Surah: Suratul Ahzab

Ayah : 34

وَٱذۡكُرۡنَ مَا يُتۡلَىٰ فِي بُيُوتِكُنَّ مِنۡ ءَايَٰتِ ٱللَّهِ وَٱلۡحِكۡمَةِۚ إِنَّ ٱللَّهَ كَانَ لَطِيفًا خَبِيرًا

Kuma ku tuna abin da ake karantawa a cikin gidajenku na ayoyin Allah da kuma hikima. Lalle Allah Ya kasance Mai tausayawa ne, Masani



Surah: Suratu Saba’i

Ayah : 6

وَيَرَى ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡعِلۡمَ ٱلَّذِيٓ أُنزِلَ إِلَيۡكَ مِن رَّبِّكَ هُوَ ٱلۡحَقَّ وَيَهۡدِيٓ إِلَىٰ صِرَٰطِ ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡحَمِيدِ

Waxanda aka bai wa ilimi kuma suna ganin abin da aka saukar maka daga Ubangijinka shi ne gaskiya, kuma yana shiryarwa ne zuwa hanyar (Allah) Mabuwayi, Sha-yabo



Surah: Suratu Saba’i

Ayah : 31

وَقَالَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لَن نُّؤۡمِنَ بِهَٰذَا ٱلۡقُرۡءَانِ وَلَا بِٱلَّذِي بَيۡنَ يَدَيۡهِۗ وَلَوۡ تَرَىٰٓ إِذِ ٱلظَّـٰلِمُونَ مَوۡقُوفُونَ عِندَ رَبِّهِمۡ يَرۡجِعُ بَعۡضُهُمۡ إِلَىٰ بَعۡضٍ ٱلۡقَوۡلَ يَقُولُ ٱلَّذِينَ ٱسۡتُضۡعِفُواْ لِلَّذِينَ ٱسۡتَكۡبَرُواْ لَوۡلَآ أَنتُمۡ لَكُنَّا مُؤۡمِنِينَ

Kuma kafirai suka ce: “Ba za mu yi imani da wannan Alqur’ani ba, haka ma da wanda yake gabaninsa (na saukakkun littattafai).” Da kuwa za ka ga lokacin da za a tsai da azzalumai wajen Ubangijinsu suna mayar wa da juna magana, masu rauninsu (mabiya) suna ce wa masu girman kai (watau shugabanninsu): “Ba don ku ba da mun zamanto muminai.”



Surah: Suratu Saba’i

Ayah : 43

وَإِذَا تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِمۡ ءَايَٰتُنَا بَيِّنَٰتٖ قَالُواْ مَا هَٰذَآ إِلَّا رَجُلٞ يُرِيدُ أَن يَصُدَّكُمۡ عَمَّا كَانَ يَعۡبُدُ ءَابَآؤُكُمۡ وَقَالُواْ مَا هَٰذَآ إِلَّآ إِفۡكٞ مُّفۡتَرٗىۚ وَقَالَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لِلۡحَقِّ لَمَّا جَآءَهُمۡ إِنۡ هَٰذَآ إِلَّا سِحۡرٞ مُّبِينٞ

Idan kuma ana karanta musu ayoyinmu mabayyana sai su ce: “Wannan ai ba wani ba ne sai wani mutum da yake nufin ya hana ku (bauta wa) abin da iyayenku suka kasance suna bauta wa.” Suka kuma ce: “Wannan ai ba wani abu ba ne in ban da qarya da aka qirqira.” Waxanda kuma suka kafirta suka ce game da gaskiya yayin da ta zo musu: “Wannan ba wani abu ba ne sai sihiri mabayyani.”



