Surah: Suratul Baqara

Ayah : 30

وَإِذۡ قَالَ رَبُّكَ لِلۡمَلَـٰٓئِكَةِ إِنِّي جَاعِلٞ فِي ٱلۡأَرۡضِ خَلِيفَةٗۖ قَالُوٓاْ أَتَجۡعَلُ فِيهَا مَن يُفۡسِدُ فِيهَا وَيَسۡفِكُ ٱلدِّمَآءَ وَنَحۡنُ نُسَبِّحُ بِحَمۡدِكَ وَنُقَدِّسُ لَكَۖ قَالَ إِنِّيٓ أَعۡلَمُ مَا لَا تَعۡلَمُونَ

Kuma ka tuna sa’adda Ubangijinka Ya ce da mala’iku: “Lalle ni zan sanya wani halifa[1] a bayan qasa.” Suka ce: “Yanzu za Ka sanya mata wanda zai yi varna a cikinta kuma ya zubar da jini, alhali ga mu muna tasbihi tare da gode Maka, kuma muna tsarkake Ka?” (Allah) Ya ce: “Ni fa tabbas Na san abin da ku ba ku sani ba.”


1- Halifa, shi ne Annabi Adamu () da zuriyarsa, waxanda za su riqa maye gurbin juna a bayan qasa.


Surah: Suratul Baqara

Ayah : 31

وَعَلَّمَ ءَادَمَ ٱلۡأَسۡمَآءَ كُلَّهَا ثُمَّ عَرَضَهُمۡ عَلَى ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةِ فَقَالَ أَنۢبِـُٔونِي بِأَسۡمَآءِ هَـٰٓؤُلَآءِ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ

Kuma sai (Allah) Ya koya wa Adamu dukkan sunaye (na abubuwa) sannan Ya kawo su gaban mala’iku, sai Ya ce: “Ku faxa min sunayen waxannan abubuwan in kun zamanto masu gaskiya.”



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 32

قَالُواْ سُبۡحَٰنَكَ لَا عِلۡمَ لَنَآ إِلَّا مَا عَلَّمۡتَنَآۖ إِنَّكَ أَنتَ ٱلۡعَلِيمُ ٱلۡحَكِيمُ

Sai suka ce: “Tsarki ya tabbata a gare Ka, ba mu da wani ilimi sai wanda Ka sanar da mu. Lalle Kai ne cikakken Masani, Mai hikima.”



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 33

قَالَ يَـٰٓـَٔادَمُ أَنۢبِئۡهُم بِأَسۡمَآئِهِمۡۖ فَلَمَّآ أَنۢبَأَهُم بِأَسۡمَآئِهِمۡ قَالَ أَلَمۡ أَقُل لَّكُمۡ إِنِّيٓ أَعۡلَمُ غَيۡبَ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَأَعۡلَمُ مَا تُبۡدُونَ وَمَا كُنتُمۡ تَكۡتُمُونَ

Ya ce: “Ya Adamu faxa musu sunayensu.” Yayin da ya faxa musu sunayensu, sai (Allah) Ya ce: “Ba Na faxa muku cewa, lalle Ni ne Nake sane da gaibin sammai da qasa ba, kuma Nake sane da abin da kuke bayyanawa da kuma abin da kuke voyewa ba?”



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 34

وَإِذۡ قُلۡنَا لِلۡمَلَـٰٓئِكَةِ ٱسۡجُدُواْ لِأٓدَمَ فَسَجَدُوٓاْ إِلَّآ إِبۡلِيسَ أَبَىٰ وَٱسۡتَكۡبَرَ وَكَانَ مِنَ ٱلۡكَٰفِرِينَ

Kuma ka tuna lokacin da Muka ce wa mala’iku: “Ku yi sujjada ga Adamu.” Sai duk suka yi sujjada[1], in ban da Iblis, sai shi ya qi, ya kuma yi girman kai, kuma ya tabbata cikin kafirai


1- Mala’iku sun yi wa Adamu () sujjada ne don biyayya ga umarnin Allah. Ba ya halatta a Musulunci wani ya yi wa wani sujjada ba Allah ba.


Surah: Suratul Baqara

Ayah : 97

قُلۡ مَن كَانَ عَدُوّٗا لِّـجِبۡرِيلَ فَإِنَّهُۥ نَزَّلَهُۥ عَلَىٰ قَلۡبِكَ بِإِذۡنِ ٱللَّهِ مُصَدِّقٗا لِّمَا بَيۡنَ يَدَيۡهِ وَهُدٗى وَبُشۡرَىٰ لِلۡمُؤۡمِنِينَ

Ka ce: “Duk wanda ya kasance maqiyi ne ga (Mala’ika) Jibrilu[1], to lalle shi ne ya saukar da shi (Alqur’ani) a kan zuciyarka da izinin Allah yana mai gaskata abin da ya gabace shi (na littattafai), kuma shiriya ne da bushara ga muminai.”


