Surah: Suratu Yunus

Ayah : 6

إِنَّ فِي ٱخۡتِلَٰفِ ٱلَّيۡلِ وَٱلنَّهَارِ وَمَا خَلَقَ ٱللَّهُ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ لَأٓيَٰتٖ لِّقَوۡمٖ يَتَّقُونَ

Lalle game da sassavawar dare da rana da kuma abubuwan da Allah Ya halitta cikin sammai da qasa akwai ayoyi ga mutanen da suke kiyaye dokokin Allah



Surah: Suratu Yunus

Ayah : 11

۞وَلَوۡ يُعَجِّلُ ٱللَّهُ لِلنَّاسِ ٱلشَّرَّ ٱسۡتِعۡجَالَهُم بِٱلۡخَيۡرِ لَقُضِيَ إِلَيۡهِمۡ أَجَلُهُمۡۖ فَنَذَرُ ٱلَّذِينَ لَا يَرۡجُونَ لِقَآءَنَا فِي طُغۡيَٰنِهِمۡ يَعۡمَهُونَ

Da dai Allah zai gaggauta (karvar addu’ar) mutane ta sharri kamar yadda yake gaggauta ta alheri to da qarshen rayuwarsu ya zo. Sai dai Mukan bar waxanda ba sa tsammanin haxuwa da Mu cikin shisshiginsu su yi ta ximuwa



Surah: Suratu Yunus

Ayah : 31

قُلۡ مَن يَرۡزُقُكُم مِّنَ ٱلسَّمَآءِ وَٱلۡأَرۡضِ أَمَّن يَمۡلِكُ ٱلسَّمۡعَ وَٱلۡأَبۡصَٰرَ وَمَن يُخۡرِجُ ٱلۡحَيَّ مِنَ ٱلۡمَيِّتِ وَيُخۡرِجُ ٱلۡمَيِّتَ مِنَ ٱلۡحَيِّ وَمَن يُدَبِّرُ ٱلۡأَمۡرَۚ فَسَيَقُولُونَ ٱللَّهُۚ فَقُلۡ أَفَلَا تَتَّقُونَ

Ka ce: “Wane ne yake arzuta ku ta sama da qasa? Ko kuma wane ne mamallakin ji da gani? Kuma wane ne yake fitar da mai rai daga matacce, ya kuma fitar da matacce daga mai rai? Wane ne kuma yake tsara al’amura?” To ai za su ce: “Allah ne.” To ka ce: “Yanzu ba za ku kiyaye dokokinsa ba?”



Surah: Suratu Yunus

Ayah : 34

قُلۡ هَلۡ مِن شُرَكَآئِكُم مَّن يَبۡدَؤُاْ ٱلۡخَلۡقَ ثُمَّ يُعِيدُهُۥۚ قُلِ ٱللَّهُ يَبۡدَؤُاْ ٱلۡخَلۡقَ ثُمَّ يُعِيدُهُۥۖ فَأَنَّىٰ تُؤۡفَكُونَ

Ka ce: “Shin daga cikin abokan tarayyarku ko akwai wanda yake qaga halitta, sannan ya maimaita ta?” Ka ce: “Allah Shi ne Wanda Yake qaga halitta sannan Ya maimaita ta. To ta yaya ake kautar da ku?”



Surah: Suratu Yunus

Ayah : 36

وَمَا يَتَّبِعُ أَكۡثَرُهُمۡ إِلَّا ظَنًّاۚ إِنَّ ٱلظَّنَّ لَا يُغۡنِي مِنَ ٱلۡحَقِّ شَيۡـًٔاۚ إِنَّ ٱللَّهَ عَلِيمُۢ بِمَا يَفۡعَلُونَ

Yawancinsu kuma ba abin da suke bi sai zato. Lalle zato ba ya wadatar da komai game da gaskiya. Lalle Allah Masanin abin da suke aikatawa ne



Surah: Suratu Yunus

Ayah : 40

وَمِنۡهُم مَّن يُؤۡمِنُ بِهِۦ وَمِنۡهُم مَّن لَّا يُؤۡمِنُ بِهِۦۚ وَرَبُّكَ أَعۡلَمُ بِٱلۡمُفۡسِدِينَ

Daga cikinsu kuma akwai wanda yake yin imani da shi (Alqur’ani), akwai kuma wanda ba ya yin imani da shi. Ubangijinka kuma Shi ne Mafi sanin mavarnata



Surah: Suratu Yunus

Ayah : 58

قُلۡ بِفَضۡلِ ٱللَّهِ وَبِرَحۡمَتِهِۦ فَبِذَٰلِكَ فَلۡيَفۡرَحُواْ هُوَ خَيۡرٞ مِّمَّا يَجۡمَعُونَ

Ka ce: “Da falalar Allah da rahamarsa, sai su yi farin ciki da wannan; shi ya fi alheri daga abin da suke tarawa (na dukiya).”