Surah: Suratu Faxir

Ayah : 29

إِنَّ ٱلَّذِينَ يَتۡلُونَ كِتَٰبَ ٱللَّهِ وَأَقَامُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَأَنفَقُواْ مِمَّا رَزَقۡنَٰهُمۡ سِرّٗا وَعَلَانِيَةٗ يَرۡجُونَ تِجَٰرَةٗ لَّن تَبُورَ

Lalle waxanda suke karanta Littafin Allah suka kuma tsai da salla suka kuma ciyar daga abin da Muka arzuta su a voye da sarari, suna burin kasuwancin da ba zai yi tazgaro ba



Surah: Suratu Faxir

Ayah : 31

وَٱلَّذِيٓ أَوۡحَيۡنَآ إِلَيۡكَ مِنَ ٱلۡكِتَٰبِ هُوَ ٱلۡحَقُّ مُصَدِّقٗا لِّمَا بَيۡنَ يَدَيۡهِۗ إِنَّ ٱللَّهَ بِعِبَادِهِۦ لَخَبِيرُۢ بَصِيرٞ

Kuma abin da Muka yiwo maka wahayinsa na Littafi shi ne gaskiya, yana gaskata abin da yake gabaninsa (na littattafai). Lalle Allah game da bayinsa Masani ne, Mai gani



Surah: Suratu Yasin

Ayah : 5

تَنزِيلَ ٱلۡعَزِيزِ ٱلرَّحِيمِ

(Alqur’ani) saukarwar (Allah) Mabuwayi Mai jin qai ne



Surah: Suratu Sad

Ayah : 29

كِتَٰبٌ أَنزَلۡنَٰهُ إِلَيۡكَ مُبَٰرَكٞ لِّيَدَّبَّرُوٓاْ ءَايَٰتِهِۦ وَلِيَتَذَكَّرَ أُوْلُواْ ٱلۡأَلۡبَٰبِ

Littafi ne mai albarka da Muka saukar maka da shi domin su yi tuntuntuni game da ayoyinsa, don kuma masu hankula su wa’azantu



Surah: Suratuz Zumar

Ayah : 1

تَنزِيلُ ٱلۡكِتَٰبِ مِنَ ٱللَّهِ ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡحَكِيمِ

Saukar Littafi daga Allah ne Mabuwayi, Mai hikima



Surah: Suratuz Zumar

Ayah : 2

إِنَّآ أَنزَلۡنَآ إِلَيۡكَ ٱلۡكِتَٰبَ بِٱلۡحَقِّ فَٱعۡبُدِ ٱللَّهَ مُخۡلِصٗا لَّهُ ٱلدِّينَ

Lalle Mu Muka saukar maka Littafi da gaskiya, to ka bauta wa Allah kana mai tsantsanta addini a gare Shi



Surah: Suratuz Zumar

Ayah : 23

ٱللَّهُ نَزَّلَ أَحۡسَنَ ٱلۡحَدِيثِ كِتَٰبٗا مُّتَشَٰبِهٗا مَّثَانِيَ تَقۡشَعِرُّ مِنۡهُ جُلُودُ ٱلَّذِينَ يَخۡشَوۡنَ رَبَّهُمۡ ثُمَّ تَلِينُ جُلُودُهُمۡ وَقُلُوبُهُمۡ إِلَىٰ ذِكۡرِ ٱللَّهِۚ ذَٰلِكَ هُدَى ٱللَّهِ يَهۡدِي بِهِۦ مَن يَشَآءُۚ وَمَن يُضۡلِلِ ٱللَّهُ فَمَا لَهُۥ مِنۡ هَادٍ

Allah Ya saukar da mafi kyan zance: Alqur’ani mai kama da juna, mai biyunta (saqo), tsikar fatun waxanda suke tsoron Ubangijinsu suna tashi, sannan fatunsu su yi taushi, zukatansu kuwa su koma zuwa ambaton Allah. Wannan ita ce shiriyar Allah, Yana shiyar da wanda Ya ga dama da ita. Wanda kuma Allah Ya vatar to ba shi da mai shiryar da shi



Surah: Suratuz Zumar

Ayah : 41

إِنَّآ أَنزَلۡنَا عَلَيۡكَ ٱلۡكِتَٰبَ لِلنَّاسِ بِٱلۡحَقِّۖ فَمَنِ ٱهۡتَدَىٰ فَلِنَفۡسِهِۦۖ وَمَن ضَلَّ فَإِنَّمَا يَضِلُّ عَلَيۡهَاۖ وَمَآ أَنتَ عَلَيۡهِم بِوَكِيلٍ