1- Yahudawa sun faxa wa Annabi cewa, Mala'ika Jibrilu maqiyinsu ne, wai domin shi ne yake saukowa da yaqi da kashe-kashe da azaba.


Surah: Suratul Baqara

Ayah : 98

مَن كَانَ عَدُوّٗا لِّلَّهِ وَمَلَـٰٓئِكَتِهِۦ وَرُسُلِهِۦ وَجِبۡرِيلَ وَمِيكَىٰلَ فَإِنَّ ٱللَّهَ عَدُوّٞ لِّلۡكَٰفِرِينَ

Duk wanda ya kasance maqiyi ne ga Allah da mala’ikunsa da manzanninsa da Jibrilu da Mika’ilu, to lalle Allah maqiyin kafirai ne



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 102

وَٱتَّبَعُواْ مَا تَتۡلُواْ ٱلشَّيَٰطِينُ عَلَىٰ مُلۡكِ سُلَيۡمَٰنَۖ وَمَا كَفَرَ سُلَيۡمَٰنُ وَلَٰكِنَّ ٱلشَّيَٰطِينَ كَفَرُواْ يُعَلِّمُونَ ٱلنَّاسَ ٱلسِّحۡرَ وَمَآ أُنزِلَ عَلَى ٱلۡمَلَكَيۡنِ بِبَابِلَ هَٰرُوتَ وَمَٰرُوتَۚ وَمَا يُعَلِّمَانِ مِنۡ أَحَدٍ حَتَّىٰ يَقُولَآ إِنَّمَا نَحۡنُ فِتۡنَةٞ فَلَا تَكۡفُرۡۖ فَيَتَعَلَّمُونَ مِنۡهُمَا مَا يُفَرِّقُونَ بِهِۦ بَيۡنَ ٱلۡمَرۡءِ وَزَوۡجِهِۦۚ وَمَا هُم بِضَآرِّينَ بِهِۦ مِنۡ أَحَدٍ إِلَّا بِإِذۡنِ ٱللَّهِۚ وَيَتَعَلَّمُونَ مَا يَضُرُّهُمۡ وَلَا يَنفَعُهُمۡۚ وَلَقَدۡ عَلِمُواْ لَمَنِ ٱشۡتَرَىٰهُ مَا لَهُۥ فِي ٱلۡأٓخِرَةِ مِنۡ خَلَٰقٖۚ وَلَبِئۡسَ مَا شَرَوۡاْ بِهِۦٓ أَنفُسَهُمۡۚ لَوۡ كَانُواْ يَعۡلَمُونَ

Sai suka bi abin da shexanu suke karantawa a (zamanin) mulkin Sulaimanu; kuma Sulaimanu bai kafirta ba, sai dai shexanun su ne suka kafirta; suna koya wa mutane tsafi da abin da aka saukar wa mala’iku biyu, Haruta da Maruta, a garin Babila. Kuma ba sa koya wa wani (tsafin) har sai sun faxa masa cewa: “Mu fa jarraba ce, don haka kada ka kafirta”. Sai (mutane) suka riqa koyo daga wajensu su biyu abin da suke raba tsakanin miji da matarsa da shi. Kuma ba za su iya cutar da wani da shi ba sai da izinin Allah. Sai su koyi abin da zai cutar da su kuma ba zai amfane su ba. Kuma haqiqa sun san cewa, tabbas duk wanda ya zavi (sihiri) ba shi da wani rabo a lahira. Kuma lalle tir da abin da suka sayar da kawunansu da shi, da a ce sun san (haqiqanin makomarsu)



Surah: Suratu Ali-Imran

Ayah : 80

وَلَا يَأۡمُرَكُمۡ أَن تَتَّخِذُواْ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةَ وَٱلنَّبِيِّـۧنَ أَرۡبَابًاۚ أَيَأۡمُرُكُم بِٱلۡكُفۡرِ بَعۡدَ إِذۡ أَنتُم مُّسۡلِمُونَ

Kuma ba zai umarce ku da ku riqi mala’iku ko annabawa a matsayin iyayengiji ba; yanzu zai umarce ku da kafirci ne bayan kuna Musulmi?