Surah: Suratu Yunus

Ayah : 60

وَمَا ظَنُّ ٱلَّذِينَ يَفۡتَرُونَ عَلَى ٱللَّهِ ٱلۡكَذِبَ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِۗ إِنَّ ٱللَّهَ لَذُو فَضۡلٍ عَلَى ٱلنَّاسِ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَهُمۡ لَا يَشۡكُرُونَ

Mene ne kuma tsammanin waxanda suke yi wa Allah qagen qarya a ranar alqiyama? Lalle Allah Ma’abocin falala ne ga mutane, sai dai kuma yawancinsu ba sa godewa



Surah: Suratu Yunus

Ayah : 61

وَمَا تَكُونُ فِي شَأۡنٖ وَمَا تَتۡلُواْ مِنۡهُ مِن قُرۡءَانٖ وَلَا تَعۡمَلُونَ مِنۡ عَمَلٍ إِلَّا كُنَّا عَلَيۡكُمۡ شُهُودًا إِذۡ تُفِيضُونَ فِيهِۚ وَمَا يَعۡزُبُ عَن رَّبِّكَ مِن مِّثۡقَالِ ذَرَّةٖ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَلَا فِي ٱلسَّمَآءِ وَلَآ أَصۡغَرَ مِن ذَٰلِكَ وَلَآ أَكۡبَرَ إِلَّا فِي كِتَٰبٖ مُّبِينٍ

Kuma babu wani al’amari da (kai Annabi) kake zamantowa cikinsa, babu kuma wani abu na Alqur’ani da kake karantawa, kuma babu wani abu da kuke aikatawa (kai da al’ummarka), sai Mun zamanto Muna kallon ku lokacin da kuke kutsawa cikinsa. Kuma babu wani abu da yake voye wa Ubangijinka daidai da qwayar komayya, a qasa ko a sama ko kuma mafi qanqanta ko mafi girma daga wancan (abin) sai fa yana cikin litttafi mabayyani (Lauhul-Mahafuzu)



Surah: Suratu Yunus

Ayah : 62

أَلَآ إِنَّ أَوۡلِيَآءَ ٱللَّهِ لَا خَوۡفٌ عَلَيۡهِمۡ وَلَا هُمۡ يَحۡزَنُونَ

A saurara, lalle waliyyan Allah babu wani tsoro a gare su, kuma ba za su yi wani baqin ciki ba



Surah: Suratu Yunus

Ayah : 63

ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَكَانُواْ يَتَّقُونَ

(Su ne) waxanda suka yi imani kuma suka kasance masu kiyaye dokokin Allah



Surah: Suratu Yunus

Ayah : 71

۞وَٱتۡلُ عَلَيۡهِمۡ نَبَأَ نُوحٍ إِذۡ قَالَ لِقَوۡمِهِۦ يَٰقَوۡمِ إِن كَانَ كَبُرَ عَلَيۡكُم مَّقَامِي وَتَذۡكِيرِي بِـَٔايَٰتِ ٱللَّهِ فَعَلَى ٱللَّهِ تَوَكَّلۡتُ فَأَجۡمِعُوٓاْ أَمۡرَكُمۡ وَشُرَكَآءَكُمۡ ثُمَّ لَا يَكُنۡ أَمۡرُكُمۡ عَلَيۡكُمۡ غُمَّةٗ ثُمَّ ٱقۡضُوٓاْ إِلَيَّ وَلَا تُنظِرُونِ

Ka kuma karanta musu labarin (Annabi) Nuhu, a lokacin da ya ce da mutanensa: “Ya ku mutanena, idan zamana a cikinku da kuma wa’azin da nake muku da ayoyin Allah sun dame ku, to ni fa ga Allah ne kawai na dogara, sai ku tattara al’amarinku ku kuma (ku kira) abokan tarayyarku, sannan kada al’amarin naku ya zama a voye, sannan ku zartar (da shi) a gare ni, kada kuma ku saurara mini



