Surah: Suratul Baqara

Ayah : 196

وَأَتِمُّواْ ٱلۡحَجَّ وَٱلۡعُمۡرَةَ لِلَّهِۚ فَإِنۡ أُحۡصِرۡتُمۡ فَمَا ٱسۡتَيۡسَرَ مِنَ ٱلۡهَدۡيِۖ وَلَا تَحۡلِقُواْ رُءُوسَكُمۡ حَتَّىٰ يَبۡلُغَ ٱلۡهَدۡيُ مَحِلَّهُۥۚ فَمَن كَانَ مِنكُم مَّرِيضًا أَوۡ بِهِۦٓ أَذٗى مِّن رَّأۡسِهِۦ فَفِدۡيَةٞ مِّن صِيَامٍ أَوۡ صَدَقَةٍ أَوۡ نُسُكٖۚ فَإِذَآ أَمِنتُمۡ فَمَن تَمَتَّعَ بِٱلۡعُمۡرَةِ إِلَى ٱلۡحَجِّ فَمَا ٱسۡتَيۡسَرَ مِنَ ٱلۡهَدۡيِۚ فَمَن لَّمۡ يَجِدۡ فَصِيَامُ ثَلَٰثَةِ أَيَّامٖ فِي ٱلۡحَجِّ وَسَبۡعَةٍ إِذَا رَجَعۡتُمۡۗ تِلۡكَ عَشَرَةٞ كَامِلَةٞۗ ذَٰلِكَ لِمَن لَّمۡ يَكُنۡ أَهۡلُهُۥ حَاضِرِي ٱلۡمَسۡجِدِ ٱلۡحَرَامِۚ وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ شَدِيدُ ٱلۡعِقَابِ

Kuma ku cika aikin Hajji da umara domin Allah. To idan an tsare ku, sai ku gabatar da abin da ya sawwaqa na hadaya, kuma kada ku aske kawunanku har sai hadaya ta kai wurin yankanta. To wanda ya kasance a cikinku mara lafiya ko akwai wata cuta a kansa, (idan yayi aski) to sai ya yi fidiya ta (hanyar) yin azumi ko sadaqa ko yanka[1]. Idan kuwa kun amintu, to duk wanda ya yi tamattu’i da yin umara tare da Hajji, to sai ya yanka abin da ya sawwaqa na hadaya; amma wanda bai samu ba, sai ya yi azumin kwana uku a lokacin aikin Hajji, da kuma na kwana bakwai idan kun dawo gida. Waxannan kwana goma ke nan cikakku. Wannan hukuncin yana ga wanda iyalinsa ba sa cikin hurumin Makka ne. Kuma ku kiyaye dokokin Allah, ku sani cewa, lalle Allah Mai tsananin uquba ne


1- Watau ya yi azumi na kwana uku, ko ya ciyar da miskinai shida, kowanne ya ba shi rabin mudu ko ya yanka akuya.


Surah: Suratul Baqara

Ayah : 215

يَسۡـَٔلُونَكَ مَاذَا يُنفِقُونَۖ قُلۡ مَآ أَنفَقۡتُم مِّنۡ خَيۡرٖ فَلِلۡوَٰلِدَيۡنِ وَٱلۡأَقۡرَبِينَ وَٱلۡيَتَٰمَىٰ وَٱلۡمَسَٰكِينِ وَٱبۡنِ ٱلسَّبِيلِۗ وَمَا تَفۡعَلُواْ مِنۡ خَيۡرٖ فَإِنَّ ٱللَّهَ بِهِۦ عَلِيمٞ

Suna tambayar ka, me za su ciyar ne? Ka ce: “Duk abin da za ku ciyar na alheri, to ga mahaifa da dangi mafiya kusanci da marayu da miskinai da matafiyi. Kuma duk abin da kuka aikata na alheri, to lalle Allah Masani ne da shi.”