Lalle Mu Mun saukar maka da Littafi da gaskiya ga mutane; saboda haka duk wanda ya shiriya to ya yi wa kansa alheri, wanda kuwa ya vata, to lalle ya vata ne don kansa; kuma kai ba wakili ba ne a kansu



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 2

تَنزِيلُ ٱلۡكِتَٰبِ مِنَ ٱللَّهِ ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡعَلِيمِ

Saukarwar Littafi daga Allah ne Mabuwayi, Masani



Surah: Suratu Fussilat

Ayah : 2

تَنزِيلٞ مِّنَ ٱلرَّحۡمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ

(Alqur’ani) saukakke ne daga (Allah) Mai rahama, Mai jin qai



Surah: Suratu Fussilat

Ayah : 3

كِتَٰبٞ فُصِّلَتۡ ءَايَٰتُهُۥ قُرۡءَانًا عَرَبِيّٗا لِّقَوۡمٖ يَعۡلَمُونَ

(Shi) Littafi ne Alqur’ani Balarabe da aka rarrabe ayoyinsa ga mutanen da suke sanin (ma’anarsa)



Surah: Suratu Fussilat

Ayah : 4

بَشِيرٗا وَنَذِيرٗا فَأَعۡرَضَ أَكۡثَرُهُمۡ فَهُمۡ لَا يَسۡمَعُونَ

Mai albishir ne kuma mai gargaxi, sai yawancinsu suka bijire, don haka su ba sa jin (kira)



Surah: Suratu Fussilat

Ayah : 26

وَقَالَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لَا تَسۡمَعُواْ لِهَٰذَا ٱلۡقُرۡءَانِ وَٱلۡغَوۡاْ فِيهِ لَعَلَّكُمۡ تَغۡلِبُونَ

Waxanda kuma suka kafirta suka ce: “Kada ku saurari wannan Alqur’ani, ku riqa yin hayaniya a cikinsa[1] don ku yi rinjaye.”


1- Watau ku riqa hayaniya da hargowa duk sanda ake karanta shi domin kada mutane su ji abin da ake faxa.


Surah: Suratu Fussilat

Ayah : 41

إِنَّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ بِٱلذِّكۡرِ لَمَّا جَآءَهُمۡۖ وَإِنَّهُۥ لَكِتَٰبٌ عَزِيزٞ

Lalle waxanda suka kafirce wa Alqur’ani lokacin da ya zo musu (tabbas Allah zai saka musu). Lalle kuma shi littafi ne mabuwayi



Surah: Suratu Fussilat

Ayah : 42

لَّا يَأۡتِيهِ ٱلۡبَٰطِلُ مِنۢ بَيۡنِ يَدَيۡهِ وَلَا مِنۡ خَلۡفِهِۦۖ تَنزِيلٞ مِّنۡ حَكِيمٍ حَمِيدٖ

Varna ba ta zuwa masa ta gabansa ko kuma ta bayansa; saukakke ne daga Mai hikima, Sha-yabo



Surah: Suratu Fussilat

Ayah : 44

وَلَوۡ جَعَلۡنَٰهُ قُرۡءَانًا أَعۡجَمِيّٗا لَّقَالُواْ لَوۡلَا فُصِّلَتۡ ءَايَٰتُهُۥٓۖ ءَا۬عۡجَمِيّٞ وَعَرَبِيّٞۗ قُلۡ هُوَ لِلَّذِينَ ءَامَنُواْ هُدٗى وَشِفَآءٞۚ وَٱلَّذِينَ لَا يُؤۡمِنُونَ فِيٓ ءَاذَانِهِمۡ وَقۡرٞ وَهُوَ عَلَيۡهِمۡ عَمًىۚ أُوْلَـٰٓئِكَ يُنَادَوۡنَ مِن مَّكَانِۭ بَعِيدٖ

