Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 70

إِذۡ قَالَ لِأَبِيهِ وَقَوۡمِهِۦ مَا تَعۡبُدُونَ

Lokacin da ya ce wa babansa da kuma mutanensa: “Me kuke bauta wa?”



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 71

قَالُواْ نَعۡبُدُ أَصۡنَامٗا فَنَظَلُّ لَهَا عَٰكِفِينَ

Suka ce: “Muna bauta wa gumaka ne, sai mukan duqufa wajen bautarsu.”



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 72

قَالَ هَلۡ يَسۡمَعُونَكُمۡ إِذۡ تَدۡعُونَ

(Ibrahimu) ya ce: “Shin suna jin ku kuwa lokacin da kuke kiran su?



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 73

أَوۡ يَنفَعُونَكُمۡ أَوۡ يَضُرُّونَ

“Ko kuwa suna amfanar ku ne, ko suna cutarwa?”



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 74

قَالُواْ بَلۡ وَجَدۡنَآ ءَابَآءَنَا كَذَٰلِكَ يَفۡعَلُونَ

Suka ce: “A’a; mun sami iyayenmu ne suna aikata kamar haka.”



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 75

قَالَ أَفَرَءَيۡتُم مَّا كُنتُمۡ تَعۡبُدُونَ

(Ibrahimu) ya ce: “Yanzu kun ga abin nan da kuka kasance kuna bautawa



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 76

أَنتُمۡ وَءَابَآؤُكُمُ ٱلۡأَقۡدَمُونَ

“Ku da iyayenku da suka gabata



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 77

فَإِنَّهُمۡ عَدُوّٞ لِّيٓ إِلَّا رَبَّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

“To lalle su abokan gabata ne sai fa Ubangijin talikai



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 78

ٱلَّذِي خَلَقَنِي فَهُوَ يَهۡدِينِ

“Wanda Ya halicce ni, to Shi ne Yake shiryar da ni



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 79

وَٱلَّذِي هُوَ يُطۡعِمُنِي وَيَسۡقِينِ

“Kuma wanda Shi ne Yake ciyar da ni kuma Yake shayar da ni



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 80

وَإِذَا مَرِضۡتُ فَهُوَ يَشۡفِينِ

“Idan kuma na yi rashin lafiya, to Shi ne zai warkar da ni



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 81

وَٱلَّذِي يُمِيتُنِي ثُمَّ يُحۡيِينِ

“Kuma wanda zai kashe ni sannan Ya (sake) raya ni



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 82

وَٱلَّذِيٓ أَطۡمَعُ أَن يَغۡفِرَ لِي خَطِيٓـَٔتِي يَوۡمَ ٱلدِّينِ

“Wanda kuma nake kwaxayin Ya gafarta min kurakuraina ranar sakamako



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 83

رَبِّ هَبۡ لِي حُكۡمٗا وَأَلۡحِقۡنِي بِٱلصَّـٰلِحِينَ

“Ubangijina Ka hore min ilimi, kuma Ka haxa ni da (bayinka) na gari



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 84

وَٱجۡعَل لِّي لِسَانَ صِدۡقٖ فِي ٱلۡأٓخِرِينَ

“Kuma Ka sanya min abin kyakkyawan ambato cikin ‘yan baya



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 85

وَٱجۡعَلۡنِي مِن وَرَثَةِ جَنَّةِ ٱلنَّعِيمِ

“Kuma Ka sanya ni cikin magada Aljannar ni’ima



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 86

وَٱغۡفِرۡ لِأَبِيٓ إِنَّهُۥ كَانَ مِنَ ٱلضَّآلِّينَ

“Kuma Ka gafarta wa babana, lalle shi ya zamo cikin vatattu.[1]


1- Ya yi masa wannan addu’a ne tun gabanin a hana shi, kamar yadda ya zo a cikin Suratut Tauba, aya ta 114.


Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 87

وَلَا تُخۡزِنِي يَوۡمَ يُبۡعَثُونَ

“Kada kuma Ka kunyata ni ranar da za a tashe su



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 88

يَوۡمَ لَا يَنفَعُ مَالٞ وَلَا بَنُونَ

“Ranar da dukiya da ‘ya’yaye ba sa amfani



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 89

إِلَّا مَنۡ أَتَى ٱللَّهَ بِقَلۡبٖ سَلِيمٖ

“Sai dai wanda ya zo wa Allah da lafiyayyar zuciya.”



Surah: Suratul Ankabut

Ayah : 16

وَإِبۡرَٰهِيمَ إِذۡ قَالَ لِقَوۡمِهِ ٱعۡبُدُواْ ٱللَّهَ وَٱتَّقُوهُۖ ذَٰلِكُمۡ خَيۡرٞ لَّكُمۡ إِن كُنتُمۡ تَعۡلَمُونَ

Kuma (ka tuna) Ibrahimu lokacin da ya ce da mutanensa: “Ku bauta wa Allah, kuma ku kiyaye dokokinsa, wannan shi ya fi muku alheri in kun kasance kun san (haka)



Surah: Suratul Ankabut

Ayah : 17

إِنَّمَا تَعۡبُدُونَ مِن دُونِ ٱللَّهِ أَوۡثَٰنٗا وَتَخۡلُقُونَ إِفۡكًاۚ إِنَّ ٱلَّذِينَ تَعۡبُدُونَ مِن دُونِ ٱللَّهِ لَا يَمۡلِكُونَ لَكُمۡ رِزۡقٗا فَٱبۡتَغُواْ عِندَ ٱللَّهِ ٱلرِّزۡقَ وَٱعۡبُدُوهُ وَٱشۡكُرُواْ لَهُۥٓۖ إِلَيۡهِ تُرۡجَعُونَ

Lalle abin da kuke bauta wa ba Allah ba gumaka ne kawai, kuna kuma qirqirar qarya ne[1]. Lalle waxanda kuke bauta wa ba Allah ba, ba su mallaki wani arziki ba gare ku, sai ku nemi arziki a wurin Allah, kuma ku bauta masa, ku kuma gode masa; gare Shi ne kawai za a mayar da ku


1- Domin su ne suke sassaqa su da hannayensu suke kuma sanya musu sunaye sannan su bauta musu.


