Surah: Suratul Fatiha

Ayah : 4

مَٰلِكِ يَوۡمِ ٱلدِّينِ

Mamallakin ranar sakamako



Surah: Suratu Ali-Imran

Ayah : 185

كُلُّ نَفۡسٖ ذَآئِقَةُ ٱلۡمَوۡتِۗ وَإِنَّمَا تُوَفَّوۡنَ أُجُورَكُمۡ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِۖ فَمَن زُحۡزِحَ عَنِ ٱلنَّارِ وَأُدۡخِلَ ٱلۡجَنَّةَ فَقَدۡ فَازَۗ وَمَا ٱلۡحَيَوٰةُ ٱلدُّنۡيَآ إِلَّا مَتَٰعُ ٱلۡغُرُورِ

Kowane rai zai xanxani mutuwa. Kuma a ranar alqiyama ne za a cika muku ladan ayyukanku; to duk wanda aka nisanta shi daga wuta, kuma aka shigar da shi Aljanna, to haqiqa ya rabauta. Kuma rayuwar duniya ba komai ba ce face jin daxi mai ruxarwa



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 82

وَٱلَّذِيٓ أَطۡمَعُ أَن يَغۡفِرَ لِي خَطِيٓـَٔتِي يَوۡمَ ٱلدِّينِ

“Wanda kuma nake kwaxayin Ya gafarta min kurakuraina ranar sakamako



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 20

وَقَالُواْ يَٰوَيۡلَنَا هَٰذَا يَوۡمُ ٱلدِّينِ

Sai su ce: “Kaitonmu!” (Sai a ce da su): “Wannan ita ce ranar sakamako



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 21

هَٰذَا يَوۡمُ ٱلۡفَصۡلِ ٱلَّذِي كُنتُم بِهِۦ تُكَذِّبُونَ

“Wannan ita ce ranar hukunci wadda kuka kasance kuna qaryatawa.”



Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 12

يَسۡـَٔلُونَ أَيَّانَ يَوۡمُ ٱلدِّينِ

Suna tambayar yaushe ne ranar sakamako?



Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 13

يَوۡمَ هُمۡ عَلَى ٱلنَّارِ يُفۡتَنُونَ

A ranar da su za a azabtar da su kan wuta



Surah: Suratuz Zariyat

Ayah : 14

ذُوقُواْ فِتۡنَتَكُمۡ هَٰذَا ٱلَّذِي كُنتُم بِهِۦ تَسۡتَعۡجِلُونَ

(A ce da su): “Ku xanxani azabarku, wannan shi ne abin da kuka kasance kuna neman gaggautowarsa.”



Surah: Suratul Infixar

Ayah : 14

وَإِنَّ ٱلۡفُجَّارَ لَفِي جَحِيمٖ

Lalle kuma fajirai tabbas suna cikin (wutar) Jahima



Surah: Suratul Infixar

Ayah : 15

يَصۡلَوۡنَهَا يَوۡمَ ٱلدِّينِ

Za su qonu da ita ranar sakamako



Surah: Suratul Infixar

Ayah : 16

وَمَا هُمۡ عَنۡهَا بِغَآئِبِينَ

Kuma su ba masu rabuwa ne da ita ba



Surah: Suratul Infixar

Ayah : 17

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا يَوۡمُ ٱلدِّينِ

Kuma kai me ya sanar da kai mece ce ranar sakamako?



Surah: Suratul Infixar

Ayah : 18

ثُمَّ مَآ أَدۡرَىٰكَ مَا يَوۡمُ ٱلدِّينِ

Sannan me ya sanar da kai mece ce ranar sakamako?



Surah: Suratul Infixar

Ayah : 19

يَوۡمَ لَا تَمۡلِكُ نَفۡسٞ لِّنَفۡسٖ شَيۡـٔٗاۖ وَٱلۡأَمۡرُ يَوۡمَئِذٖ لِّلَّهِ

(Ita ce) ranar da wani rai ba ya mallakar wani amfani ga wani rai; al’amari kuwa (gaba xayansa) a wannan ranar yana ga Allah