Surah: Suratul Jasiya

Ayah : 6

تِلۡكَ ءَايَٰتُ ٱللَّهِ نَتۡلُوهَا عَلَيۡكَ بِٱلۡحَقِّۖ فَبِأَيِّ حَدِيثِۭ بَعۡدَ ٱللَّهِ وَءَايَٰتِهِۦ يُؤۡمِنُونَ

Waxannan su ne ayoyin Allah da Muke karanta maka su da gaskiya; to da wane zance ne za su yi imani bayan (zancen) Allah da ayoyinsa?



Surah: Suratul Jasiya

Ayah : 8

يَسۡمَعُ ءَايَٰتِ ٱللَّهِ تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِ ثُمَّ يُصِرُّ مُسۡتَكۡبِرٗا كَأَن لَّمۡ يَسۡمَعۡهَاۖ فَبَشِّرۡهُ بِعَذَابٍ أَلِيمٖ

Yana jin ana karanta masa ayoyin Allah, sai ya doge yana mai girman kai kamar bai ji su ba; to ka yi masa albishir da azaba mai raxaxi



Surah: Suratul Jasiya

Ayah : 9

وَإِذَا عَلِمَ مِنۡ ءَايَٰتِنَا شَيۡـًٔا ٱتَّخَذَهَا هُزُوًاۚ أُوْلَـٰٓئِكَ لَهُمۡ عَذَابٞ مُّهِينٞ

Idan kuma ya san wani abu daga ayoyinmu sai ya xauke su abin yi wa izgili. Waxannan suna da wata azaba mai wulaqantarwa



Surah: Suratul Jasiya

Ayah : 11

هَٰذَا هُدٗىۖ وَٱلَّذِينَ كَفَرُواْ بِـَٔايَٰتِ رَبِّهِمۡ لَهُمۡ عَذَابٞ مِّن رِّجۡزٍ أَلِيمٌ

Wannan (Alqur’ani) shiriya ne; waxanda kuwa suka kafirce da ayoyin Ubangijinsu, suna da (sakamakon) wata mummunar azaba mai raxaxi



Surah: Suratul Jasiya

Ayah : 20

هَٰذَا بَصَـٰٓئِرُ لِلنَّاسِ وَهُدٗى وَرَحۡمَةٞ لِّقَوۡمٖ يُوقِنُونَ

Wannan (Alqur’ani) izina ne ga mutane da shiriya da rahama ga mutanen da suke sakankancewa



Surah: Suratul Jasiya

Ayah : 25

وَإِذَا تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِمۡ ءَايَٰتُنَا بَيِّنَٰتٖ مَّا كَانَ حُجَّتَهُمۡ إِلَّآ أَن قَالُواْ ٱئۡتُواْ بِـَٔابَآئِنَآ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ

Idan kuma ana karanta musu ayoyinmu mabayyana, ba su da wata hujja sai kawai su ce: “Ku zo da iyayenmu idan kun kasance masu gaskiya.”



Surah: Suratul Ahqaf 

Ayah : 2

تَنزِيلُ ٱلۡكِتَٰبِ مِنَ ٱللَّهِ ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡحَكِيمِ

Saukar da Alqur’ani daga Allah ne Mabuwayi, Mai hikima



Surah: Suratul Ahqaf 

Ayah : 7

وَإِذَا تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِمۡ ءَايَٰتُنَا بَيِّنَٰتٖ قَالَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لِلۡحَقِّ لَمَّا جَآءَهُمۡ هَٰذَا سِحۡرٞ مُّبِينٌ

Idan kuma an karanta musu ayoyinmu bayyanannu sai waxanda suka kafirce wa gaskiya lokacin da ta zo musu su ce: “Wannan sihiri ne mabayyani.”