Da Mun sanya shi Alqur’ani Ba’ajame da tabbas za su ce: “Me ya hana a bayyana ayoyinsa? Yanzu (a ce Alqur’ani) Ba’ajame (Annabi kuma) Balarabe?” Ka ce: “Shi ga waxanda suka yi imani shiriya ne da waraka. Waxanda kuwa ba sa yin imani akwai nauyi cikin kunnuwansu, shi kuma makanta ne a gare su.” Waxannan (sun yi kama da waxanda) ake kira daga wuri mai nisa



Surah: Suratus Shura

Ayah : 17

ٱللَّهُ ٱلَّذِيٓ أَنزَلَ ٱلۡكِتَٰبَ بِٱلۡحَقِّ وَٱلۡمِيزَانَۗ وَمَا يُدۡرِيكَ لَعَلَّ ٱلسَّاعَةَ قَرِيبٞ

Allah ne Ya saukar da Littafi da gaskiya da kuma adalci. Me yake sanar da kai cewa ko alqiyama kusa take



Surah: Suratus Shura

Ayah : 52

وَكَذَٰلِكَ أَوۡحَيۡنَآ إِلَيۡكَ رُوحٗا مِّنۡ أَمۡرِنَاۚ مَا كُنتَ تَدۡرِي مَا ٱلۡكِتَٰبُ وَلَا ٱلۡإِيمَٰنُ وَلَٰكِن جَعَلۡنَٰهُ نُورٗا نَّهۡدِي بِهِۦ مَن نَّشَآءُ مِنۡ عِبَادِنَاۚ وَإِنَّكَ لَتَهۡدِيٓ إِلَىٰ صِرَٰطٖ مُّسۡتَقِيمٖ

Kuma kamar haka ne Muka yiwo maka wahayin Ruhi (watau Alqur’ani) daga umarninmu. Ba ka zamanto ka san mene ne littafi ko kuma imani ba, sai dai kuma Mun sanya shi (Alqur’ani) haske ne da Muke shiryar da wanda Muka ga dama daga bayinmu da shi. Lalle kuma kai tabbas kana shiryarwa zuwa ga tafarki madaidaici



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 1

حمٓ

HA MIM[1]


1- Duba Suratul Baqara, aya ta 1, hashiya ta 8.


Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 2

وَٱلۡكِتَٰبِ ٱلۡمُبِينِ

Na rantse da Littafi mabayyani (Alqur’ani)



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 3

إِنَّا جَعَلۡنَٰهُ قُرۡءَٰنًا عَرَبِيّٗا لَّعَلَّكُمۡ تَعۡقِلُونَ

Lalle Mu Mun sanya shi ya zamo abin karantawa cikin harshen Larabci domin ku hankalta



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 4

وَإِنَّهُۥ فِيٓ أُمِّ ٱلۡكِتَٰبِ لَدَيۡنَا لَعَلِيٌّ حَكِيمٌ

Lalle kuma shi (Alqur’ani) a cikin Littafi Lauhul-Mahafuzu a wurinmu tabbas maxaukaki ne, mai hikima



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 31

وَقَالُواْ لَوۡلَا نُزِّلَ هَٰذَا ٱلۡقُرۡءَانُ عَلَىٰ رَجُلٖ مِّنَ ٱلۡقَرۡيَتَيۡنِ عَظِيمٍ

Suka kuma ce: “Me ya hana a saukar da wannan Alqur’ani ga wani babban mutum, daga alqaryun nan guda biyu?”



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 2

وَٱلۡكِتَٰبِ ٱلۡمُبِينِ

Na rantse da Littafi mai bayyanawa (shi ne Alqur’ani)



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 3

إِنَّآ أَنزَلۡنَٰهُ فِي لَيۡلَةٖ مُّبَٰرَكَةٍۚ إِنَّا كُنَّا مُنذِرِينَ

Lalle Mu Muka saukar da shi a cikin dare mai albarka[1]. Lalle Mu Mun kasance Masu gargaxi


1- Shi ne daren Lailatul Qadari. Duba Suratul Qadri.


Surah: Suratul Jasiya

Ayah : 2

تَنزِيلُ ٱلۡكِتَٰبِ مِنَ ٱللَّهِ ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡحَكِيمِ

Saukar da Alqur’ani daga Allah ne Mabuwayi, Mai hikima