Surah: Suratul Jasiya

Ayah : 3

إِنَّ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ لَأٓيَٰتٖ لِّلۡمُؤۡمِنِينَ

Lalle a cikin sammai da qasa tabbas akwai ayoyi ga muminai



Surah: Suratul Jasiya

Ayah : 4

وَفِي خَلۡقِكُمۡ وَمَا يَبُثُّ مِن دَآبَّةٍ ءَايَٰتٞ لِّقَوۡمٖ يُوقِنُونَ

A cikin halittarku ma da abin da Yake bazawa na dabbobi, akwai ayoyi ga mutane masu sakankancewa



Surah: Suratu Qaf 

Ayah : 15

أَفَعَيِينَا بِٱلۡخَلۡقِ ٱلۡأَوَّلِۚ بَلۡ هُمۡ فِي لَبۡسٖ مِّنۡ خَلۡقٖ جَدِيدٖ

Shin Mun gaza ne da halittar farko? A’a, su dai suna cikin shakka ne game da sake halitta



Surah: Suratux Xur

Ayah : 35

أَمۡ خُلِقُواْ مِنۡ غَيۡرِ شَيۡءٍ أَمۡ هُمُ ٱلۡخَٰلِقُونَ

Ko kuwa an halicce su ne ba da wani mai halitta ba, ko kuwa su ne masu halittar (kansu)?



Surah: Suratul Mulk

Ayah : 2

ٱلَّذِي خَلَقَ ٱلۡمَوۡتَ وَٱلۡحَيَوٰةَ لِيَبۡلُوَكُمۡ أَيُّكُمۡ أَحۡسَنُ عَمَلٗاۚ وَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡغَفُورُ

Wanda Ya halicci mutuwa da rayuwa don Ya jarraba ku (Ya bayyana) wane ne a cikinku ya fi kyakkyawan aiki? Shi kuma Mabuwayi ne, Mai gafara



Surah: Suratul Mulk

Ayah : 3

ٱلَّذِي خَلَقَ سَبۡعَ سَمَٰوَٰتٖ طِبَاقٗاۖ مَّا تَرَىٰ فِي خَلۡقِ ٱلرَّحۡمَٰنِ مِن تَفَٰوُتٖۖ فَٱرۡجِعِ ٱلۡبَصَرَ هَلۡ تَرَىٰ مِن فُطُورٖ

Wanda Ya halicci sammai bakwai hawa-hawa; ba za ka ga wata tangarxa cikin halittar (Allah) Mai rahama ba. Ka maimaita dubanka, shin za ka ga wata tsaga?



Surah: Suratun Nazi’at

Ayah : 27

ءَأَنتُمۡ أَشَدُّ خَلۡقًا أَمِ ٱلسَّمَآءُۚ بَنَىٰهَا

Yanzu ku ne halittarku ta fi tsanani ko kuwa sama wadda Shi ne Ya gina ta?



Surah: Suratun Nazi’at

Ayah : 28

رَفَعَ سَمۡكَهَا فَسَوَّىٰهَا

Ya xaukaka rufinta Ya kuma daidaita ta[1]


1- Watau ya zama babu wata varaka ko tsagewa ko wani aibi tare da ita.


Surah: Suratun Nazi’at

Ayah : 29

وَأَغۡطَشَ لَيۡلَهَا وَأَخۡرَجَ ضُحَىٰهَا

Ya lulluve darenta da duhu Ya kuma fitar da hasken hantsinta



Surah: Suratun Nazi’at

Ayah : 30

وَٱلۡأَرۡضَ بَعۡدَ ذَٰلِكَ دَحَىٰهَآ

Qasa kuma bayan haka Ya shimfixa ta



Surah: Suratun Nazi’at

Ayah : 31

أَخۡرَجَ مِنۡهَا مَآءَهَا وَمَرۡعَىٰهَا

Ya fitar da ruwanta da makiyayarta daga gare ta



Surah: Suratun Nazi’at

Ayah : 32

وَٱلۡجِبَالَ أَرۡسَىٰهَا

Duwatsu kuma Ya kafa su



Surah: Suratun Nazi’at

Ayah : 33

مَتَٰعٗا لَّكُمۡ وَلِأَنۡعَٰمِكُمۡ

Don jin daxinku da na dabbobinku



Surah: Suratux Xariq

Ayah : 5

فَلۡيَنظُرِ ٱلۡإِنسَٰنُ مِمَّ خُلِقَ

To mutum ya duba mana, daga me aka halicce shi?



Surah: Suratux Xariq

Ayah : 6

خُلِقَ مِن مَّآءٖ دَافِقٖ

An halicce shi ne daga wani ruwa mai ingizar juna[1]


1- Watau maniyyi.


Surah: Suratul Ghashiya

Ayah : 17

أَفَلَا يَنظُرُونَ إِلَى ٱلۡإِبِلِ كَيۡفَ خُلِقَتۡ

Shin ba sa duban raqumi yadda aka halicce shi?