Surah: Suratu Ali-Imran

Ayah : 124

إِذۡ تَقُولُ لِلۡمُؤۡمِنِينَ أَلَن يَكۡفِيَكُمۡ أَن يُمِدَّكُمۡ رَبُّكُم بِثَلَٰثَةِ ءَالَٰفٖ مِّنَ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةِ مُنزَلِينَ

Ka tuna lokacin da kake ce wa muminai: “Shin bai ishe ku ba idan Ubangijinku Ya kawo muku agajin mala’iku dubu uku waxanda za a saukar da su (daga sama)?”



Surah: Suratu Ali-Imran

Ayah : 125

بَلَىٰٓۚ إِن تَصۡبِرُواْ وَتَتَّقُواْ وَيَأۡتُوكُم مِّن فَوۡرِهِمۡ هَٰذَا يُمۡدِدۡكُمۡ رَبُّكُم بِخَمۡسَةِ ءَالَٰفٖ مِّنَ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةِ مُسَوِّمِينَ

Haka ne, idan har za ku yi haquri, kuma ku yi taqawa, kuma (kafirai) suka auko muku cikin gaggawa a wannan lokacin, to Ubangijinku zai qaro muku agaji da mala’iku dubu biyar masu alamomi



Surah: Suratun Nisa’i

Ayah : 97

إِنَّ ٱلَّذِينَ تَوَفَّىٰهُمُ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ ظَالِمِيٓ أَنفُسِهِمۡ قَالُواْ فِيمَ كُنتُمۡۖ قَالُواْ كُنَّا مُسۡتَضۡعَفِينَ فِي ٱلۡأَرۡضِۚ قَالُوٓاْ أَلَمۡ تَكُنۡ أَرۡضُ ٱللَّهِ وَٰسِعَةٗ فَتُهَاجِرُواْ فِيهَاۚ فَأُوْلَـٰٓئِكَ مَأۡوَىٰهُمۡ جَهَنَّمُۖ وَسَآءَتۡ مَصِيرًا

Lalle waxanda mala’iku suke karvar rayukansu suna masu zaluntar kawunansu[1], (mala’ikun) za su ce (da su): “Cikin wane hali kuka kasance?” Sai su ce: “Mu mun kasance masu rauni a bayan qasa.” Sai su ce: “Ashe qasar Allah ba mai yalwa ba ce, ta yadda za ku sami damar yin hijira a cikinta?” To waxannan, makomarsu ita ce wutar Jahannama, kuma wannan makoma ta munana


1- Watau sun qi yin hijira zuwa cikin ‘yan’uwansu Musulmi, sun ci gaba da zama a qasar kafirci, tare da cewa suna da ikon yin hijirar.


Surah: Suratul An’am

Ayah : 93

وَمَنۡ أَظۡلَمُ مِمَّنِ ٱفۡتَرَىٰ عَلَى ٱللَّهِ كَذِبًا أَوۡ قَالَ أُوحِيَ إِلَيَّ وَلَمۡ يُوحَ إِلَيۡهِ شَيۡءٞ وَمَن قَالَ سَأُنزِلُ مِثۡلَ مَآ أَنزَلَ ٱللَّهُۗ وَلَوۡ تَرَىٰٓ إِذِ ٱلظَّـٰلِمُونَ فِي غَمَرَٰتِ ٱلۡمَوۡتِ وَٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ بَاسِطُوٓاْ أَيۡدِيهِمۡ أَخۡرِجُوٓاْ أَنفُسَكُمُۖ ٱلۡيَوۡمَ تُجۡزَوۡنَ عَذَابَ ٱلۡهُونِ بِمَا كُنتُمۡ تَقُولُونَ عَلَى ٱللَّهِ غَيۡرَ ٱلۡحَقِّ وَكُنتُمۡ عَنۡ ءَايَٰتِهِۦ تَسۡتَكۡبِرُونَ

Kuma wane ne ya fi zalunci kamar wanda ya qagi qarya ya jingina wa Allah, ko kuma ya ce: “An yiwo mini wahayi,” alhalin kuma ba a yi masa wahayin komai ba, da kuma wanda ya ce: “Zan saukar da irin abin da Allah Ya saukar?” Kuma da za ka ga lokacin da kafirai suke cikin magagin mutuwa, mala’iku kuma suna miqa hannayensu suna cewa: “Ku fito da rayukanku (da kanku), a yau ne za a saka muku da azabar wulaqanci, saboda irin abin da kuke faxa game da Allah wanda ba gaskiya ba, kuma kun kasance kuna girman kai game da ayoyinsa.”