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 254

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ أَنفِقُواْ مِمَّا رَزَقۡنَٰكُم مِّن قَبۡلِ أَن يَأۡتِيَ يَوۡمٞ لَّا بَيۡعٞ فِيهِ وَلَا خُلَّةٞ وَلَا شَفَٰعَةٞۗ وَٱلۡكَٰفِرُونَ هُمُ ٱلظَّـٰلِمُونَ

Ya ku waxanda suka yi imani, ku ciyar daga abin da Muka arzurta ku (da shi) tun kafin wani yini ya zo wanda babu ciniki a cikinsa kuma babu abokantaka, kuma babu ceto. Kafirai kuwa su ne azzalumai



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 261

مَّثَلُ ٱلَّذِينَ يُنفِقُونَ أَمۡوَٰلَهُمۡ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ كَمَثَلِ حَبَّةٍ أَنۢبَتَتۡ سَبۡعَ سَنَابِلَ فِي كُلِّ سُنۢبُلَةٖ مِّاْئَةُ حَبَّةٖۗ وَٱللَّهُ يُضَٰعِفُ لِمَن يَشَآءُۚ وَٱللَّهُ وَٰسِعٌ عَلِيمٌ

Misalin waxanda suke ciyar da dukiyoyinsu a hanyar Allah, kamar misalin qwaya xaya ce da ta fitar da zangarniya bakwai, a cikinta kowace zangarniya kuma (aka sami) qwaya xari. Kuma Allah Yana ninninkawa ga wanda Ya ga dama, kuma Allah Mai yalwa ne, Masani



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 262

ٱلَّذِينَ يُنفِقُونَ أَمۡوَٰلَهُمۡ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ ثُمَّ لَا يُتۡبِعُونَ مَآ أَنفَقُواْ مَنّٗا وَلَآ أَذٗى لَّهُمۡ أَجۡرُهُمۡ عِندَ رَبِّهِمۡ وَلَا خَوۡفٌ عَلَيۡهِمۡ وَلَا هُمۡ يَحۡزَنُونَ

Waxanda suke ciyar da dukiyoyinsu a hanyar Allah, sannan ba sa bin abin da suka ciyar da gori ko cuta, (waxannan) suna da ladansu a wajen Ubangijinsu, kuma babu tsoro a tare da su, kuma ba za su yi baqin ciki ba



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 263

۞قَوۡلٞ مَّعۡرُوفٞ وَمَغۡفِرَةٌ خَيۡرٞ مِّن صَدَقَةٖ يَتۡبَعُهَآ أَذٗىۗ وَٱللَّهُ غَنِيٌّ حَلِيمٞ

Kyakkyawar magana da yafiya sun fi sadakar da cutarwa za ta biyo bayanta alheri. Kuma Allah Shi ne Wadatacce, Mai haquri



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 264

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لَا تُبۡطِلُواْ صَدَقَٰتِكُم بِٱلۡمَنِّ وَٱلۡأَذَىٰ كَٱلَّذِي يُنفِقُ مَالَهُۥ رِئَآءَ ٱلنَّاسِ وَلَا يُؤۡمِنُ بِٱللَّهِ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِۖ فَمَثَلُهُۥ كَمَثَلِ صَفۡوَانٍ عَلَيۡهِ تُرَابٞ فَأَصَابَهُۥ وَابِلٞ فَتَرَكَهُۥ صَلۡدٗاۖ لَّا يَقۡدِرُونَ عَلَىٰ شَيۡءٖ مِّمَّا كَسَبُواْۗ وَٱللَّهُ لَا يَهۡدِي ٱلۡقَوۡمَ ٱلۡكَٰفِرِينَ

Ya ku waxanda suka yi imani, kada ku vata sadaqoqinku da gori da cutarwa, kamar wanda yake ciyar da dukiyarsa don mutane su gani, kuma ba ya imani da Allah da ranar lahira; to misalinsa kamar misalin kamfa ne da turvaya take a kansa sai ruwan sama mamako ya same shi, sai ya bar shi tatas. Ba za su amfana da komai daga abin da suka aikata ba. Kuma Allah ba Ya shiryar da mutane kafirai



