ عُقۡدَةٗ مِّن لِّسَانِي

“Ka kuma warware qullin da yake a harshena



Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 28

يَفۡقَهُواْ قَوۡلِي

“(Don) su fahimci maganata



Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 29

وَٱجۡعَل لِّي وَزِيرٗا مِّنۡ أَهۡلِي

“Kuma Ka sanya mini waziri daga dangina



Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 30

هَٰرُونَ أَخِي

“(Watau) xau’uwana Haruna