Surah: Suratun Nazi’at

Ayah : 41

فَإِنَّ ٱلۡجَنَّةَ هِيَ ٱلۡمَأۡوَىٰ

To lalle Aljanna ita ce makoma



Surah: Suratun Nazi’at

Ayah : 42

يَسۡـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلسَّاعَةِ أَيَّانَ مُرۡسَىٰهَا

Suna tambayar ka game da alqiyama, yaushe ne lokacinta?



Surah: Suratun Nazi’at

Ayah : 43

فِيمَ أَنتَ مِن ذِكۡرَىٰهَآ

Me ya gama ka da ambaton lokacinta?



Surah: Suratun Nazi’at

Ayah : 44

إِلَىٰ رَبِّكَ مُنتَهَىٰهَآ

Zuwa ga Ubangijinka ne iyakacin saninta yake[1]


1- Watau Allah ne kaxai ya san lokacin aukuwarta.


Surah: Suratun Nazi’at

Ayah : 45

إِنَّمَآ أَنتَ مُنذِرُ مَن يَخۡشَىٰهَا

Kai dai kawai mai gargaxin wanda yake tsoron ta ne



Surah: Suratun Nazi’at

Ayah : 46

كَأَنَّهُمۡ يَوۡمَ يَرَوۡنَهَا لَمۡ يَلۡبَثُوٓاْ إِلَّا عَشِيَّةً أَوۡ ضُحَىٰهَا

Kai ka ce su ranar da za su gan ta ba su zauna ba (a duniya) face wani yammaci ko kuma hantsinta



Surah: Suratu Abasa

Ayah : 33

فَإِذَا جَآءَتِ ٱلصَّآخَّةُ

Sannan idan mai sa kurunta ta zo (watau busa ta farko)



Surah: Suratu Abasa

Ayah : 34

يَوۡمَ يَفِرُّ ٱلۡمَرۡءُ مِنۡ أَخِيهِ

A ranar da mutum yake guje wa xan’uwansa



Surah: Suratu Abasa

Ayah : 35

وَأُمِّهِۦ وَأَبِيهِ

Da uwarsa da ubansa



Surah: Suratu Abasa

Ayah : 36

وَصَٰحِبَتِهِۦ وَبَنِيهِ

Da matarsa da ‘ya’yansa



Surah: Suratu Abasa

Ayah : 37

لِكُلِّ ٱمۡرِيٕٖ مِّنۡهُمۡ يَوۡمَئِذٖ شَأۡنٞ يُغۡنِيهِ

Kowane mutum daga cikinsu a wannan ranar yana da lamarin da ya sha kansa



Surah: Suratu Abasa

Ayah : 38

وُجُوهٞ يَوۡمَئِذٖ مُّسۡفِرَةٞ

Wasu fuskoki a wannan ranar masu haske ne



Surah: Suratu Abasa

Ayah : 39

ضَاحِكَةٞ مُّسۡتَبۡشِرَةٞ

Masu dariya, masu farin ciki



Surah: Suratu Abasa

Ayah : 40

وَوُجُوهٞ يَوۡمَئِذٍ عَلَيۡهَا غَبَرَةٞ

Wasu fuskokin kuma a ranar akwai qura a kansu



Surah: Suratu Abasa

Ayah : 41

تَرۡهَقُهَا قَتَرَةٌ

Baqin ciki zai lulluve su



Surah: Suratu Abasa

Ayah : 42

أُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡكَفَرَةُ ٱلۡفَجَرَةُ

Waxannan su ne kafirai mavarnata



Surah: Suratul Infixar

Ayah : 17

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا يَوۡمُ ٱلدِّينِ

Kuma kai me ya sanar da kai mece ce ranar sakamako?



Surah: Suratul Infixar

Ayah : 18

ثُمَّ مَآ أَدۡرَىٰكَ مَا يَوۡمُ ٱلدِّينِ

Sannan me ya sanar da kai mece ce ranar sakamako?



Surah: Suratul Infixar

Ayah : 19

يَوۡمَ لَا تَمۡلِكُ نَفۡسٞ لِّنَفۡسٖ شَيۡـٔٗاۖ وَٱلۡأَمۡرُ يَوۡمَئِذٖ لِّلَّهِ

(Ita ce) ranar da wani rai ba ya mallakar wani amfani ga wani rai; al’amari kuwa (gaba xayansa) a wannan ranar yana ga Allah



Surah: Suratul Fajr

Ayah : 21

كَلَّآۖ إِذَا دُكَّتِ ٱلۡأَرۡضُ دَكّٗا دَكّٗا

Ba haka ne ba, idan aka girgiza qasa matuqar girgiza



Surah: Suratul Fajr

Ayah : 22

وَجَآءَ رَبُّكَ وَٱلۡمَلَكُ صَفّٗا صَفّٗا

Ubangijinka kuma Ya zo[1] tare da mala’iku sahu-sahu


1- Watau don yin hukunci a tsakanin bayinsa.


Surah: Suratul Fajr

Ayah : 23

وَجِاْيٓءَ يَوۡمَئِذِۭ بِجَهَنَّمَۚ يَوۡمَئِذٖ يَتَذَكَّرُ ٱلۡإِنسَٰنُ وَأَنَّىٰ لَهُ ٱلذِّكۡرَىٰ

Aka kuma zo da Jahannama a wannan ranar. To fa a wannan ranar ne mutum zai tuna (sakacinsa), ta yaya wannan tunawar za ta yi masa amfani?



Surah: Suratul Fajr

Ayah : 24

يَقُولُ يَٰلَيۡتَنِي قَدَّمۡتُ لِحَيَاتِي

Zai ce: “Kaitona, ina ma da na gabatar (da ayyukan alheri) a rayuwata!”



Surah: Suratul Fajr

Ayah : 25

فَيَوۡمَئِذٖ لَّا يُعَذِّبُ عَذَابَهُۥٓ أَحَدٞ

To a wannan ranar ba wani xaya da zai yi azaba irin azabarsa (watau Allah)



Surah: Suratul Fajr

Ayah : 26

وَلَا يُوثِقُ وَثَاقَهُۥٓ أَحَدٞ

Ba kuma xaya da zai yi xauri irin xaurinsa



Surah: Suratul Fajr

Ayah : 27

يَـٰٓأَيَّتُهَا ٱلنَّفۡسُ ٱلۡمُطۡمَئِنَّةُ

(Za a ce): Ya kai wannan rai mai nutsuwa



Surah: Suratul Fajr

Ayah : 28

ٱرۡجِعِيٓ إِلَىٰ رَبِّكِ رَاضِيَةٗ مَّرۡضِيَّةٗ

Ka koma zuwa ga Ubangijinka kana mai yarda (da sakamako), abin yarda



Surah: Suratul Fajr

Ayah : 29

فَٱدۡخُلِي فِي عِبَٰدِي

Don haka ka shiga cikin bayina



Surah: Suratul Fajr

Ayah : 30

وَٱدۡخُلِي جَنَّتِي

Ka kuma shiga Aljannata



Surah: Suratuz Zalzala

Ayah : 1

إِذَا زُلۡزِلَتِ ٱلۡأَرۡضُ زِلۡزَالَهَا

Idan aka girgiza qasa matuqar girgiza ta