Surah: Suratul Qasas

Ayah : 29

۞فَلَمَّا قَضَىٰ مُوسَى ٱلۡأَجَلَ وَسَارَ بِأَهۡلِهِۦٓ ءَانَسَ مِن جَانِبِ ٱلطُّورِ نَارٗاۖ قَالَ لِأَهۡلِهِ ٱمۡكُثُوٓاْ إِنِّيٓ ءَانَسۡتُ نَارٗا لَّعَلِّيٓ ءَاتِيكُم مِّنۡهَا بِخَبَرٍ أَوۡ جَذۡوَةٖ مِّنَ ٱلنَّارِ لَعَلَّكُمۡ تَصۡطَلُونَ

To yayin da Musa ya cika lokacinsa ya kuma tafi da iyalinsa, sai ya hango wuta daga gefen (dutsen) Xuri, ya ce: “Lalle na hango wuta, (zan je don) in zo muku da labari daga wurinta ko kuma (in samo muku) wani garwashi na wutar don ku ji xumi.”



Surah: Suratul Qasas

Ayah : 30

فَلَمَّآ أَتَىٰهَا نُودِيَ مِن شَٰطِيِٕ ٱلۡوَادِ ٱلۡأَيۡمَنِ فِي ٱلۡبُقۡعَةِ ٱلۡمُبَٰرَكَةِ مِنَ ٱلشَّجَرَةِ أَن يَٰمُوسَىٰٓ إِنِّيٓ أَنَا ٱللَّهُ رَبُّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

To lokacin da ya zo wurinta sai aka yi kira daga gefen kwari na damarsa a wani wuri mai albarka na bishiya, cewa: “Ya Musa, lalle Ni ne Allah Ubangijin talikai!



Surah: Suratul Qasas

Ayah : 31

وَأَنۡ أَلۡقِ عَصَاكَۚ فَلَمَّا رَءَاهَا تَهۡتَزُّ كَأَنَّهَا جَآنّٞ وَلَّىٰ مُدۡبِرٗا وَلَمۡ يُعَقِّبۡۚ يَٰمُوسَىٰٓ أَقۡبِلۡ وَلَا تَخَفۡۖ إِنَّكَ مِنَ ٱلۡأٓمِنِينَ

“Kuma ka jefar da sandarka;” to lokacin da ya gan ta tana girgiza kamar maciji sai ya ba da baya a guje, bai ko waiwaya ba. (Aka ce da shi): “Ya Musa dawo, kada ka ji tsoro; lalle kai kana cikin amintattu



Surah: Suratul Qasas

Ayah : 32

ٱسۡلُكۡ يَدَكَ فِي جَيۡبِكَ تَخۡرُجۡ بَيۡضَآءَ مِنۡ غَيۡرِ سُوٓءٖ وَٱضۡمُمۡ إِلَيۡكَ جَنَاحَكَ مِنَ ٱلرَّهۡبِۖ فَذَٰنِكَ بُرۡهَٰنَانِ مِن رَّبِّكَ إِلَىٰ فِرۡعَوۡنَ وَمَلَإِيْهِۦٓۚ إِنَّهُمۡ كَانُواْ قَوۡمٗا فَٰسِقِينَ

“Ka sanya hannunka a cikin wuyan rigarka, zai fito fari fat ba tare da wata cuta ba, kuma ka haxe hannunka da kwivinka saboda tsoron (farinta); to biyu xin nan hujjoji ne daga Ubangijinka zuwa ga Fir’auna da mutanensa. Lalle su sun kasance mutane ne fasiqai.”



Surah: Suratul Qasas

Ayah : 33

قَالَ رَبِّ إِنِّي قَتَلۡتُ مِنۡهُمۡ نَفۡسٗا فَأَخَافُ أَن يَقۡتُلُونِ

(Musa) ya ce: “Ya Ubangijina, lalle ni na kashe musu wani mutum, to ina tsoron su kashe ni



Surah: Suratul Qasas

Ayah : 34

وَأَخِي هَٰرُونُ هُوَ أَفۡصَحُ مِنِّي لِسَانٗا فَأَرۡسِلۡهُ مَعِيَ رِدۡءٗا يُصَدِّقُنِيٓۖ إِنِّيٓ أَخَافُ أَن يُكَذِّبُونِ

“Kuma xan’uwana Haruna shi ya fi ni fasahar harshe, sai Ka aike shi tare da ni ya zama mataimakina yana gaskata ni; lalle ni ina jin tsoron su qaryata ni.”



Surah: Suratul Qasas

Ayah : 35

قَالَ سَنَشُدُّ عَضُدَكَ بِأَخِيكَ وَنَجۡعَلُ لَكُمَا سُلۡطَٰنٗا فَلَا يَصِلُونَ إِلَيۡكُمَا بِـَٔايَٰتِنَآۚ أَنتُمَا وَمَنِ ٱتَّبَعَكُمَا ٱلۡغَٰلِبُونَ

(Sai Allah) Ya ce: “Za Mu qarfafa dantsenka da xan’uwanka kuma za Mu sanya muku wata hujja, don haka ba za su isa gare ku (da cuta) ba. Da ayoyinmu - ku da waxanda suka bi ku - ku ne masu yin galaba.”