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 265

وَمَثَلُ ٱلَّذِينَ يُنفِقُونَ أَمۡوَٰلَهُمُ ٱبۡتِغَآءَ مَرۡضَاتِ ٱللَّهِ وَتَثۡبِيتٗا مِّنۡ أَنفُسِهِمۡ كَمَثَلِ جَنَّةِۭ بِرَبۡوَةٍ أَصَابَهَا وَابِلٞ فَـَٔاتَتۡ أُكُلَهَا ضِعۡفَيۡنِ فَإِن لَّمۡ يُصِبۡهَا وَابِلٞ فَطَلّٞۗ وَٱللَّهُ بِمَا تَعۡمَلُونَ بَصِيرٌ

Kuma misalin waxanda suke ciyar da dukiyoyinsu don neman yardar Allah da tabbatar da (imani) a zukatansu, kamar misalin gona ce a kan jigawa sai ruwan sama mamako ya same ta, sai ta ba da amfaninta rivi-biyu. To idan mamakon ruwan bai same ta ba, sai yayyafi (ya wadatar da ita). Kuma Allah Mai ganin abin da kuke aikatawa ne



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 267

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ أَنفِقُواْ مِن طَيِّبَٰتِ مَا كَسَبۡتُمۡ وَمِمَّآ أَخۡرَجۡنَا لَكُم مِّنَ ٱلۡأَرۡضِۖ وَلَا تَيَمَّمُواْ ٱلۡخَبِيثَ مِنۡهُ تُنفِقُونَ وَلَسۡتُم بِـَٔاخِذِيهِ إِلَّآ أَن تُغۡمِضُواْ فِيهِۚ وَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ غَنِيٌّ حَمِيدٌ

Ya ku waxanda suka yi imani, ku ciyar daga daxaxan abin da kuka tsuwurwuta da kuma abin da muka fitar muku shi daga cikin qasa, kuma kar ku nufaci mummuna daga cikinsa ku ce daga gare shi ne za ku ciyar, alhalin ku ma kanku (idan an ba ku) ba za ku karve shi ba sai kun runtse idanu. Kuma ku sani cewa lalle Allah Mawadaci ne, Sha-yabo



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 270

وَمَآ أَنفَقۡتُم مِّن نَّفَقَةٍ أَوۡ نَذَرۡتُم مِّن نَّذۡرٖ فَإِنَّ ٱللَّهَ يَعۡلَمُهُۥۗ وَمَا لِلظَّـٰلِمِينَ مِنۡ أَنصَارٍ

Kuma abin da kuka ciyar na abin ciyarwa ko kuka yi alwashi na bakance, to lalle Allah Yana sane da shi. Kuma azzalumai ba su da waxansu mataimaka



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 271

إِن تُبۡدُواْ ٱلصَّدَقَٰتِ فَنِعِمَّا هِيَۖ وَإِن تُخۡفُوهَا وَتُؤۡتُوهَا ٱلۡفُقَرَآءَ فَهُوَ خَيۡرٞ لَّكُمۡۚ وَيُكَفِّرُ عَنكُم مِّن سَيِّـَٔاتِكُمۡۗ وَٱللَّهُ بِمَا تَعۡمَلُونَ خَبِيرٞ

In da za ku bayyanar da sadakoki a fili, to madalla da hakan, kuma idan kuka voye sadaqar, kuma kuka ba da ita ga talakawa, to hakan shi ya fi alheri a gare ku, kuma zai kankare muku kurakurenku, kuma Allah Masanin abin da kuke aikatawa ne



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 272

۞لَّيۡسَ عَلَيۡكَ هُدَىٰهُمۡ وَلَٰكِنَّ ٱللَّهَ يَهۡدِي مَن يَشَآءُۗ وَمَا تُنفِقُواْ مِنۡ خَيۡرٖ فَلِأَنفُسِكُمۡۚ وَمَا تُنفِقُونَ إِلَّا ٱبۡتِغَآءَ وَجۡهِ ٱللَّهِۚ وَمَا تُنفِقُواْ مِنۡ خَيۡرٖ يُوَفَّ إِلَيۡكُمۡ وَأَنتُمۡ لَا تُظۡلَمُونَ