Surah: Suratul Anfal

Ayah : 9

إِذۡ تَسۡتَغِيثُونَ رَبَّكُمۡ فَٱسۡتَجَابَ لَكُمۡ أَنِّي مُمِدُّكُم بِأَلۡفٖ مِّنَ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةِ مُرۡدِفِينَ

Ku tuna lokacin da kuke neman taimakon Ubangijinku, sai Ya amsa muku cewa: “Ni zan kawo muku xauki na mala’iku dubu masu bibiyar juna.”



Surah: Suratul Anfal

Ayah : 12

إِذۡ يُوحِي رَبُّكَ إِلَى ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةِ أَنِّي مَعَكُمۡ فَثَبِّتُواْ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْۚ سَأُلۡقِي فِي قُلُوبِ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ ٱلرُّعۡبَ فَٱضۡرِبُواْ فَوۡقَ ٱلۡأَعۡنَاقِ وَٱضۡرِبُواْ مِنۡهُمۡ كُلَّ بَنَانٖ

(Ka kuma tuna) lokacin da Ubangijinka Yake wahayi zuwa ga mala’iku cewa: “Lalle Ni ina tare da ku, saboda haka ku qarfafa wa waxanda suka yi imani gwiwa. Da sannu zan jefa tsoro cikin zukatan waxanda suka kafirce, saboda haka ku doki wuyansu, kuma ku doki dukkanin gavovin hannaye da qafafu.”



Surah: Suratul Anfal

Ayah : 50

وَلَوۡ تَرَىٰٓ إِذۡ يَتَوَفَّى ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ يَضۡرِبُونَ وُجُوهَهُمۡ وَأَدۡبَٰرَهُمۡ وَذُوقُواْ عَذَابَ ٱلۡحَرِيقِ

Kuma da za ka ga lokacin da mala’iku suke xaukan ran waxanda suka kafirta, suna dukan fuskokinsu da kuma bayansu, suna kuma (cewa da su): “Ku xanxani azabar quna.”



Surah: Suratul Anfal

Ayah : 51

ذَٰلِكَ بِمَا قَدَّمَتۡ أَيۡدِيكُمۡ وَأَنَّ ٱللَّهَ لَيۡسَ بِظَلَّـٰمٖ لِّلۡعَبِيدِ

“Wannan (ya faru gare ku ne) saboda abin da hannayenku suka aikata, kuma lalle Allah ba Mai zaluntar bayi ne ba.”



Surah: Suratu Hud

Ayah : 69

وَلَقَدۡ جَآءَتۡ رُسُلُنَآ إِبۡرَٰهِيمَ بِٱلۡبُشۡرَىٰ قَالُواْ سَلَٰمٗاۖ قَالَ سَلَٰمٞۖ فَمَا لَبِثَ أَن جَآءَ بِعِجۡلٍ حَنِيذٖ

Haqiqa kuma mazanninmu sun zo wa Ibrahimu da albishir, suka ce: “Aminci (a gare ku)”, ya ce: “Aminci (a gare ku kuma).” To bai zauna ba sai da ya kawo musu soyayyen xan maraqi



Surah: Suratur Ra’ad

Ayah : 11

لَهُۥ مُعَقِّبَٰتٞ مِّنۢ بَيۡنِ يَدَيۡهِ وَمِنۡ خَلۡفِهِۦ يَحۡفَظُونَهُۥ مِنۡ أَمۡرِ ٱللَّهِۗ إِنَّ ٱللَّهَ لَا يُغَيِّرُ مَا بِقَوۡمٍ حَتَّىٰ يُغَيِّرُواْ مَا بِأَنفُسِهِمۡۗ وَإِذَآ أَرَادَ ٱللَّهُ بِقَوۡمٖ سُوٓءٗا فَلَا مَرَدَّ لَهُۥۚ وَمَا لَهُم مِّن دُونِهِۦ مِن وَالٍ

(Kowanensu) yana da (mala’iku) masu take masa baya a gabansa da kuma bayansa suna kiyaye shi da umarnin Allah. Lalle Allah ba Ya canja abin da mutane suke ciki har sai sun canja halayensu. Idan kuma Allah Ya yi nufin wata azaba ga mutane, to ba mai juyar da ita, ba su kuwa da wani mai jivintar su wanda ba Shi ba



Surah: Suratur Ra’ad

Ayah : 13

وَيُسَبِّحُ ٱلرَّعۡدُ بِحَمۡدِهِۦ وَٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ مِنۡ خِيفَتِهِۦ وَيُرۡسِلُ ٱلصَّوَٰعِقَ فَيُصِيبُ بِهَا مَن يَشَآءُ وَهُمۡ يُجَٰدِلُونَ فِي ٱللَّهِ وَهُوَ شَدِيدُ ٱلۡمِحَالِ