Surah: Suratul Ahqaf 

Ayah : 8

أَمۡ يَقُولُونَ ٱفۡتَرَىٰهُۖ قُلۡ إِنِ ٱفۡتَرَيۡتُهُۥ فَلَا تَمۡلِكُونَ لِي مِنَ ٱللَّهِ شَيۡـًٔاۖ هُوَ أَعۡلَمُ بِمَا تُفِيضُونَ فِيهِۚ كَفَىٰ بِهِۦ شَهِيدَۢا بَيۡنِي وَبَيۡنَكُمۡۖ وَهُوَ ٱلۡغَفُورُ ٱلرَّحِيمُ

A’a, cewa dai suka yi: “Qagar sa ya yi.” Ka ce: “Idan har na qage shi ne to ba za ku amfana min komai ba game da Allah; Shi ne Ya fi sanin abin da kuke kutsawa cikinsa[1]; Shi Ya isa Mai shaida tsakanina da ku; kuma Shi ne Mai gafara, Mai rahama.”


1- Watau na saqon Alqur’ani da saqon Manzon Allah ().


Surah: Suratul Ahqaf 

Ayah : 12

وَمِن قَبۡلِهِۦ كِتَٰبُ مُوسَىٰٓ إِمَامٗا وَرَحۡمَةٗۚ وَهَٰذَا كِتَٰبٞ مُّصَدِّقٞ لِّسَانًا عَرَبِيّٗا لِّيُنذِرَ ٱلَّذِينَ ظَلَمُواْ وَبُشۡرَىٰ لِلۡمُحۡسِنِينَ

A gabaninsa kuwa akwai littafin Musa wanda yake jagora ne da rahama. Wannan littafin kuma mai gaskata (na gabaninsa) ne a harshen Larabci, don ya gargaxi waxanda suka kafirta da kuma yin albishir ga masu kyautatawa



Surah: Suratul Ahqaf 

Ayah : 30

قَالُواْ يَٰقَوۡمَنَآ إِنَّا سَمِعۡنَا كِتَٰبًا أُنزِلَ مِنۢ بَعۡدِ مُوسَىٰ مُصَدِّقٗا لِّمَا بَيۡنَ يَدَيۡهِ يَهۡدِيٓ إِلَى ٱلۡحَقِّ وَإِلَىٰ طَرِيقٖ مُّسۡتَقِيمٖ

Suka ce: “Ya ku mutanenmu, haqiqa mu mun jiwo wani littafi da aka saukar bayan Musa, mai gaskata abin da yake gabaninsa, yana shiryarwa zuwa gaskiya da kuma zuwa tafarki madaidaici



Surah: Suratu Muhammad

Ayah : 24

أَفَلَا يَتَدَبَّرُونَ ٱلۡقُرۡءَانَ أَمۡ عَلَىٰ قُلُوبٍ أَقۡفَالُهَآ

Yanzu ba za su yi tunani na basira ba (game da) Alqur’ani ba, ko kuwa akwai wani rufi ne a kan zukatansu?



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 77

إِنَّهُۥ لَقُرۡءَانٞ كَرِيمٞ

Lalle shi Alqur’ani ne mai girma



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 78

فِي كِتَٰبٖ مَّكۡنُونٖ

A cikin littafi abin kiyayewa (daga wani sauyi).[1]


1- Shi ne Lauhul Mahfuz.


Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 79

لَّا يَمَسُّهُۥٓ إِلَّا ٱلۡمُطَهَّرُونَ

Babu mai tava shi sai tsarkakakku



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 80

تَنزِيلٞ مِّن رَّبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Saukakke ne daga Ubangijin talikai



Surah: Suratul Hadid

Ayah : 9

هُوَ ٱلَّذِي يُنَزِّلُ عَلَىٰ عَبۡدِهِۦٓ ءَايَٰتِۭ بَيِّنَٰتٖ لِّيُخۡرِجَكُم مِّنَ ٱلظُّلُمَٰتِ إِلَى ٱلنُّورِۚ وَإِنَّ ٱللَّهَ بِكُمۡ لَرَءُوفٞ رَّحِيمٞ

Shi ne Wanda Yake saukar da ayoyi bayyanannu ga Bawansa don Ya fitar da ku daga duffai zuwa haske. Kuma lalle Allah Mai tausayi ne, Mai rahama a gare ku



