فَإِنَّ ٱلۡجَنَّةَ هِيَ ٱلۡمَأۡوَىٰ
To lalle Aljanna ita ce makoma
Share :
يَسۡـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلسَّاعَةِ أَيَّانَ مُرۡسَىٰهَا
Suna tambayar ka game da alqiyama, yaushe ne lokacinta?
فِيمَ أَنتَ مِن ذِكۡرَىٰهَآ
Me ya gama ka da ambaton lokacinta?
إِلَىٰ رَبِّكَ مُنتَهَىٰهَآ
Zuwa ga Ubangijinka ne iyakacin saninta yake[1]
1- Watau Allah ne kaxai ya san lokacin aukuwarta.
إِنَّمَآ أَنتَ مُنذِرُ مَن يَخۡشَىٰهَا
Kai dai kawai mai gargaxin wanda yake tsoron ta ne
كَأَنَّهُمۡ يَوۡمَ يَرَوۡنَهَا لَمۡ يَلۡبَثُوٓاْ إِلَّا عَشِيَّةً أَوۡ ضُحَىٰهَا
Kai ka ce su ranar da za su gan ta ba su zauna ba (a duniya) face wani yammaci ko kuma hantsinta
فَإِذَا جَآءَتِ ٱلصَّآخَّةُ
Sannan idan mai sa kurunta ta zo (watau busa ta farko)
يَوۡمَ يَفِرُّ ٱلۡمَرۡءُ مِنۡ أَخِيهِ
A ranar da mutum yake guje wa xan’uwansa
وَأُمِّهِۦ وَأَبِيهِ
Da uwarsa da ubansa
وَصَٰحِبَتِهِۦ وَبَنِيهِ
Da matarsa da ‘ya’yansa
لِكُلِّ ٱمۡرِيٕٖ مِّنۡهُمۡ يَوۡمَئِذٖ شَأۡنٞ يُغۡنِيهِ
Kowane mutum daga cikinsu a wannan ranar yana da lamarin da ya sha kansa
وُجُوهٞ يَوۡمَئِذٖ مُّسۡفِرَةٞ
Wasu fuskoki a wannan ranar masu haske ne
ضَاحِكَةٞ مُّسۡتَبۡشِرَةٞ
Masu dariya, masu farin ciki
وَوُجُوهٞ يَوۡمَئِذٍ عَلَيۡهَا غَبَرَةٞ
Wasu fuskokin kuma a ranar akwai qura a kansu
تَرۡهَقُهَا قَتَرَةٌ
Baqin ciki zai lulluve su
أُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡكَفَرَةُ ٱلۡفَجَرَةُ
Waxannan su ne kafirai mavarnata
وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا يَوۡمُ ٱلدِّينِ
Kuma kai me ya sanar da kai mece ce ranar sakamako?
ثُمَّ مَآ أَدۡرَىٰكَ مَا يَوۡمُ ٱلدِّينِ
Sannan me ya sanar da kai mece ce ranar sakamako?
يَوۡمَ لَا تَمۡلِكُ نَفۡسٞ لِّنَفۡسٖ شَيۡـٔٗاۖ وَٱلۡأَمۡرُ يَوۡمَئِذٖ لِّلَّهِ
(Ita ce) ranar da wani rai ba ya mallakar wani amfani ga wani rai; al’amari kuwa (gaba xayansa) a wannan ranar yana ga Allah
كَلَّآۖ إِذَا دُكَّتِ ٱلۡأَرۡضُ دَكّٗا دَكّٗا
Ba haka ne ba, idan aka girgiza qasa matuqar girgiza
وَجَآءَ رَبُّكَ وَٱلۡمَلَكُ صَفّٗا صَفّٗا
Ubangijinka kuma Ya zo[1] tare da mala’iku sahu-sahu
1- Watau don yin hukunci a tsakanin bayinsa.
وَجِاْيٓءَ يَوۡمَئِذِۭ بِجَهَنَّمَۚ يَوۡمَئِذٖ يَتَذَكَّرُ ٱلۡإِنسَٰنُ وَأَنَّىٰ لَهُ ٱلذِّكۡرَىٰ
Aka kuma zo da Jahannama a wannan ranar. To fa a wannan ranar ne mutum zai tuna (sakacinsa), ta yaya wannan tunawar za ta yi masa amfani?
يَقُولُ يَٰلَيۡتَنِي قَدَّمۡتُ لِحَيَاتِي
Zai ce: “Kaitona, ina ma da na gabatar (da ayyukan alheri) a rayuwata!”
فَيَوۡمَئِذٖ لَّا يُعَذِّبُ عَذَابَهُۥٓ أَحَدٞ
To a wannan ranar ba wani xaya da zai yi azaba irin azabarsa (watau Allah)
وَلَا يُوثِقُ وَثَاقَهُۥٓ أَحَدٞ
Ba kuma xaya da zai yi xauri irin xaurinsa
يَـٰٓأَيَّتُهَا ٱلنَّفۡسُ ٱلۡمُطۡمَئِنَّةُ
(Za a ce): Ya kai wannan rai mai nutsuwa
ٱرۡجِعِيٓ إِلَىٰ رَبِّكِ رَاضِيَةٗ مَّرۡضِيَّةٗ
Ka koma zuwa ga Ubangijinka kana mai yarda (da sakamako), abin yarda
فَٱدۡخُلِي فِي عِبَٰدِي
Don haka ka shiga cikin bayina
وَٱدۡخُلِي جَنَّتِي
Ka kuma shiga Aljannata
إِذَا زُلۡزِلَتِ ٱلۡأَرۡضُ زِلۡزَالَهَا
Idan aka girgiza qasa matuqar girgiza ta