Surah: Suratul Qasas

Ayah : 54

أُوْلَـٰٓئِكَ يُؤۡتَوۡنَ أَجۡرَهُم مَّرَّتَيۡنِ بِمَا صَبَرُواْ وَيَدۡرَءُونَ بِٱلۡحَسَنَةِ ٱلسَّيِّئَةَ وَمِمَّا رَزَقۡنَٰهُمۡ يُنفِقُونَ

Waxannan (su ne) za a ba su ladansu ninki biyu saboda haqurin da suka yi. Kuma suna kawar da mummunan aiki da kyakkyawa, suna kuma ciyarwa daga abin da Muka arzuta su (da shi)



Surah: Suratul Ankabut

Ayah : 58

وَٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ لَنُبَوِّئَنَّهُم مِّنَ ٱلۡجَنَّةِ غُرَفٗا تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ خَٰلِدِينَ فِيهَاۚ نِعۡمَ أَجۡرُ ٱلۡعَٰمِلِينَ

Waxanda kuma suka yi imani suka kuma yi aiki nagari, lallai za Mu zaunar da su cikin manya-manyan gidaje a Aljanna (waxanda) qoramu za su riqa gudana ta qarqashinsu suna madawwama a cikinsu. Madalla da ladan masu aiki (nagari)



Surah: Suratul Ankabut

Ayah : 59

ٱلَّذِينَ صَبَرُواْ وَعَلَىٰ رَبِّهِمۡ يَتَوَكَّلُونَ

(Su ne) waxanda suka yi haquri, kuma ga Ubangijinsu kawai suke dogara



Surah: Suratu Luqman

Ayah : 17

يَٰبُنَيَّ أَقِمِ ٱلصَّلَوٰةَ وَأۡمُرۡ بِٱلۡمَعۡرُوفِ وَٱنۡهَ عَنِ ٱلۡمُنكَرِ وَٱصۡبِرۡ عَلَىٰ مَآ أَصَابَكَۖ إِنَّ ذَٰلِكَ مِنۡ عَزۡمِ ٱلۡأُمُورِ

“Ya kai xanxana, ka tsayar da salla kuma ka yi umarni da aikata alheri, ka kuma hana aikata mummunan aiki, kuma ka yi haquri bisa duk abin da ya same ka; lalle wannan yana daga manyan al’amura



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 77

فَٱصۡبِرۡ إِنَّ وَعۡدَ ٱللَّهِ حَقّٞۚ فَإِمَّا نُرِيَنَّكَ بَعۡضَ ٱلَّذِي نَعِدُهُمۡ أَوۡ نَتَوَفَّيَنَّكَ فَإِلَيۡنَا يُرۡجَعُونَ

Sai ka yi haquri, lalle alqawarin Allah gaskiya ne. To idan Mun nuna maka sashin abin da Muke yi musu alqawari da shi na narko; ko kuma Mun karvi ranka, to zuwa gare Mu dai za a dawo da su



Surah: Suratus Shura

Ayah : 43

وَلَمَن صَبَرَ وَغَفَرَ إِنَّ ذَٰلِكَ لَمِنۡ عَزۡمِ ٱلۡأُمُورِ

Tabbas kuma wanda ya yi haquri ya yafe, to tabbas wannan yana daga muhimman al’amura[1]


1- Watau haqurinsa zai zame masa alheri, har ma da al’ummarsa gaba xaya.


Surah: Suratul Ahqaf 

Ayah : 35

فَٱصۡبِرۡ كَمَا صَبَرَ أُوْلُواْ ٱلۡعَزۡمِ مِنَ ٱلرُّسُلِ وَلَا تَسۡتَعۡجِل لَّهُمۡۚ كَأَنَّهُمۡ يَوۡمَ يَرَوۡنَ مَا يُوعَدُونَ لَمۡ يَلۡبَثُوٓاْ إِلَّا سَاعَةٗ مِّن نَّهَارِۭۚ بَلَٰغٞۚ فَهَلۡ يُهۡلَكُ إِلَّا ٱلۡقَوۡمُ ٱلۡفَٰسِقُونَ

To ka yi haquri kamar yadda masu azama daga manzanni suka yi haquri, kada kuma ka nemi gaggauto musu (azaba). Kai ka ce ranar da za su ga abin da ake yi musu alqawarinsa kamar ba su zauna (a duniya) ba sai wani xan lokaci na wuni. (Wannan) isar da saqo ne. To akwai waxanda za a halakar in ba mutane fasiqai ba?



Surah: Suratul Hujurat

Ayah : 5

وَلَوۡ أَنَّهُمۡ صَبَرُواْ حَتَّىٰ تَخۡرُجَ إِلَيۡهِمۡ لَكَانَ خَيۡرٗا لَّهُمۡۚ وَٱللَّهُ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

Da za su yi haquri har sai ka fito wurinsu da ya fiye musu alheri. Allah kuma Mai gafara ne, Mai jin qai



Surah: Suratux Xur

Ayah : 16

ٱصۡلَوۡهَا فَٱصۡبِرُوٓاْ أَوۡ لَا تَصۡبِرُواْ سَوَآءٌ عَلَيۡكُمۡۖ إِنَّمَا تُجۡزَوۡنَ مَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

“To ku shige ta, sai ku yi haquri ko kada ku yi haquri duk xaya ne; ana saka muku ne kawai da abin da kuka kasance kuna aikatawa.”



Surah: Suratul Ma’arij

Ayah : 5

فَٱصۡبِرۡ صَبۡرٗا جَمِيلًا

Sai ka yi haquri kyakkyawan haquri



Surah: Suratul Muzzammil

Ayah : 10

وَٱصۡبِرۡ عَلَىٰ مَا يَقُولُونَ وَٱهۡجُرۡهُمۡ هَجۡرٗا جَمِيلٗا

Kuma ka yi haquri a kan abin da suke faxa, kuma ka qaurace musu kyakkyawar qauracewa[1]


1- Watau qauracewar da babu cutarwa a cikinta.


Surah: Suratul Muddassir

Ayah : 7

وَلِرَبِّكَ فَٱصۡبِرۡ

Ka kuma yi haquri game da Ubangijinka



Surah: Suratul Insan

Ayah : 12

وَجَزَىٰهُم بِمَا صَبَرُواْ جَنَّةٗ وَحَرِيرٗا

Ya kuma saka musu da Aljanna da alharini saboda haqurin da suka yi



Surah: Suratul Asr

Ayah : 3

إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ وَتَوَاصَوۡاْ بِٱلۡحَقِّ وَتَوَاصَوۡاْ بِٱلصَّبۡرِ

Sai dai waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka nagari, suka kuma yi wa juna wasiyya da gaskiya, suka kuma yi wa juna wasiyya da haquri