Surah: Suratul Baqara

Ayah : 27

ٱلَّذِينَ يَنقُضُونَ عَهۡدَ ٱللَّهِ مِنۢ بَعۡدِ مِيثَٰقِهِۦ وَيَقۡطَعُونَ مَآ أَمَرَ ٱللَّهُ بِهِۦٓ أَن يُوصَلَ وَيُفۡسِدُونَ فِي ٱلۡأَرۡضِۚ أُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡخَٰسِرُونَ

Waxanda suke warware alqawarin Allah bayan qulla shi, kuma suke yanke abin da Allah Ya yi umarni a sadar da shi, kuma suke varna a bayan qasa. Waxannan su ne cikakkun hasararru



Surah: Suratu Ali-Imran

Ayah : 77

إِنَّ ٱلَّذِينَ يَشۡتَرُونَ بِعَهۡدِ ٱللَّهِ وَأَيۡمَٰنِهِمۡ ثَمَنٗا قَلِيلًا أُوْلَـٰٓئِكَ لَا خَلَٰقَ لَهُمۡ فِي ٱلۡأٓخِرَةِ وَلَا يُكَلِّمُهُمُ ٱللَّهُ وَلَا يَنظُرُ إِلَيۡهِمۡ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ وَلَا يُزَكِّيهِمۡ وَلَهُمۡ عَذَابٌ أَلِيمٞ

Lalle waxanda suke musanya alqawarin Allah da rantse-rantsensu da wani xan farashi qanqani, waxannan ba su da wani rabo a lahira, kuma Allah ba zai yi musu magana ba, kuma ba zai dube su (duba na rahama) ba a ranar alqiyama, kuma ba zai tsarkake su ba, kuma suna da azaba mai raxaxi



Surah: Suratul Anfal

Ayah : 55

إِنَّ شَرَّ ٱلدَّوَآبِّ عِندَ ٱللَّهِ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ فَهُمۡ لَا يُؤۡمِنُونَ

Lalle mafi sharrin masu tafiya a bayan qasa a wurin Allah (su ne) waxanda suka kafirta, don haka kuma su ba sa yin imani



Surah: Suratul Anfal

Ayah : 56

ٱلَّذِينَ عَٰهَدتَّ مِنۡهُمۡ ثُمَّ يَنقُضُونَ عَهۡدَهُمۡ فِي كُلِّ مَرَّةٖ وَهُمۡ لَا يَتَّقُونَ

Waxanda idan ka yi alqawari da su sai su warware alqawarinsu ko da yaushe, ba sa kuma kiyaye dokokin Allah (dangane da alqawari)



Surah: Suratul Anfal

Ayah : 57

فَإِمَّا تَثۡقَفَنَّهُمۡ فِي ٱلۡحَرۡبِ فَشَرِّدۡ بِهِم مَّنۡ خَلۡفَهُمۡ لَعَلَّهُمۡ يَذَّكَّرُونَ

Sannan idan ka haxu da su a wurin yaqi, to sai ka fatattaki na bayansu da su, don su (na bayan) sa wa’azantu



Surah: Suratul Anfal

Ayah : 58

وَإِمَّا تَخَافَنَّ مِن قَوۡمٍ خِيَانَةٗ فَٱنۢبِذۡ إِلَيۡهِمۡ عَلَىٰ سَوَآءٍۚ إِنَّ ٱللَّهَ لَا يُحِبُّ ٱلۡخَآئِنِينَ

Kuma idan kana jin tsoron wani ha’inci daga wasu mutane (da ka yi sulhu da su), to sai ka jefar musu shi (sulhun) a bayyane (ba da ha’inci ba). Lalle Allah ba Ya son masu ha’inci



Surah: Suratut Tauba

Ayah : 3

وَأَذَٰنٞ مِّنَ ٱللَّهِ وَرَسُولِهِۦٓ إِلَى ٱلنَّاسِ يَوۡمَ ٱلۡحَجِّ ٱلۡأَكۡبَرِ أَنَّ ٱللَّهَ بَرِيٓءٞ مِّنَ ٱلۡمُشۡرِكِينَ وَرَسُولُهُۥۚ فَإِن تُبۡتُمۡ فَهُوَ خَيۡرٞ لَّكُمۡۖ وَإِن تَوَلَّيۡتُمۡ فَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّكُمۡ غَيۡرُ مُعۡجِزِي ٱللَّهِۗ وَبَشِّرِ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ بِعَذَابٍ أَلِيمٍ

Kuma sanarwa daga Allah da Manzonsa zuwa ga mutane ranar Babbar Salla cewa, lalle Allah da Manzonsa babu ruwansu da mushrikai[1]. Amma idan kuka tuba, to shi ya fi alheri a gare ku, idan kuma kuka ba da baya, to ku sani lalle ku fa ba za ku gagari Allah ba. Kuma ka yi albishir ga waxanda suka kafirta da azaba mai raxadi


1- A shekara ta tara bayan hijira, Annabi () ya aika Abubakar da Aliyyu () su yi shela a Makka a ranar sallar layya cewa, kada wani mushiriki ya sake zuwa hajji ko ya yi xawafi tsirara.


Surah: Suratur Ra’ad

Ayah : 25

وَٱلَّذِينَ يَنقُضُونَ عَهۡدَ ٱللَّهِ مِنۢ بَعۡدِ مِيثَٰقِهِۦ وَيَقۡطَعُونَ مَآ أَمَرَ ٱللَّهُ بِهِۦٓ أَن يُوصَلَ وَيُفۡسِدُونَ فِي ٱلۡأَرۡضِ أُوْلَـٰٓئِكَ لَهُمُ ٱللَّعۡنَةُ وَلَهُمۡ سُوٓءُ ٱلدَّارِ

Waxanda kuma suke warware alqawarin Allah bayan sun qulla shi, suke kuma yanke abin da Allah Ya yi umarni a sadar da shi, kuma suke varna a bayan qasa, waxannan la’ana ta tabbata a gare su kuma suna da (sakamakon) mummunan gida (shi ne Jahannama)



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 95

وَلَا تَشۡتَرُواْ بِعَهۡدِ ٱللَّهِ ثَمَنٗا قَلِيلًاۚ إِنَّمَا عِندَ ٱللَّهِ هُوَ خَيۡرٞ لَّكُمۡ إِن كُنتُمۡ تَعۡلَمُونَ

Kada kuma ku sayar da alqawarin Allah da xan kuxi qanqani. Lalle abin da yake wurin Allah shi ya fi muku alheri in kun kasance kun san (haka)