Surah: Suratun Nahl

Ayah : 58

وَإِذَا بُشِّرَ أَحَدُهُم بِٱلۡأُنثَىٰ ظَلَّ وَجۡهُهُۥ مُسۡوَدّٗا وَهُوَ كَظِيمٞ

Kuma idan aka yi wa xayansu albishir da (‘ya) mace sai fuskarsa ta yi baqi qirin yana cike da tsananin baqin ciki



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 17

وَإِذَا بُشِّرَ أَحَدُهُم بِمَا ضَرَبَ لِلرَّحۡمَٰنِ مَثَلٗا ظَلَّ وَجۡهُهُۥ مُسۡوَدّٗا وَهُوَ كَظِيمٌ

Idan kuma aka yi wa xayansu albishir da abin da ya buga misali cewa na (Allah) Arrahmanu ne, sai fuskarsa ta yini a murtuke yana cike da baqin ciki



Surah: Suratut Takwir

Ayah : 8

وَإِذَا ٱلۡمَوۡءُۥدَةُ سُئِلَتۡ

Idan kuma yarinyar da aka binne da rai aka tambaye ta