Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 31

وَمَآءٖ مَّسۡكُوبٖ

Da kuma ruwa mai kwarara



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 32

وَفَٰكِهَةٖ كَثِيرَةٖ

Da ababen marmari masu yawa



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 33

لَّا مَقۡطُوعَةٖ وَلَا مَمۡنُوعَةٖ

Ba masu yankewa ba kuma ba ababen hanawa ba



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 34

وَفُرُشٖ مَّرۡفُوعَةٍ

Da shimfixu masu daraja



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 35

إِنَّآ أَنشَأۡنَٰهُنَّ إِنشَآءٗ

Lalle Mu ne Muka qage su (‘yan matan Aljanna) sabuwar qagowa



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 36

فَجَعَلۡنَٰهُنَّ أَبۡكَارًا

Sannan Muka sanya su budurwai



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 37

عُرُبًا أَتۡرَابٗا

Masu begen mazajensu, tsarekun juna



Surah: Suratul Waqi’a

Ayah : 38

لِّأَصۡحَٰبِ ٱلۡيَمِينِ

Don ma’abota hannun dama



Surah: Suratul Hadid

Ayah : 21

سَابِقُوٓاْ إِلَىٰ مَغۡفِرَةٖ مِّن رَّبِّكُمۡ وَجَنَّةٍ عَرۡضُهَا كَعَرۡضِ ٱلسَّمَآءِ وَٱلۡأَرۡضِ أُعِدَّتۡ لِلَّذِينَ ءَامَنُواْ بِٱللَّهِ وَرُسُلِهِۦۚ ذَٰلِكَ فَضۡلُ ٱللَّهِ يُؤۡتِيهِ مَن يَشَآءُۚ وَٱللَّهُ ذُو ٱلۡفَضۡلِ ٱلۡعَظِيمِ

Ku yi rige-rige zuwa neman gafara daga Ubangijinku da Aljanna wadda faxinta kamar faxin sammai da qasa yake, an tanade ta don waxanda suka yi imani da Allah da manzanninsa. Wannan falalar Allah ce da Yake ba da ita ga wanda Ya ga dama. Allah kuwa Ma’abocin falala ne, Mai girma



Surah: Suratul Haqqa

Ayah : 22

فِي جَنَّةٍ عَالِيَةٖ

Cikin Aljanna maxaukakiya



Surah: Suratul Haqqa

Ayah : 23

قُطُوفُهَا دَانِيَةٞ

‘Ya’yan itatuwanta dab da dab suke



Surah: Suratul Insan

Ayah : 12

وَجَزَىٰهُم بِمَا صَبَرُواْ جَنَّةٗ وَحَرِيرٗا

Ya kuma saka musu da Aljanna da alharini saboda haqurin da suka yi



Surah: Suratul Insan

Ayah : 13

مُّتَّكِـِٔينَ فِيهَا عَلَى ٱلۡأَرَآئِكِۖ لَا يَرَوۡنَ فِيهَا شَمۡسٗا وَلَا زَمۡهَرِيرٗا

Suna masu kishingixa a cikinta a kan gadaje; ba sa ganin rana ko jin tsananin sanyi a cikinta



Surah: Suratul Insan

Ayah : 14

وَدَانِيَةً عَلَيۡهِمۡ ظِلَٰلُهَا وَذُلِّلَتۡ قُطُوفُهَا تَذۡلِيلٗا

Inuwoyinta kuma suna kusa da su, an kuma hore musu ‘ya’yan itatuwanta matuqar horewa



Surah: Suratul Insan

Ayah : 15

وَيُطَافُ عَلَيۡهِم بِـَٔانِيَةٖ مِّن فِضَّةٖ وَأَكۡوَابٖ كَانَتۡ قَوَارِيرَا۠

Ana kuma kai-kawo a tsakaninsu da qorai na azurfa da kofuna waxanda suka kasance na qarau