Surah: Suratul Qasas

Ayah : 36

فَلَمَّا جَآءَهُم مُّوسَىٰ بِـَٔايَٰتِنَا بَيِّنَٰتٖ قَالُواْ مَا هَٰذَآ إِلَّا سِحۡرٞ مُّفۡتَرٗى وَمَا سَمِعۡنَا بِهَٰذَا فِيٓ ءَابَآئِنَا ٱلۡأَوَّلِينَ

To lokacin da Musa ya zo musu da ayoyinmu mabayyana sai suka ce: “Ai wannan ba wani abu ba ne face qagaggen sihiri, mu kuma ba mu tava jin wannan ba a wurin iyayenmu na farko.”



Surah: Suratul Qasas

Ayah : 37

وَقَالَ مُوسَىٰ رَبِّيٓ أَعۡلَمُ بِمَن جَآءَ بِٱلۡهُدَىٰ مِنۡ عِندِهِۦ وَمَن تَكُونُ لَهُۥ عَٰقِبَةُ ٱلدَّارِۚ إِنَّهُۥ لَا يُفۡلِحُ ٱلظَّـٰلِمُونَ

Musa kuma ya ce: “Ubangijina (Shi ne) Ya fi sanin wanda ya zo da shiriya daga wurinsa, da kuma wanda kyakkyawan qarshe zai kasance a gare shi; lalle yadda al’amarin yake, azzalumai ba sa rabauta.”



Surah: Suratul Qasas

Ayah : 38

وَقَالَ فِرۡعَوۡنُ يَـٰٓأَيُّهَا ٱلۡمَلَأُ مَا عَلِمۡتُ لَكُم مِّنۡ إِلَٰهٍ غَيۡرِي فَأَوۡقِدۡ لِي يَٰهَٰمَٰنُ عَلَى ٱلطِّينِ فَٱجۡعَل لِّي صَرۡحٗا لَّعَلِّيٓ أَطَّلِعُ إِلَىٰٓ إِلَٰهِ مُوسَىٰ وَإِنِّي لَأَظُنُّهُۥ مِنَ ٱلۡكَٰذِبِينَ

Fir’auna kuma ya ce: “Ya ku manyan gari, ban san kuna da wani abin bauta ba in ba ni ba, kai ko Hamana, shirya min qonannen tavo sannan ka yi min dogon gini don in hango abin bautar Musa, lalle ni ina tsammanin cewa shi yana cikin maqaryata.”



Surah: Suratul Qasas

Ayah : 39

وَٱسۡتَكۡبَرَ هُوَ وَجُنُودُهُۥ فِي ٱلۡأَرۡضِ بِغَيۡرِ ٱلۡحَقِّ وَظَنُّوٓاْ أَنَّهُمۡ إِلَيۡنَا لَا يُرۡجَعُونَ

Ya kuma yi girman kai shi da rundunoninsa a qasar (Masar) ba da gaskiya ba, suka kuma yi tsammanin cewa su ba za a komar da su zuwa gare Mu ba



Surah: Suratul Qasas

Ayah : 40

فَأَخَذۡنَٰهُ وَجُنُودَهُۥ فَنَبَذۡنَٰهُمۡ فِي ٱلۡيَمِّۖ فَٱنظُرۡ كَيۡفَ كَانَ عَٰقِبَةُ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Sai Muka kama shi da rundunoninsa, sannan Muka watsa su a cikin kogi; to ka duba ka ga yadda qarshen azzalumai ya kasance



Surah: Suratul Qasas

Ayah : 41

وَجَعَلۡنَٰهُمۡ أَئِمَّةٗ يَدۡعُونَ إِلَى ٱلنَّارِۖ وَيَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ لَا يُنصَرُونَ

Muka kuma mayar da su shugabanni masu kira zuwa ga wuta; ranar alqiyama kuma ba za a taimake su ba



Surah: Suratul Qasas

Ayah : 42

وَأَتۡبَعۡنَٰهُمۡ فِي هَٰذِهِ ٱلدُّنۡيَا لَعۡنَةٗۖ وَيَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ هُم مِّنَ ٱلۡمَقۡبُوحِينَ

Muka kuma bi su da la’anta a wannan duniyar; ranar alqiyama kuma suna cikin waxanda za a jefa cikin mummunan hali



Surah: Suratul Qasas

Ayah : 43

وَلَقَدۡ ءَاتَيۡنَا مُوسَى ٱلۡكِتَٰبَ مِنۢ بَعۡدِ مَآ أَهۡلَكۡنَا ٱلۡقُرُونَ ٱلۡأُولَىٰ بَصَآئِرَ لِلنَّاسِ وَهُدٗى وَرَحۡمَةٗ لَّعَلَّهُمۡ يَتَذَكَّرُونَ