Shiryar da su ba a kanka yake ba, sai dai Allah ne Yake shiryar da wanda Ya ga dama, kuma duk abin da kuka ciyar na alheri, to domin kawunanku ne, kuma ba za ku ciyar ba sai don neman yardar Allah; kuma duk abin da kuka ciyar na alheri, za a cika muku ladansa, alhali kuma ba za a zalunce ku ba



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 273

لِلۡفُقَرَآءِ ٱلَّذِينَ أُحۡصِرُواْ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ لَا يَسۡتَطِيعُونَ ضَرۡبٗا فِي ٱلۡأَرۡضِ يَحۡسَبُهُمُ ٱلۡجَاهِلُ أَغۡنِيَآءَ مِنَ ٱلتَّعَفُّفِ تَعۡرِفُهُم بِسِيمَٰهُمۡ لَا يَسۡـَٔلُونَ ٱلنَّاسَ إِلۡحَافٗاۗ وَمَا تُنفِقُواْ مِنۡ خَيۡرٖ فَإِنَّ ٱللَّهَ بِهِۦ عَلِيمٌ

Ga mabuqata waxanda aka tsare saboda Allah, ba su da ikon yawatawa a bayan qasa, har wanda ya jahilci halinsu yana zato su mawadata ne saboda kame kai; za ka gane su ne da alamominsu, ba sa naciyar roqar mutane, kuma duk abin da kuka ciyar na alheri, to Allah Yana sane da shi



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 274

ٱلَّذِينَ يُنفِقُونَ أَمۡوَٰلَهُم بِٱلَّيۡلِ وَٱلنَّهَارِ سِرّٗا وَعَلَانِيَةٗ فَلَهُمۡ أَجۡرُهُمۡ عِندَ رَبِّهِمۡ وَلَا خَوۡفٌ عَلَيۡهِمۡ وَلَا هُمۡ يَحۡزَنُونَ

Waxanda suke ciyar da dukiyoyinsu dare da rana a voye da kuma a sarari, to suna da ladansu a wajen Ubangijinsu, kuma babu tsoro a tare da su, kuma ba za su yi baqin ciki ba



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 276

يَمۡحَقُ ٱللَّهُ ٱلرِّبَوٰاْ وَيُرۡبِي ٱلصَّدَقَٰتِۗ وَٱللَّهُ لَا يُحِبُّ كُلَّ كَفَّارٍ أَثِيمٍ

Allah Yana shafe albarkar riba, Yana kuma havaka sadaqa. Kuma Allah ba Ya son dukkan wani mai yawan kafircewa, mai yawan savo



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 280

وَإِن كَانَ ذُو عُسۡرَةٖ فَنَظِرَةٌ إِلَىٰ مَيۡسَرَةٖۚ وَأَن تَصَدَّقُواْ خَيۡرٞ لَّكُمۡ إِن كُنتُمۡ تَعۡلَمُونَ

Kuma idan (mai cin bashin) ya kasance ma’abocin matsi, to sai a yi masa jinkiri zuwa lokacin da zai sami sauqi, kuma in da za ku yi sadaqa shi ya fi alheri a gare ku in kun kasance kuna da masaniya



Surah: Suratu Ali-Imran

Ayah : 92

لَن تَنَالُواْ ٱلۡبِرَّ حَتَّىٰ تُنفِقُواْ مِمَّا تُحِبُّونَۚ وَمَا تُنفِقُواْ مِن شَيۡءٖ فَإِنَّ ٱللَّهَ بِهِۦ عَلِيمٞ

Ba za ku tava dacewa da aiki na alheri ba har sai kun ciyar daga abin da kuke so, kuma abin da duk kuka ciyar kowane iri ne, to lalle Allah Yana sane da shi



