Surah: Suratul Ahqaf 

Ayah : 7

وَإِذَا تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِمۡ ءَايَٰتُنَا بَيِّنَٰتٖ قَالَ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لِلۡحَقِّ لَمَّا جَآءَهُمۡ هَٰذَا سِحۡرٞ مُّبِينٌ

Idan kuma an karanta musu ayoyinmu bayyanannu sai waxanda suka kafirce wa gaskiya lokacin da ta zo musu su ce: “Wannan sihiri ne mabayyani.”



Surah: Suratul Ahqaf 

Ayah : 8

أَمۡ يَقُولُونَ ٱفۡتَرَىٰهُۖ قُلۡ إِنِ ٱفۡتَرَيۡتُهُۥ فَلَا تَمۡلِكُونَ لِي مِنَ ٱللَّهِ شَيۡـًٔاۖ هُوَ أَعۡلَمُ بِمَا تُفِيضُونَ فِيهِۚ كَفَىٰ بِهِۦ شَهِيدَۢا بَيۡنِي وَبَيۡنَكُمۡۖ وَهُوَ ٱلۡغَفُورُ ٱلرَّحِيمُ

A’a, cewa dai suka yi: “Qagar sa ya yi.” Ka ce: “Idan har na qage shi ne to ba za ku amfana min komai ba game da Allah; Shi ne Ya fi sanin abin da kuke kutsawa cikinsa[1]; Shi Ya isa Mai shaida tsakanina da ku; kuma Shi ne Mai gafara, Mai rahama.”


1- Watau na saqon Alqur’ani da saqon Manzon Allah ().


Surah: Suratul Qalam

Ayah : 15

إِذَا تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِ ءَايَٰتُنَا قَالَ أَسَٰطِيرُ ٱلۡأَوَّلِينَ

Idan ana karanta masa ayoyinmu sai ya ce: “Tatsuniyoyin mutanen farko ne.”



Surah: Suratul Muxaffifin

Ayah : 13

إِذَا تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِ ءَايَٰتُنَا قَالَ أَسَٰطِيرُ ٱلۡأَوَّلِينَ

Idan ana karanta masa ayoyinmu sai ya ce: “Wannan tatsuniyoyi ne na mutanen farko.”



Surah: Suratul Inshiqaq

Ayah : 21

وَإِذَا قُرِئَ عَلَيۡهِمُ ٱلۡقُرۡءَانُ لَا يَسۡجُدُونَۤ۩

Idan kuma an karanta musu Alqur’ani ba sa yin sujjada?