Haqiqa kuma Mun bai wa Musa littafin (Attaura) bayan Mun hallaka al’ummu na farko don izina ga mutane da shiriya da rahama ko sa wa’azantu



Surah: Suratul Ankabut

Ayah : 39

وَقَٰرُونَ وَفِرۡعَوۡنَ وَهَٰمَٰنَۖ وَلَقَدۡ جَآءَهُم مُّوسَىٰ بِٱلۡبَيِّنَٰتِ فَٱسۡتَكۡبَرُواْ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَمَا كَانُواْ سَٰبِقِينَ

Kuma (Mun hallaka) Qaruna da Fir’auna da Hamana; haqiqa kuma Musa ya zo musu da hujjoji bayyanannu, sai suka yi girman kai a bayan qasa, kuma ba su kasance masu guje wa (azaba) ba



Surah: Suratus Sajda

Ayah : 23

وَلَقَدۡ ءَاتَيۡنَا مُوسَى ٱلۡكِتَٰبَ فَلَا تَكُن فِي مِرۡيَةٖ مِّن لِّقَآئِهِۦۖ وَجَعَلۡنَٰهُ هُدٗى لِّبَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ

Haqiqa kuma Mu Mun bai wa Musa Littafi, to kada ka kasance (kai Manzo) cikin kokwanto na saduwa da shi (Musan)[1]. Kuma Mun sanya shi ya zamanto shiriya ga Banu-Isra’ila


1- Watau haxuwar Annabi Muhammad () da Annabi Musa () a daren mi’iraji.


Surah: Suratul Ahzab

Ayah : 69

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لَا تَكُونُواْ كَٱلَّذِينَ ءَاذَوۡاْ مُوسَىٰ فَبَرَّأَهُ ٱللَّهُ مِمَّا قَالُواْۚ وَكَانَ عِندَ ٱللَّهِ وَجِيهٗا

Ya ku waxanda suka yi imani, kada ku zamanto kamar waxanda suka cuci Musa sai Allah Ya wanke shi daga abin da suka faxa (a kansa). Ya kuma kasance mai alfarma ne a wurin Allah



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 114

وَلَقَدۡ مَنَنَّا عَلَىٰ مُوسَىٰ وَهَٰرُونَ

Haqiqa kuma Mun yi ni’ima ga Musa da Haruna



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 115

وَنَجَّيۡنَٰهُمَا وَقَوۡمَهُمَا مِنَ ٱلۡكَرۡبِ ٱلۡعَظِيمِ

Muka kuma tserar da su da mutanensu daga babban baqin ciki



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 116

وَنَصَرۡنَٰهُمۡ فَكَانُواْ هُمُ ٱلۡغَٰلِبِينَ

Muka kuma taimake su, sai suka kasance su ne masu rinjaye



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 117

وَءَاتَيۡنَٰهُمَا ٱلۡكِتَٰبَ ٱلۡمُسۡتَبِينَ

Muka kuma ba su Littafi mabayyani (Attaura)



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 118

وَهَدَيۡنَٰهُمَا ٱلصِّرَٰطَ ٱلۡمُسۡتَقِيمَ

Muka kuma shiryar da su hanya madaidaiciya



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 119

وَتَرَكۡنَا عَلَيۡهِمَا فِي ٱلۡأٓخِرِينَ

Muka kuma bar (kyakkyawan yabo) a gare su ga ‘yan baya



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 120

سَلَٰمٌ عَلَىٰ مُوسَىٰ وَهَٰرُونَ

Aminci ya tabbata ga Musa da Haruna



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 121

إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Lalle Mu kamar haka Muke saka wa masu kyautatawa



Surah: Suratus Saffat

Ayah : 122

إِنَّهُمَا مِنۡ عِبَادِنَا ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

Lalle suna daga cikin bayinmu muminai



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 23

وَلَقَدۡ أَرۡسَلۡنَا مُوسَىٰ بِـَٔايَٰتِنَا وَسُلۡطَٰنٖ مُّبِينٍ

Haqiqa kuma Mun aiko Musa da ayoyinmu da kuma hujja mabayyaniya



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 24

إِلَىٰ فِرۡعَوۡنَ وَهَٰمَٰنَ وَقَٰرُونَ فَقَالُواْ سَٰحِرٞ كَذَّابٞ

Zuwa ga Fir’auna da Hamana da Qaruna, sai suka ce shi mai sihiri ne, babban maqaryaci



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 25

فَلَمَّا جَآءَهُم بِٱلۡحَقِّ مِنۡ عِندِنَا قَالُواْ ٱقۡتُلُوٓاْ أَبۡنَآءَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ مَعَهُۥ وَٱسۡتَحۡيُواْ نِسَآءَهُمۡۚ وَمَا كَيۡدُ ٱلۡكَٰفِرِينَ إِلَّا فِي ضَلَٰلٖ

To lokacin da ya zo musu da gaskiya daga wajenmu sai suka ce: “Ku kashe `ya`yan waxanda suka yi imani tare da shi, ku kuma qyale matansu da rai.” Makircin kafirai bai zama ba sai a lalace