Surah: Suratun Nisa’i

Ayah : 92

وَمَا كَانَ لِمُؤۡمِنٍ أَن يَقۡتُلَ مُؤۡمِنًا إِلَّا خَطَـٔٗاۚ وَمَن قَتَلَ مُؤۡمِنًا خَطَـٔٗا فَتَحۡرِيرُ رَقَبَةٖ مُّؤۡمِنَةٖ وَدِيَةٞ مُّسَلَّمَةٌ إِلَىٰٓ أَهۡلِهِۦٓ إِلَّآ أَن يَصَّدَّقُواْۚ فَإِن كَانَ مِن قَوۡمٍ عَدُوّٖ لَّكُمۡ وَهُوَ مُؤۡمِنٞ فَتَحۡرِيرُ رَقَبَةٖ مُّؤۡمِنَةٖۖ وَإِن كَانَ مِن قَوۡمِۭ بَيۡنَكُمۡ وَبَيۡنَهُم مِّيثَٰقٞ فَدِيَةٞ مُّسَلَّمَةٌ إِلَىٰٓ أَهۡلِهِۦ وَتَحۡرِيرُ رَقَبَةٖ مُّؤۡمِنَةٖۖ فَمَن لَّمۡ يَجِدۡ فَصِيَامُ شَهۡرَيۡنِ مُتَتَابِعَيۡنِ تَوۡبَةٗ مِّنَ ٱللَّهِۗ وَكَانَ ٱللَّهُ عَلِيمًا حَكِيمٗا

Kuma bai dace ga mumini ya kashe wani mumini ba, sai bisa kuskure. Wanda ya kashe mumini bisa ga kuskure, to zai ‘yanta bawa ko baiwa mumina da kuma diyya wadda za a miqa wa iyalinsa, sai fa idan sun yafe. Amma idan wanda aka kashe yana cikin mutanen da suke maqiyanku, alhalin kuma shi mumini ne, to za ku ‘yanta bawa ko baiwa mumina; idan kuwa ya kasance yana cikin mutanen da kuke da yarjejeniyar zaman lafiya da su, to za a bayar da diyya wadda za a miqa wa iyalinsa, sannan za ku ‘yanta bawa ko baiwa mumina; wanda kuwa bai sami ikon haka ba, to sai ya yi azumin wata biyu a jere[1] don tuba zuwa ga Allah. Allah kuwa Ya kasance Mai yawan sani ne, Mai hikima


1- Watau sai dai idan akwai wani uzuri na rashin lafiya, ko na shari’a kamar shigowar Ramadana ko a ranar salla.


Surah: Suratun Nisa’i

Ayah : 114

۞لَّا خَيۡرَ فِي كَثِيرٖ مِّن نَّجۡوَىٰهُمۡ إِلَّا مَنۡ أَمَرَ بِصَدَقَةٍ أَوۡ مَعۡرُوفٍ أَوۡ إِصۡلَٰحِۭ بَيۡنَ ٱلنَّاسِۚ وَمَن يَفۡعَلۡ ذَٰلِكَ ٱبۡتِغَآءَ مَرۡضَاتِ ٱللَّهِ فَسَوۡفَ نُؤۡتِيهِ أَجۡرًا عَظِيمٗا

Babu wani alheri a cikin yawancin ganawarsu, sai fa wanda ya yi umarni da yin sadaka, ko wani aiki nagari ko kuma sulhuntawa tsakanin mutane. Wanda ya aikata haka don neman yardar Allah, to za Mu ba shi lada mai girma



Surah: Suratut Tauba

Ayah : 75

۞وَمِنۡهُم مَّنۡ عَٰهَدَ ٱللَّهَ لَئِنۡ ءَاتَىٰنَا مِن فَضۡلِهِۦ لَنَصَّدَّقَنَّ وَلَنَكُونَنَّ مِنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ

Daga cikinsu kuma akwai waxanda suka yi wa Allah alqawarin cewa: “Idan Ya arzuta mu daga falalarsa, to lalle tabbas za mu riqa ba da sadaka, kuma lalle tabbas za mu zama cikin mutane salihai.”