Surah: Suratul Ankabut

Ayah : 18

وَإِن تُكَذِّبُواْ فَقَدۡ كَذَّبَ أُمَمٞ مِّن قَبۡلِكُمۡۖ وَمَا عَلَى ٱلرَّسُولِ إِلَّا ٱلۡبَلَٰغُ ٱلۡمُبِينُ

Idan kuma kuka qaryata, to haqiqa da ma wasu al’ummun da suke gabaninku sun qaryata; ba abin da yake kan Manzo sai isar da saqo mabayyani



Surah: Suratul Ankabut

Ayah : 24

فَمَا كَانَ جَوَابَ قَوۡمِهِۦٓ إِلَّآ أَن قَالُواْ ٱقۡتُلُوهُ أَوۡ حَرِّقُوهُ فَأَنجَىٰهُ ٱللَّهُ مِنَ ٱلنَّارِۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَٰتٖ لِّقَوۡمٖ يُؤۡمِنُونَ

To ba wani jawabi da ya fito daga bakin mutanensa sai cewa da suka yi: “Ku kashe shi ko kuma ku qone shi!” Sai Allah Ya tserar da shi daga wutar. Lalle a game da wannan tabbas akwai ayoyi ga mutanen da suka yi imani



Surah: Suratul Ankabut

Ayah : 25

وَقَالَ إِنَّمَا ٱتَّخَذۡتُم مِّن دُونِ ٱللَّهِ أَوۡثَٰنٗا مَّوَدَّةَ بَيۡنِكُمۡ فِي ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَاۖ ثُمَّ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ يَكۡفُرُ بَعۡضُكُم بِبَعۡضٖ وَيَلۡعَنُ بَعۡضُكُم بَعۡضٗا وَمَأۡوَىٰكُمُ ٱلنَّارُ وَمَا لَكُم مِّن نَّـٰصِرِينَ

Kuma ya ce (da su): “Lalle ba abin da kuka riqa wanin Allah sai gumaka kawai don qauna da take tsakaninku a rayuwar duniya; sannan ranar alqiyama wasunku za su kafirce wa wasu, kuma wasunku za su la’anci wasu, makomarku kuma wuta ce, ba ku da kuwa wasu mataimaka.”



Surah: Suratul Ankabut

Ayah : 26

۞فَـَٔامَنَ لَهُۥ لُوطٞۘ وَقَالَ إِنِّي مُهَاجِرٌ إِلَىٰ رَبِّيٓۖ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡحَكِيمُ

Sai Luxu ya yi imani da shi. (Sai Ibrahimu) kuma ya ce: “Lalle ni mai yin hijira ne zuwa ga Ubangijina; lalle Shi Mabuwayi ne, Mai hikima.”



Surah: Suratul Ankabut

Ayah : 27

وَوَهَبۡنَا لَهُۥٓ إِسۡحَٰقَ وَيَعۡقُوبَ وَجَعَلۡنَا فِي ذُرِّيَّتِهِ ٱلنُّبُوَّةَ وَٱلۡكِتَٰبَ وَءَاتَيۡنَٰهُ أَجۡرَهُۥ فِي ٱلدُّنۡيَاۖ وَإِنَّهُۥ فِي ٱلۡأٓخِرَةِ لَمِنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ

Muka kuma yi masa baiwa da (xansa) Is’haqa da kuma (jikansa) Ya’aqubu, Muka kuma sanya annabta da littafi a cikin zuriyarsa, Muka kuma ba shi ladansa a duniya; kuma lalle shi a lahira tabbas yana cikin salihai



Surah: Suratul Ankabut

Ayah : 31

وَلَمَّا جَآءَتۡ رُسُلُنَآ إِبۡرَٰهِيمَ بِٱلۡبُشۡرَىٰ قَالُوٓاْ إِنَّا مُهۡلِكُوٓاْ أَهۡلِ هَٰذِهِ ٱلۡقَرۡيَةِۖ إِنَّ أَهۡلَهَا كَانُواْ ظَٰلِمِينَ

Lokacin kuwa da manzanninmu suka zo wa Ibrahimu da albishir[1], sai suka ce: “Lalle mu masu hallaka mutanen wannan alqaryar ne, lalle mutanenta sun kasance azzalumai.”


1- Albishir na samun haihuwar xansa Ishaq () da kuma jikansa Ya’aqub ().


Surah: Suratul Ankabut

Ayah : 32

قَالَ إِنَّ فِيهَا لُوطٗاۚ قَالُواْ نَحۡنُ أَعۡلَمُ بِمَن فِيهَاۖ لَنُنَجِّيَنَّهُۥ وَأَهۡلَهُۥٓ إِلَّا ٱمۡرَأَتَهُۥ كَانَتۡ مِنَ ٱلۡغَٰبِرِينَ

Sai (Ibrahimu) ya ce: “Lalle Luxu yana cikinta”. Sai suka ce: “Mu muka fi sanin waxanda suke cikinta; tabbas za mu tserar da shi tare da iyalinsa, sai matarsa kawai da ta kasance cikin waxanda za su yi saura (a hallaka su tare)”



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 83

۞وَإِنَّ مِن شِيعَتِهِۦ لَإِبۡرَٰهِيمَ

Lalle kuma Ibrahimu yana daga mabiya addininsa