Surah: Suratul Insan

Ayah : 28

نَّحۡنُ خَلَقۡنَٰهُمۡ وَشَدَدۡنَآ أَسۡرَهُمۡۖ وَإِذَا شِئۡنَا بَدَّلۡنَآ أَمۡثَٰلَهُمۡ تَبۡدِيلًا

Mu Muka halicce su Muka kuma qarfafa gavovinsu; idan kuwa Muka ga dama sai Mu musanya irinsu (kyakkyawar) musanyawa



Surah: Suratul Insan

Ayah : 29

إِنَّ هَٰذِهِۦ تَذۡكِرَةٞۖ فَمَن شَآءَ ٱتَّخَذَ إِلَىٰ رَبِّهِۦ سَبِيلٗا

Lalle wannan wa’azi ne; saboda haka wanda ya ga dama sai ya riqi hanya zuwa ga Ubangijinsa



Surah: Suratul Insan

Ayah : 30

وَمَا تَشَآءُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُۚ إِنَّ ٱللَّهَ كَانَ عَلِيمًا حَكِيمٗا

Kuma ba ganin damarku ba ce sai abin da Allah ya ga dama. Lalle Allah Ya kasance Masani, Mai hikima



Surah: Suratul Insan

Ayah : 31

يُدۡخِلُ مَن يَشَآءُ فِي رَحۡمَتِهِۦۚ وَٱلظَّـٰلِمِينَ أَعَدَّ لَهُمۡ عَذَابًا أَلِيمَۢا

Yana shigar da wanda Ya ga dama cikin rahamarsa. Azzalumai kuwa Ya tanadar musu azaba mai raxaxi



Surah: Suratu Abasa

Ayah : 22

ثُمَّ إِذَا شَآءَ أَنشَرَهُۥ

Sannan in Ya ga dama Ya tashe shi



Surah: Suratut Takwir

Ayah : 29

وَمَا تَشَآءُونَ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُ رَبُّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Ku kuma ba za ku iya ganin dama ba sai Allah Ubangijin talikai Ya ga dama



Surah: Suratul Infixar

Ayah : 8

فِيٓ أَيِّ صُورَةٖ مَّا شَآءَ رَكَّبَكَ

Ya harhaxa ka cikin irin surar da Ya ga dama?



Surah: Suratul Buruj

Ayah : 16

فَعَّالٞ لِّمَا يُرِيدُ

Mai aikata abin da Yake nufi