Surah: Suratul Buruj

Ayah : 4

قُتِلَ أَصۡحَٰبُ ٱلۡأُخۡدُودِ

An la’anci ma’abota rami (na azabtar da muminai)[1]


1- Wani azzalumin sarki ne da aka yi a Najrana ta qasar Yaman kafin aiko Annabi () wanda aka haqa masa rami aka hura wuta, ya riqa jefa muminai a cikinsa yana qona su da ransu.


Surah: Suratul Buruj

Ayah : 5

ٱلنَّارِ ذَاتِ ٱلۡوَقُودِ

Na wuta mai ruruwa



Surah: Suratul Buruj

Ayah : 6

إِذۡ هُمۡ عَلَيۡهَا قُعُودٞ

Yayin da suke zaune a gefenta



Surah: Suratul Buruj

Ayah : 7

وَهُمۡ عَلَىٰ مَا يَفۡعَلُونَ بِٱلۡمُؤۡمِنِينَ شُهُودٞ

Alhali su suna kallon abin da suke aikata wa muminai



Surah: Suratul Buruj

Ayah : 8

وَمَا نَقَمُواْ مِنۡهُمۡ إِلَّآ أَن يُؤۡمِنُواْ بِٱللَّهِ ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡحَمِيدِ

Babu kuwa abin da suke tuhumar su da shi sai don kawai sun yi imani da Allah Mabuwayi, Sha-yabo



Surah: Suratul Buruj

Ayah : 9

ٱلَّذِي لَهُۥ مُلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ وَٱللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ شَهِيدٌ

Wanda Yake da mulkin sammai da qasa. Allah kuma Mai ganin komai ne



Surah: Suratul Buruj

Ayah : 10

إِنَّ ٱلَّذِينَ فَتَنُواْ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ وَٱلۡمُؤۡمِنَٰتِ ثُمَّ لَمۡ يَتُوبُواْ فَلَهُمۡ عَذَابُ جَهَنَّمَ وَلَهُمۡ عَذَابُ ٱلۡحَرِيقِ

Lalle waxanda suka azabtar da muminai maza da muminai mata sannan ba su tuba ba, to suna da azabar Jahannama, suna kuma da azabar quna