Surah: Suratu Yunus

Ayah : 84

وَقَالَ مُوسَىٰ يَٰقَوۡمِ إِن كُنتُمۡ ءَامَنتُم بِٱللَّهِ فَعَلَيۡهِ تَوَكَّلُوٓاْ إِن كُنتُم مُّسۡلِمِينَ

Musa kuma ya ce: “Ya ku mutanena, idan har kun yi imani da Allah, to a gare Shi kawai za ku dogara in kun kasance Musulmai



Surah: Suratu Yunus

Ayah : 85

فَقَالُواْ عَلَى ٱللَّهِ تَوَكَّلۡنَا رَبَّنَا لَا تَجۡعَلۡنَا فِتۡنَةٗ لِّلۡقَوۡمِ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Sai suka ce: “Ga Allah kaxai muka dogara. Ya Ubangijinmu, kada ka sanya mu zama fitina ga mutane azzalumai



Surah: Suratu Yunus

Ayah : 99

وَلَوۡ شَآءَ رَبُّكَ لَأٓمَنَ مَن فِي ٱلۡأَرۡضِ كُلُّهُمۡ جَمِيعًاۚ أَفَأَنتَ تُكۡرِهُ ٱلنَّاسَ حَتَّىٰ يَكُونُواْ مُؤۡمِنِينَ

Da Ubangijinka Ya ga dama lalle da duk waxanda suke bayan qasa sun yi imani gaba xayansu. Shin kai ne za ka tilasa wa mutane har su zama muminai?



Surah: Suratu Yunus

Ayah : 107

وَإِن يَمۡسَسۡكَ ٱللَّهُ بِضُرّٖ فَلَا كَاشِفَ لَهُۥٓ إِلَّا هُوَۖ وَإِن يُرِدۡكَ بِخَيۡرٖ فَلَا رَآدَّ لِفَضۡلِهِۦۚ يُصِيبُ بِهِۦ مَن يَشَآءُ مِنۡ عِبَادِهِۦۚ وَهُوَ ٱلۡغَفُورُ ٱلرَّحِيمُ

Idan Allah Ya xora maka wata cuta to ba mai yaye maka ita sai shi; idan kuma Ya nufe ka da alheri to ba mai juyar da falalarsa. Yana bayar da shi ga waxanda Ya ga dama daga bayinsa. Shi ne kuma Mai gafara, Mai jin qai



Surah: Suratu Hud

Ayah : 5

أَلَآ إِنَّهُمۡ يَثۡنُونَ صُدُورَهُمۡ لِيَسۡتَخۡفُواْ مِنۡهُۚ أَلَا حِينَ يَسۡتَغۡشُونَ ثِيَابَهُمۡ يَعۡلَمُ مَا يُسِرُّونَ وَمَا يُعۡلِنُونَۚ إِنَّهُۥ عَلِيمُۢ بِذَاتِ ٱلصُّدُورِ

Ku saurara! Lalle su suna karkatar da qirazansu don su voye masa (Allah). Ku saurara! Ai lokacin da suke lulluva da tufafinsu Yana sane da abin da suke voyewa da kuma abin da suke bayyanawa. Lalle Shi (Allah) Masanin abin da yake cikin zukata ne



Surah: Suratu Hud

Ayah : 6

۞وَمَا مِن دَآبَّةٖ فِي ٱلۡأَرۡضِ إِلَّا عَلَى ٱللَّهِ رِزۡقُهَا وَيَعۡلَمُ مُسۡتَقَرَّهَا وَمُسۡتَوۡدَعَهَاۚ كُلّٞ فِي كِتَٰبٖ مُّبِينٖ

Kuma babu wata dabba a ban qasa face arzikinta yana hannun Allah, kuma Yana sane da matabbatarta da ma’ajiyarta[1]. Dukkanin wannan yana nan a cikin littafi mabayyani (shi ne Lauhul Mahafuzu)


1- Watau ya san wurin zamansu da wurin tafiye-tafiyensu, ya san inda za su mutu a binne su.


Surah: Suratu Hud

Ayah : 9

وَلَئِنۡ أَذَقۡنَا ٱلۡإِنسَٰنَ مِنَّا رَحۡمَةٗ ثُمَّ نَزَعۡنَٰهَا مِنۡهُ إِنَّهُۥ لَيَـُٔوسٞ كَفُورٞ

Kuma tabbas idan Muka xanxana wa mutum wata rahama daga gare Mu sannan Muka karve ta daga gare shi, lalle shi mai yawan yanke qauna ne, mai kuma yawan kafirci



Surah: Suratu Hud

Ayah : 14

فَإِلَّمۡ يَسۡتَجِيبُواْ لَكُمۡ فَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّمَآ أُنزِلَ بِعِلۡمِ ٱللَّهِ وَأَن لَّآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَۖ فَهَلۡ أَنتُم مُّسۡلِمُونَ

To idan ba su amsa muku ba, to ku tabbatar cewa lalle an saukar da shi ne (Alqur’ani) da sanin Allah, kuma babu wani abin bauta da gaskiya sai Shi, To shin yanzu za ku miqa wuya?