Surah: Suratut Tauba

Ayah : 76

فَلَمَّآ ءَاتَىٰهُم مِّن فَضۡلِهِۦ بَخِلُواْ بِهِۦ وَتَوَلَّواْ وَّهُم مُّعۡرِضُونَ

To lokacin da Ya arzuta su xin sai suka yi rowa da ita (sadakar) suka kuma ba da baya suna masu bijirewa



Surah: Suratut Tauba

Ayah : 77

فَأَعۡقَبَهُمۡ نِفَاقٗا فِي قُلُوبِهِمۡ إِلَىٰ يَوۡمِ يَلۡقَوۡنَهُۥ بِمَآ أَخۡلَفُواْ ٱللَّهَ مَا وَعَدُوهُ وَبِمَا كَانُواْ يَكۡذِبُونَ

Sai Ya gadar musu da munafunci a cikin zukatansu har zuwa ranar da za su gamu da Shi, saboda sava wa alqawarin da suka yi wa Allah da kuma qaryatawar da suka zamanto suna yi



Surah: Suratut Tauba

Ayah : 103

خُذۡ مِنۡ أَمۡوَٰلِهِمۡ صَدَقَةٗ تُطَهِّرُهُمۡ وَتُزَكِّيهِم بِهَا وَصَلِّ عَلَيۡهِمۡۖ إِنَّ صَلَوٰتَكَ سَكَنٞ لَّهُمۡۗ وَٱللَّهُ سَمِيعٌ عَلِيمٌ

Ka karvi sadaka daga dukiyoyinsu da za ka tsarkake su kuma ka gyara musu halaye da ita, ka kuma yi musu addu’a. Lalle addu’arka nutsuwa ce a gare su. Allah kuwa Mai ji ne, Masani



Surah: Suratut Tauba

Ayah : 104

أَلَمۡ يَعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ هُوَ يَقۡبَلُ ٱلتَّوۡبَةَ عَنۡ عِبَادِهِۦ وَيَأۡخُذُ ٱلصَّدَقَٰتِ وَأَنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلتَّوَّابُ ٱلرَّحِيمُ

Shin yanzu ba su sani ba ne cewa Allah Shi Yake karvar tuba daga bayinsa Yake kuma karvar sadakoki, kuma lalle Shi ne Mai yawan karvar tuba, Mai jin qai?



Surah: Suratur Ra’ad

Ayah : 22

وَٱلَّذِينَ صَبَرُواْ ٱبۡتِغَآءَ وَجۡهِ رَبِّهِمۡ وَأَقَامُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَأَنفَقُواْ مِمَّا رَزَقۡنَٰهُمۡ سِرّٗا وَعَلَانِيَةٗ وَيَدۡرَءُونَ بِٱلۡحَسَنَةِ ٱلسَّيِّئَةَ أُوْلَـٰٓئِكَ لَهُمۡ عُقۡبَى ٱلدَّارِ

Waxanda kuma suka yi haquri don neman yardar Ubangijnsu, suka kuma tsai da salla, kuma suka ciyar daga abin da Muka arzuta su da shi a voye da sarari, suke kuma ingije mummunan aiki da kyakkyawa, waxannan suna da (kyakkyawar) makoma ta gidan (Aljanna)



Surah: Suratu Ibrahim

Ayah : 31

قُل لِّعِبَادِيَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ يُقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَيُنفِقُواْ مِمَّا رَزَقۡنَٰهُمۡ سِرّٗا وَعَلَانِيَةٗ مِّن قَبۡلِ أَن يَأۡتِيَ يَوۡمٞ لَّا بَيۡعٞ فِيهِ وَلَا خِلَٰلٌ

Ka ce da bayina waxanda suka yi imani, su tsayar da salla kuma su ciyar daga abin da Muka arzuta su da shi, a voye da sarari tun kafin zuwan ranar da babu ciniki a cikinta, kuma babu abota