Surah: Suratul Hashr

Ayah : 21

لَوۡ أَنزَلۡنَا هَٰذَا ٱلۡقُرۡءَانَ عَلَىٰ جَبَلٖ لَّرَأَيۡتَهُۥ خَٰشِعٗا مُّتَصَدِّعٗا مِّنۡ خَشۡيَةِ ٱللَّهِۚ وَتِلۡكَ ٱلۡأَمۡثَٰلُ نَضۡرِبُهَا لِلنَّاسِ لَعَلَّهُمۡ يَتَفَكَّرُونَ

Da za Mu saukar da wannan Alqur’ani ga wani dutse, da lalle ka gan shi yana mai qasqantar da kai mai tsattsagewa don tsoron Allah. Waxannan misalan Muna buga wa mutane su ne don su yi tunani



Surah: Suratul Qalam

Ayah : 15

إِذَا تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِ ءَايَٰتُنَا قَالَ أَسَٰطِيرُ ٱلۡأَوَّلِينَ

Idan ana karanta masa ayoyinmu sai ya ce: “Tatsuniyoyin mutanen farko ne.”



Surah: Suratul Haqqa

Ayah : 43

تَنزِيلٞ مِّن رَّبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Shi saukakke ne daga Ubangijin halittu



Surah: Suratul Jinn

Ayah : 1

قُلۡ أُوحِيَ إِلَيَّ أَنَّهُ ٱسۡتَمَعَ نَفَرٞ مِّنَ ٱلۡجِنِّ فَقَالُوٓاْ إِنَّا سَمِعۡنَا قُرۡءَانًا عَجَبٗا

Ka ce: “An yiwo min wahayi na cewa, wata jama’a ta aljannu[1] sun saurari (karatun Alqur’ani), sai suka ce: “Lalle mu mun ji Alqur’ani mai ban mamaki


1- Su ne wasu aljannu da suka saurari karatun Annabi () a wani wuri da ake kira Baxnu Nakhla, lokacin da yake yi wa sahabbansa sallar asuba.


Surah: Suratul Jinn

Ayah : 2

يَهۡدِيٓ إِلَى ٱلرُّشۡدِ فَـَٔامَنَّا بِهِۦۖ وَلَن نُّشۡرِكَ بِرَبِّنَآ أَحَدٗا

“Yana shiryarwa zuwa ga daidai, saboda haka muka yi imani da shi; ba kuwa za mu haxa wani da Ubangijinmu ba har abada



Surah: Suratul Jinn

Ayah : 13

وَأَنَّا لَمَّا سَمِعۡنَا ٱلۡهُدَىٰٓ ءَامَنَّا بِهِۦۖ فَمَن يُؤۡمِنۢ بِرَبِّهِۦ فَلَا يَخَافُ بَخۡسٗا وَلَا رَهَقٗا

“Lalle kuma mu lokacin da muka ji Alqur’ani, sai muka yi imani da shi, to duk wanda zai yi imani da Ubangijinsa, to ba zai ji tsoron qwara ko zalunci ba[1]


1- Watau ba za a tauye masa ladansa ba, kuma ba za a qara masa wani laifin da bai aikata ba.


