Surah: Suratus Saffat

Ayah : 46

بَيۡضَآءَ لَذَّةٖ لِّلشَّـٰرِبِينَ

Fara fat, ga kuma daxi ga masu sha



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 47

لَا فِيهَا غَوۡلٞ وَلَا هُمۡ عَنۡهَا يُنزَفُونَ

Babu sa ciwon kai a gare ta, kuma ba za a bugar da su da ita ba



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 48

وَعِندَهُمۡ قَٰصِرَٰتُ ٱلطَّرۡفِ عِينٞ

A wurinsu kuma akwai mataye masu taqaita kallonsu ga mazajensu, masu qwala-qwalan ido



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 49

كَأَنَّهُنَّ بَيۡضٞ مَّكۡنُونٞ

Kai ka ce su wani qwai ne a cikin kwasfa



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 71

يُطَافُ عَلَيۡهِم بِصِحَافٖ مِّن ذَهَبٖ وَأَكۡوَابٖۖ وَفِيهَا مَا تَشۡتَهِيهِ ٱلۡأَنفُسُ وَتَلَذُّ ٱلۡأَعۡيُنُۖ وَأَنتُمۡ فِيهَا خَٰلِدُونَ

Ana zagayawa tsakaninsu da akusa na zinari da kofuna; a cikinta kuma akwai (duk) abin da rayuka suke sha’awa, idanuwa kuma suke jin daxin (ganinsu); ku kuma a cikinta madawwama ne



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 72

وَتِلۡكَ ٱلۡجَنَّةُ ٱلَّتِيٓ أُورِثۡتُمُوهَا بِمَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

Waccan kuma ita ce Aljannar da aka gadar muku ita saboda abin da kuka kasance kuma aikatawa



Surah: Suratuz Zukhruf 

Ayah : 73

لَكُمۡ فِيهَا فَٰكِهَةٞ كَثِيرَةٞ مِّنۡهَا تَأۡكُلُونَ

A cikinta kuna da `ya`yan itatuwa na marmari masu yawa, daga gare su kuma za ku riqa ci



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 51

إِنَّ ٱلۡمُتَّقِينَ فِي مَقَامٍ أَمِينٖ

Lalle masu taqawa suna cikin wani amintaccen wuri



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 52

فِي جَنَّـٰتٖ وَعُيُونٖ

Cikin lambuna da idanuwan ruwa



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 53

يَلۡبَسُونَ مِن سُندُسٖ وَإِسۡتَبۡرَقٖ مُّتَقَٰبِلِينَ

Suna saye da tufafi na alharini mai shara-shara da mai kauri suna fuskantar juna



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 54

كَذَٰلِكَ وَزَوَّجۡنَٰهُم بِحُورٍ عِينٖ

Kamar haka ne, Muka kuma aura musu (‘yan matan) Hurul-Ini



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 55

يَدۡعُونَ فِيهَا بِكُلِّ فَٰكِهَةٍ ءَامِنِينَ

A cikinta (Aljannar) suna kiran a kawo musu duk wani kayan marmari, suna cikin aminci



Surah: Suratu Muhammad

Ayah : 15

مَّثَلُ ٱلۡجَنَّةِ ٱلَّتِي وُعِدَ ٱلۡمُتَّقُونَۖ فِيهَآ أَنۡهَٰرٞ مِّن مَّآءٍ غَيۡرِ ءَاسِنٖ وَأَنۡهَٰرٞ مِّن لَّبَنٖ لَّمۡ يَتَغَيَّرۡ طَعۡمُهُۥ وَأَنۡهَٰرٞ مِّنۡ خَمۡرٖ لَّذَّةٖ لِّلشَّـٰرِبِينَ وَأَنۡهَٰرٞ مِّنۡ عَسَلٖ مُّصَفّٗىۖ وَلَهُمۡ فِيهَا مِن كُلِّ ٱلثَّمَرَٰتِ وَمَغۡفِرَةٞ مِّن رَّبِّهِمۡۖ كَمَنۡ هُوَ خَٰلِدٞ فِي ٱلنَّارِ وَسُقُواْ مَآءً حَمِيمٗا فَقَطَّعَ أَمۡعَآءَهُمۡ

Kwatankwacin Aljannar da aka yi wa masu taqawa alqawari da ita shi ne, a cikinta akwai qoramu na ruwa ba gurvatacce ba, da kuma qoramu na nono da xanxanonsa bai canja ba, da qoramu na giya masu daxi ga mashaya, da qoramu na tatacciyar zuma, kuma suna da kowane irin nau’i na ‘ya’yan itace da kuma gafara daga Ubangijinsu. Yanzu (masu waxannan sa yi) daidai da waxanda za su dawwama a cikin wuta a kuma shayar da su ruwa tafasasshe, sai ya yayyanke kayan cikinsu?



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 46

وَلِمَنۡ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ جَنَّتَانِ

Duk wanda kuwa ya ji tsoron tsayuwa (gaban) Ubangijinsa yana da Aljanna biyu



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 47

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 48

ذَوَاتَآ أَفۡنَانٖ

Ma’abota rassan bishiyoyi



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 49

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 50

فِيهِمَا عَيۡنَانِ تَجۡرِيَانِ

A cikinsu akwai idanuwa (na ruwa) guda biyu masu gudana



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 51

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 52

فِيهِمَا مِن كُلِّ فَٰكِهَةٖ زَوۡجَانِ

A cikinsu akwai (dangi) biyu na kowane abin marmari



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 53

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 54

مُتَّكِـِٔينَ عَلَىٰ فُرُشِۭ بَطَآئِنُهَا مِنۡ إِسۡتَبۡرَقٖۚ وَجَنَى ٱلۡجَنَّتَيۡنِ دَانٖ

Suna kishingixe a kan shimfixu da shafin cikinsu na kakkauran alhariri ne. Kuma ‘ya’yan bishiyoyin Aljannatai biyun kusa suke (da kowa)



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 55

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 56

فِيهِنَّ قَٰصِرَٰتُ ٱلطَّرۡفِ لَمۡ يَطۡمِثۡهُنَّ إِنسٞ قَبۡلَهُمۡ وَلَا جَآنّٞ

A cikinsu akwai (mata) masu taqaita kallo (ga mazajensu, waxanda) wani mutum ko aljan bai tava shafar su ba a gabaninsu



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 57

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 58

كَأَنَّهُنَّ ٱلۡيَاقُوتُ وَٱلۡمَرۡجَانُ

Kai ka ce su yaqutu ne da murjani



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 59

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 60

هَلۡ جَزَآءُ ٱلۡإِحۡسَٰنِ إِلَّا ٱلۡإِحۡسَٰنُ

Shin akwai wani sakamako na kyautatawa in ba kyautatawa ba?



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 61

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Surah: Suratur Rahman

Ayah : 62

وَمِن دُونِهِمَا جَنَّتَانِ

A qasa da su kuma akwai wasu aljannatai guda biyu