Surah: Suratu Hud

Ayah : 31

وَلَآ أَقُولُ لَكُمۡ عِندِي خَزَآئِنُ ٱللَّهِ وَلَآ أَعۡلَمُ ٱلۡغَيۡبَ وَلَآ أَقُولُ إِنِّي مَلَكٞ وَلَآ أَقُولُ لِلَّذِينَ تَزۡدَرِيٓ أَعۡيُنُكُمۡ لَن يُؤۡتِيَهُمُ ٱللَّهُ خَيۡرًاۖ ٱللَّهُ أَعۡلَمُ بِمَا فِيٓ أَنفُسِهِمۡ إِنِّيٓ إِذٗا لَّمِنَ ٱلظَّـٰلِمِينَ

“Ba kuma zan ce da ku ina da taskokin Allah ba, ban kuma san gaibu ba, kuma ba zan ce lalle ni mala’ika ne ba, ba kuma zan ce wa waxanda idanuwanku suke wulaqantawa, Allah ba zai ba su wani alheri ba. Allah ne Ya fi sanin abin da yake zukatansu. Idan na yi haka, to lalle na zamanto daga cikin azzalumai.”



Surah: Suratu Hud

Ayah : 56

إِنِّي تَوَكَّلۡتُ عَلَى ٱللَّهِ رَبِّي وَرَبِّكُمۚ مَّا مِن دَآبَّةٍ إِلَّا هُوَ ءَاخِذُۢ بِنَاصِيَتِهَآۚ إِنَّ رَبِّي عَلَىٰ صِرَٰطٖ مُّسۡتَقِيمٖ

“Lalle ni na dogara ga Allah, Ubangijina kuma Ubangijinku. Babu wata dabba face Shi ne Yake riqe da makwarkwaxarta. Lalle Ubangijina a kan tafarki madaidaici Yake



Surah: Suratu Hud

Ayah : 66

فَلَمَّا جَآءَ أَمۡرُنَا نَجَّيۡنَا صَٰلِحٗا وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ مَعَهُۥ بِرَحۡمَةٖ مِّنَّا وَمِنۡ خِزۡيِ يَوۡمِئِذٍۚ إِنَّ رَبَّكَ هُوَ ٱلۡقَوِيُّ ٱلۡعَزِيزُ

To lokacin da umarninmu ya zo sai Muka tserar da Salihu shi da waxanda suka yi imani tare da shi saboda wata rahama daga gare mu, kuma (Muka tserar da su) daga kunyatar wannan rana. Lalle Ubangijinka Shi ne Mai qarfi Mabuwayi



Surah: Suratu Hud

Ayah : 88

قَالَ يَٰقَوۡمِ أَرَءَيۡتُمۡ إِن كُنتُ عَلَىٰ بَيِّنَةٖ مِّن رَّبِّي وَرَزَقَنِي مِنۡهُ رِزۡقًا حَسَنٗاۚ وَمَآ أُرِيدُ أَنۡ أُخَالِفَكُمۡ إِلَىٰ مَآ أَنۡهَىٰكُمۡ عَنۡهُۚ إِنۡ أُرِيدُ إِلَّا ٱلۡإِصۡلَٰحَ مَا ٱسۡتَطَعۡتُۚ وَمَا تَوۡفِيقِيٓ إِلَّا بِٱللَّهِۚ عَلَيۡهِ تَوَكَّلۡتُ وَإِلَيۡهِ أُنِيبُ

Ya ce: “Ya ku mutanena, me kuke gani ne, idan na kasance a kan bayyananniyar hujja daga Ubangijina, Ya kuma arzuta ni da kyakkyawan arziki daga gare Shi. Ba na kuma nufin in aikata abin da nake hana ku aikata shi. Ba komai nake nufi ba sai gyara iyakacin ikona. Kuma dacewata daga Allah kaxai take. A gare Shi na dogara, kuma zuwa gare Shi ne zan koma



