Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 180

وَمَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ أَجۡرٍۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

“Kuma ba na tambayar ku wani lada game da shi (isar da manzancin); ladana yana wajen Ubangijin talikai kawai



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 181

۞أَوۡفُواْ ٱلۡكَيۡلَ وَلَا تَكُونُواْ مِنَ ٱلۡمُخۡسِرِينَ

“Ku cika mudu kada kuma ku zamanto daga masu tauye (shi)



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 182

وَزِنُواْ بِٱلۡقِسۡطَاسِ ٱلۡمُسۡتَقِيمِ

“Kuma ku riqa yin awon nauyi da ma’auni na adalci



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 183

وَلَا تَبۡخَسُواْ ٱلنَّاسَ أَشۡيَآءَهُمۡ وَلَا تَعۡثَوۡاْ فِي ٱلۡأَرۡضِ مُفۡسِدِينَ

“Kada kuma ku tauye wa mutane kayayyakinsu, kuma kada ku yawaita varna a bayan qasa



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 184

وَٱتَّقُواْ ٱلَّذِي خَلَقَكُمۡ وَٱلۡجِبِلَّةَ ٱلۡأَوَّلِينَ

“Kuma ku kiyaye dokokin (Allah) wanda Ya halicce ku da kuma al’ummu na farko.”



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 185

قَالُوٓاْ إِنَّمَآ أَنتَ مِنَ ٱلۡمُسَحَّرِينَ

Suka ce: “Kai dai kana daga waxanda aka sihirce ne kawai



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 186

وَمَآ أَنتَ إِلَّا بَشَرٞ مِّثۡلُنَا وَإِن نَّظُنُّكَ لَمِنَ ٱلۡكَٰذِبِينَ

“Kuma kai ba kowa ba ne sai mutum kamarmu, kuma ma lalle muna zaton kana daga maqaryata!



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 187

فَأَسۡقِطۡ عَلَيۡنَا كِسَفٗا مِّنَ ٱلسَّمَآءِ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّـٰدِقِينَ

“Sai ka jeho mana da yankuna (na azaba) daga sama in ka kasance daga masu gaskiya!”



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 188

قَالَ رَبِّيٓ أَعۡلَمُ بِمَا تَعۡمَلُونَ

(Shu’aibu) Ya ce: “Ubangijina Ya fi kowa sanin abin da kuke aikatawa.”



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 189

فَكَذَّبُوهُ فَأَخَذَهُمۡ عَذَابُ يَوۡمِ ٱلظُّلَّةِۚ إِنَّهُۥ كَانَ عَذَابَ يَوۡمٍ عَظِيمٍ

Sai suka qaryata shi, sannan sai azabar yinin girgije (na wuta) ta kama su. Lalle ta kasance azabar wani yini ne mai girma



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 190

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ

Lalle a game da wannan tabbas akwai aya; sai dai kuma yawancinsu ba su kasance muminai ba



Surah: Suratul Qasas

Ayah : 22

وَلَمَّا تَوَجَّهَ تِلۡقَآءَ مَدۡيَنَ قَالَ عَسَىٰ رَبِّيٓ أَن يَهۡدِيَنِي سَوَآءَ ٱلسَّبِيلِ

Yayin da kuma ya sa gaba ya nufi wajen (birnin) Madyana, sai ya ce: “Ina fatan Ubangijina Ya shiryar da ni hanyar da ta fi dacewa.”



Surah: Suratul Qasas

Ayah : 23

وَلَمَّا وَرَدَ مَآءَ مَدۡيَنَ وَجَدَ عَلَيۡهِ أُمَّةٗ مِّنَ ٱلنَّاسِ يَسۡقُونَ وَوَجَدَ مِن دُونِهِمُ ٱمۡرَأَتَيۡنِ تَذُودَانِۖ قَالَ مَا خَطۡبُكُمَاