Surah: Suratul A’araf

Ayah : 8

وَٱلۡوَزۡنُ يَوۡمَئِذٍ ٱلۡحَقُّۚ فَمَن ثَقُلَتۡ مَوَٰزِينُهُۥ فَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡمُفۡلِحُونَ

Awo kuma a wannan ranar gaskiya ne. Don haka duk wanda ma’aunansa suka yi nauyi, to waxannan su ne masu rabauta



Surah: Suratul A’araf

Ayah : 9

وَمَنۡ خَفَّتۡ مَوَٰزِينُهُۥ فَأُوْلَـٰٓئِكَ ٱلَّذِينَ خَسِرُوٓاْ أَنفُسَهُم بِمَا كَانُواْ بِـَٔايَٰتِنَا يَظۡلِمُونَ

Wanda kuwa ma’aunansa suka yi sakayau, to waxannan su ne waxanda suka yi hasarar kawunansu, saboda abin da suka kasance suna yi na zalunci da ayoyinmu



Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 102

فَمَن ثَقُلَتۡ مَوَٰزِينُهُۥ فَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡمُفۡلِحُونَ

To waxanda ma’aunansu suka yi nauyi waxannan su ne masu babban rabo



Surah: Suratul Mu’uminun

Ayah : 103

وَمَنۡ خَفَّتۡ مَوَٰزِينُهُۥ فَأُوْلَـٰٓئِكَ ٱلَّذِينَ خَسِرُوٓاْ أَنفُسَهُمۡ فِي جَهَنَّمَ خَٰلِدُونَ

Waxanda kuwa ma’aunansu suka yi sakayau waxannan su ne waxanda suka yi asarar kawunansu, suna masu dawwama a cikin (wutar) Jahannama



Surah: Suratul Qari’a

Ayah : 6

فَأَمَّا مَن ثَقُلَتۡ مَوَٰزِينُهُۥ

To amma wanda ma’aunan ayyukansa suka yi nauyi



Surah: Suratul Qari’a

Ayah : 7

فَهُوَ فِي عِيشَةٖ رَّاضِيَةٖ

To shi kam yana cikin rayuwa mai gamsarwa



Surah: Suratul Qari’a

Ayah : 8

وَأَمَّا مَنۡ خَفَّتۡ مَوَٰزِينُهُۥ

Amma kuma duk wanda ma’aunan ayyukansa suka yi shafal



Surah: Suratul Qari’a

Ayah : 9

فَأُمُّهُۥ هَاوِيَةٞ

To shi makomarsa (wutar) Hawiya ce