Surah: Suratu Hud

Ayah : 107

خَٰلِدِينَ فِيهَا مَا دَامَتِ ٱلسَّمَٰوَٰتُ وَٱلۡأَرۡضُ إِلَّا مَا شَآءَ رَبُّكَۚ إِنَّ رَبَّكَ فَعَّالٞ لِّمَا يُرِيدُ

Suna madawwama a cikinta matuqar sammai da qasa suna nan a dawwame, sai dai abin da Ubangijinka Ya ga dama. Lalle Ubangijinka Mai yawan aikata abin da Yake nufi ne



Surah: Suratu Hud

Ayah : 108

۞وَأَمَّا ٱلَّذِينَ سُعِدُواْ فَفِي ٱلۡجَنَّةِ خَٰلِدِينَ فِيهَا مَا دَامَتِ ٱلسَّمَٰوَٰتُ وَٱلۡأَرۡضُ إِلَّا مَا شَآءَ رَبُّكَۖ عَطَآءً غَيۡرَ مَجۡذُوذٖ

Amma waxanda aka yi musu dace da rabauta, to suna cikin Aljanna suna masu dawwama a cikinta matuqar sammai da qasa suna nan a dawwame, sai dai abin da Ubangijinka Ya ga dama, (wannan) kyauta ce marar yankewa



Surah: Suratu Hud

Ayah : 112

فَٱسۡتَقِمۡ كَمَآ أُمِرۡتَ وَمَن تَابَ مَعَكَ وَلَا تَطۡغَوۡاْۚ إِنَّهُۥ بِمَا تَعۡمَلُونَ بَصِيرٞ

Don haka sai ka tsaya totar kamar yadda aka umarce ka kai da waxanda suka tuba tare da kai, kada kuwa ku wuce iyaka. Lalle Shi (Allah) Mai ganin abin da kuke aikatawa ne



Surah: Suratu Hud

Ayah : 123

وَلِلَّهِ غَيۡبُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَإِلَيۡهِ يُرۡجَعُ ٱلۡأَمۡرُ كُلُّهُۥ فَٱعۡبُدۡهُ وَتَوَكَّلۡ عَلَيۡهِۚ وَمَا رَبُّكَ بِغَٰفِلٍ عَمَّا تَعۡمَلُونَ

Kuma (sanin) gaibu na sammai da na qasa na Allah ne, kuma gare Shi ake komar da dukkanin al’amari. To ka bauta masa kuma ka dogara gare Shi. Ubangijinka kuwa ba gafalalle ba ne ga abin da kuke aikatawa



Surah: Suratu Yusuf 

Ayah : 38

وَٱتَّبَعۡتُ مِلَّةَ ءَابَآءِيٓ إِبۡرَٰهِيمَ وَإِسۡحَٰقَ وَيَعۡقُوبَۚ مَا كَانَ لَنَآ أَن نُّشۡرِكَ بِٱللَّهِ مِن شَيۡءٖۚ ذَٰلِكَ مِن فَضۡلِ ٱللَّهِ عَلَيۡنَا وَعَلَى ٱلنَّاسِ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَ ٱلنَّاسِ لَا يَشۡكُرُونَ

“Na kuma bi hanyar iyayena Ibrahimu da Is’haqa da kuma Yaqubu. Bai kamace mu ba a ce mu tara wani abu da Allah. Wannan yana daga falalar Allah a gare mu da kuma sauran mutane, sai dai kuma yawancin mutane ba sa godewa



Surah: Suratu Yusuf 

Ayah : 40

مَا تَعۡبُدُونَ مِن دُونِهِۦٓ إِلَّآ أَسۡمَآءٗ سَمَّيۡتُمُوهَآ أَنتُمۡ وَءَابَآؤُكُم مَّآ أَنزَلَ ٱللَّهُ بِهَا مِن سُلۡطَٰنٍۚ إِنِ ٱلۡحُكۡمُ إِلَّا لِلَّهِ أَمَرَ أَلَّا تَعۡبُدُوٓاْ إِلَّآ إِيَّاهُۚ ذَٰلِكَ ٱلدِّينُ ٱلۡقَيِّمُ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَ ٱلنَّاسِ لَا يَعۡلَمُونَ

“Ba komai kuke bauta wa ba- bayan Allah- sai wasu sunaye da kuka qaga ku da iyayenku, waxanda Allah bai saukar da wata hujja game da su ba. Hukunci na Allah ne kawai; Ya yi umarni cewa kada ku bauta wa kowa sai Shi kaxai. Wannan shi ne addini miqaqqe, sai dai yawancin mutane ba sa sanin (haka)