Tsawa tana tsarkake (Shi) tare da gode masa, mala’iku ma (suna tasbihi) saboda tsoron Sa, Yana kuma aiko da tsawawwaki sai Ya sami wanda Ya ga dama da su, kuma su (kafirai) ga su suna jayayya game da (sha’anin) Allah. Shi kuwa Mai tsananin qarfi ne



Surah: Suratur Ra’ad

Ayah : 23

جَنَّـٰتُ عَدۡنٖ يَدۡخُلُونَهَا وَمَن صَلَحَ مِنۡ ءَابَآئِهِمۡ وَأَزۡوَٰجِهِمۡ وَذُرِّيَّـٰتِهِمۡۖ وَٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ يَدۡخُلُونَ عَلَيۡهِم مِّن كُلِّ بَابٖ

Gidajen Aljanna na dawwama, za su shiga su da waxanda suka kyautata (aiki) daga iyayensu da matansu da kuma zuriyarsu; mala’iku kuma za su riqa shigowa wurinsu ta kowace qofa



Surah: Suratur Ra’ad

Ayah : 24

سَلَٰمٌ عَلَيۡكُم بِمَا صَبَرۡتُمۡۚ فَنِعۡمَ عُقۡبَى ٱلدَّارِ

(Suna ce musu): “Aminci ya tabbata a gare ku saboda haqurin da kuka yi. To madalla da gida na qarshe (watau Aljanna)”



Surah: Suratul Hijr

Ayah : 7

لَّوۡمَا تَأۡتِينَا بِٱلۡمَلَـٰٓئِكَةِ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّـٰدِقِينَ

“Me zai hana ka zo mana da mala’iku idan kana daga cikin masu gaskiya?”



Surah: Suratul Hijr

Ayah : 8

مَا نُنَزِّلُ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةَ إِلَّا بِٱلۡحَقِّ وَمَا كَانُوٓاْ إِذٗا مُّنظَرِينَ

(Allah ya ce): “Ba ma saukar da mala’iku sai da gaskiya[1]; inda kuwa haka ya faru, to ba za a saurara musu ba.”


1- Watau sai idan lokacin da za a hallaka su ya zo.


Surah: Suratul Hijr

Ayah : 28

وَإِذۡ قَالَ رَبُّكَ لِلۡمَلَـٰٓئِكَةِ إِنِّي خَٰلِقُۢ بَشَرٗا مِّن صَلۡصَٰلٖ مِّنۡ حَمَإٖ مَّسۡنُونٖ

Kuma (ka tuna) lokacin da Ubangijinka ya ce da mala’iku: “Lalle Ni zan halicci mutum daga busasshen tavo mai amo na wani yumvu mai wari



Surah: Suratul Hijr

Ayah : 29

فَإِذَا سَوَّيۡتُهُۥ وَنَفَخۡتُ فِيهِ مِن رُّوحِي فَقَعُواْ لَهُۥ سَٰجِدِينَ

“To idan Na daidaita shi Na kuma busa masa daga ruhina, to ku faxi kuna masu sujjada a gare shi.”



Surah: Suratul Hijr

Ayah : 30

فَسَجَدَ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةُ كُلُّهُمۡ أَجۡمَعُونَ

Sai mala’iku dukkaninsu suka yi sujjada gaba xaya



Surah: Suratul Hijr

Ayah : 51

وَنَبِّئۡهُمۡ عَن ضَيۡفِ إِبۡرَٰهِيمَ

Kuma ka ba su labari game da baqin Ibrahimu[1]


1- Su ne mala’ikun da suka ziyarci Ibrahim () a kan hanyarsu ta zuwa hallaka mutanen Annabi Luxu ().


Surah: Suratul Hijr

Ayah : 52

إِذۡ دَخَلُواْ عَلَيۡهِ فَقَالُواْ سَلَٰمٗا قَالَ إِنَّا مِنكُمۡ وَجِلُونَ

Lokacin da suka shiga wurinsa suka ce: “Muna yi maka sallama”, ya ce: “Lalle mu a tsorace muke da ku.”



Surah: Suratul Hijr

Ayah : 53

قَالُواْ لَا تَوۡجَلۡ إِنَّا نُبَشِّرُكَ بِغُلَٰمٍ عَلِيمٖ

Suka ce: “Kada ka ji tsoro, lalle mu muna yi maka albishir ne da (samun) yaro mai ilimi.”