Surah: Suratul Insan

Ayah : 16

قَوَارِيرَاْ مِن فِضَّةٖ قَدَّرُوهَا تَقۡدِيرٗا

Qarau xin na azurfa ne, sun auna su, aunawa daidai da buqata



Surah: Suratul Insan

Ayah : 17

وَيُسۡقَوۡنَ فِيهَا كَأۡسٗا كَانَ مِزَاجُهَا زَنجَبِيلًا

Ana kuma shayar da su wata giya a cikinta, wadda mahaxinta ya kasance citta mai yatsu ce



Surah: Suratul Insan

Ayah : 18

عَيۡنٗا فِيهَا تُسَمَّىٰ سَلۡسَبِيلٗا

Wani marmaro ne a cikinta da ake kiran sa Salsabilu



Surah: Suratul Insan

Ayah : 19

۞وَيَطُوفُ عَلَيۡهِمۡ وِلۡدَٰنٞ مُّخَلَّدُونَ إِذَا رَأَيۡتَهُمۡ حَسِبۡتَهُمۡ لُؤۡلُؤٗا مَّنثُورٗا

Samari hadimai dawwamammu (da ba sa tsufa) kuma suna kai-kawo tsakaninsu, idan ka gan su sai ka yi tsammanin su wani lu’ulu’u ne da aka baza



Surah: Suratul Insan

Ayah : 20

وَإِذَا رَأَيۡتَ ثَمَّ رَأَيۡتَ نَعِيمٗا وَمُلۡكٗا كَبِيرًا

Idan kuma ka yi kallo a can, za ka ga ni’ima da kuma mulki qasaitacce



Surah: Suratul Insan

Ayah : 21

عَٰلِيَهُمۡ ثِيَابُ سُندُسٍ خُضۡرٞ وَإِسۡتَبۡرَقٞۖ وَحُلُّوٓاْ أَسَاوِرَ مِن فِضَّةٖ وَسَقَىٰهُمۡ رَبُّهُمۡ شَرَابٗا طَهُورًا

Suna sanye da korayen tufafin alharini marar kauri da na alharini mai kauri; aka kuma yi musu ado da warawarai na azurfa, Ubangijinsu kuma Ya shayar da su abin sha mai tsarki



Surah: Suratul Insan

Ayah : 22

إِنَّ هَٰذَا كَانَ لَكُمۡ جَزَآءٗ وَكَانَ سَعۡيُكُم مَّشۡكُورًا

Lalle wannan ya kasance sakamako ne a gare ku, kuma aikinku ya kasance abin godewa



Surah: Suratun Naba’i

Ayah : 31

إِنَّ لِلۡمُتَّقِينَ مَفَازًا

Lalle masu taqawa suna da babban rabo



Surah: Suratun Naba’i

Ayah : 32

حَدَآئِقَ وَأَعۡنَٰبٗا

(Su ne) gonaki da inabai



Surah: Suratun Naba’i

Ayah : 33

وَكَوَاعِبَ أَتۡرَابٗا

Da ‘yan mata tsaraiku



Surah: Suratun Naba’i

Ayah : 34

وَكَأۡسٗا دِهَاقٗا

Da kofin (giya) cikakke



Surah: Suratun Naba’i

Ayah : 35

لَّا يَسۡمَعُونَ فِيهَا لَغۡوٗا وَلَا كِذَّـٰبٗا

Ba sa jin maganar banza a cikinta ko kuma qarya



Surah: Suratun Naba’i

Ayah : 36

جَزَآءٗ مِّن رَّبِّكَ عَطَآءً حِسَابٗا

Sakamako ne daga Ubangijinka, kyauta ce a lissafe (gwargwadon aikin kowa)



Surah: Suratul Muxaffifin

Ayah : 25

يُسۡقَوۡنَ مِن رَّحِيقٖ مَّخۡتُومٍ

Ana shayar da su giyar da aka rufe (bakin mazubinta)



Surah: Suratul Muxaffifin

Ayah : 26

خِتَٰمُهُۥ مِسۡكٞۚ وَفِي ذَٰلِكَ فَلۡيَتَنَافَسِ ٱلۡمُتَنَٰفِسُونَ

(Har) qarshensa (qamshin) almiski ne. To game da wannan kuwa lalle masu gasa su yi gasa