Surah: Suratul Hajji

Ayah : 28

لِّيَشۡهَدُواْ مَنَٰفِعَ لَهُمۡ وَيَذۡكُرُواْ ٱسۡمَ ٱللَّهِ فِيٓ أَيَّامٖ مَّعۡلُومَٰتٍ عَلَىٰ مَا رَزَقَهُم مِّنۢ بَهِيمَةِ ٱلۡأَنۡعَٰمِۖ فَكُلُواْ مِنۡهَا وَأَطۡعِمُواْ ٱلۡبَآئِسَ ٱلۡفَقِيرَ

Don su halarci amfanin da za su samu, kuma su ambaci sunan Allah cikin kwanaki sanannu a kan abin da Ya arzuta su da shi na dabbobin ni’ima (watau raquma da tumaki da awakai da shanu); sai ku ci daga gare su kuma ku ciyar da galavaitaccen matalauci



Surah: Suratul Hajji

Ayah : 36

وَٱلۡبُدۡنَ جَعَلۡنَٰهَا لَكُم مِّن شَعَـٰٓئِرِ ٱللَّهِ لَكُمۡ فِيهَا خَيۡرٞۖ فَٱذۡكُرُواْ ٱسۡمَ ٱللَّهِ عَلَيۡهَا صَوَآفَّۖ فَإِذَا وَجَبَتۡ جُنُوبُهَا فَكُلُواْ مِنۡهَا وَأَطۡعِمُواْ ٱلۡقَانِعَ وَٱلۡمُعۡتَرَّۚ كَذَٰلِكَ سَخَّرۡنَٰهَا لَكُمۡ لَعَلَّكُمۡ تَشۡكُرُونَ

(Raquma) kuma masu qiba Mun sanya muku su alamomi ne na bautar Allah; kuna da amfani game da su (na rayuwarku). To sai ku ambaci sunan Allah a kansu suna tsaye a kan qafa uku (lokacin soke su). To idan ransu ya fita bayan sun faxi, sai ku ci daga gare su kuma ku ciyar da mai wadatar zuci da kuma mai bara. Kamar haka Muka hore muku su don ku yi godiya



Surah: Suratur Rum

Ayah : 39

وَمَآ ءَاتَيۡتُم مِّن رِّبٗا لِّيَرۡبُوَاْ فِيٓ أَمۡوَٰلِ ٱلنَّاسِ فَلَا يَرۡبُواْ عِندَ ٱللَّهِۖ وَمَآ ءَاتَيۡتُم مِّن زَكَوٰةٖ تُرِيدُونَ وَجۡهَ ٱللَّهِ فَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡمُضۡعِفُونَ

Kuma abin da kuka bayar na riba don ya qaru a cikin dukiyoyin mutane, to ba ya qaruwa a wurin Allah[1]; abin kuma da kuka bayar na zakka kuna masu nufin Fuskar Allah, to waxannan su ne masu ninninka (ladansu)


1- Da yawa daga cikin malamai sun fassara wannan gavar da cewa, ana nufin wanda zai bayar da kyauta yana nufin a mayar masa da fiye da abin da ya bayar, to ba shi da lada a wurin Allah.


Surah: Suratu Saba’i

Ayah : 39

قُلۡ إِنَّ رَبِّي يَبۡسُطُ ٱلرِّزۡقَ لِمَن يَشَآءُ مِنۡ عِبَادِهِۦ وَيَقۡدِرُ لَهُۥۚ وَمَآ أَنفَقۡتُم مِّن شَيۡءٖ فَهُوَ يُخۡلِفُهُۥۖ وَهُوَ خَيۡرُ ٱلرَّـٰزِقِينَ

Ka ce: “Lalle Ubangijna Yana shimfixa arziki ga wanda ya ga dama cikin bayinsa, Yana kuma quntata masa. Kuma duk abin da kuka ciyar (don Allah), to Shi ne zai ba ku madadinsa, Shi ne kuwa Fiyayyen masu arzutawa.”