Surah: Suratul Muzzammil

Ayah : 4

أَوۡ زِدۡ عَلَيۡهِ وَرَتِّلِ ٱلۡقُرۡءَانَ تَرۡتِيلًا

Ko ka qara a kansa, ka kuma karanta Alqur’ani daki-daki



Surah: Suratul Muzzammil

Ayah : 20

۞إِنَّ رَبَّكَ يَعۡلَمُ أَنَّكَ تَقُومُ أَدۡنَىٰ مِن ثُلُثَيِ ٱلَّيۡلِ وَنِصۡفَهُۥ وَثُلُثَهُۥ وَطَآئِفَةٞ مِّنَ ٱلَّذِينَ مَعَكَۚ وَٱللَّهُ يُقَدِّرُ ٱلَّيۡلَ وَٱلنَّهَارَۚ عَلِمَ أَن لَّن تُحۡصُوهُ فَتَابَ عَلَيۡكُمۡۖ فَٱقۡرَءُواْ مَا تَيَسَّرَ مِنَ ٱلۡقُرۡءَانِۚ عَلِمَ أَن سَيَكُونُ مِنكُم مَّرۡضَىٰ وَءَاخَرُونَ يَضۡرِبُونَ فِي ٱلۡأَرۡضِ يَبۡتَغُونَ مِن فَضۡلِ ٱللَّهِ وَءَاخَرُونَ يُقَٰتِلُونَ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِۖ فَٱقۡرَءُواْ مَا تَيَسَّرَ مِنۡهُۚ وَأَقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَءَاتُواْ ٱلزَّكَوٰةَ وَأَقۡرِضُواْ ٱللَّهَ قَرۡضًا حَسَنٗاۚ وَمَا تُقَدِّمُواْ لِأَنفُسِكُم مِّنۡ خَيۡرٖ تَجِدُوهُ عِندَ ٱللَّهِ هُوَ خَيۡرٗا وَأَعۡظَمَ أَجۡرٗاۚ وَٱسۡتَغۡفِرُواْ ٱللَّهَۖ إِنَّ ٱللَّهَ غَفُورٞ رَّحِيمُۢ

Lalle Ubangijinka Yana sane da cewa kai kana tsayawa qasa da kashi biyu cikin uku na dare, da kuma rabinsa, da kuma xaya bisa ukunsa, kai da wata jama’ar da take tare da kai. Allah ne kuma Yake qaddara dare da rana. Ya san kuma cewa, ba za ku iya qididdige (sa’o’insa) ba, don haka sai Ya yafe muku; to sai ku karanta abin da ya sauqaqa daga Alqur’ani. Ya san cewa daga cikinku akwai waxanda za su kasance marasa lafiya, waxansu kuma suna tafiya a bayan qasa don fatauci suna neman falala daga Allah, waxansu kuma suna yin yaqi saboda Allah; to sai ku karanta abin da ya sauqaqa daga gare shi (Alqur’ani). Ku kuma tsayar da salla, ku kuma ba da zakka, kuma ku bai wa Allah rance kyakkyawa[1]. Kuma abin da kuka gabatar wa kanku na wani alheri, to za ku same shi wurin Allah, shi ya fi alheri ya kuma fi girman lada. Ku kuma nemi gafarar Allah; lalle Allah Mai gafara ne, Mai jin qai


1- Watau su ciyar da dukiyoyinsu don Allah wuraren da suka dace.


Surah: Suratul Insan

Ayah : 23

إِنَّا نَحۡنُ نَزَّلۡنَا عَلَيۡكَ ٱلۡقُرۡءَانَ تَنزِيلٗا

Lalle Mu Muka saukar maka da Alqur’ani daki-daki



Surah: Suratul Muxaffifin

Ayah : 13

إِذَا تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِ ءَايَٰتُنَا قَالَ أَسَٰطِيرُ ٱلۡأَوَّلِينَ

Idan ana karanta masa ayoyinmu sai ya ce: “Wannan tatsuniyoyi ne na mutanen farko.”



Surah: Suratul Inshiqaq

Ayah : 21

وَإِذَا قُرِئَ عَلَيۡهِمُ ٱلۡقُرۡءَانُ لَا يَسۡجُدُونَۤ۩

Idan kuma an karanta musu Alqur’ani ba sa yin sujjada?



Surah: Suratul Alaq

Ayah : 1

ٱقۡرَأۡ بِٱسۡمِ رَبِّكَ ٱلَّذِي خَلَقَ

Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, Wanda Ya yi halitta



Surah: Suratul Alaq

Ayah : 3

ٱقۡرَأۡ وَرَبُّكَ ٱلۡأَكۡرَمُ

Ka yi karatu alhali Ubangijinka Shi ne mafi karamci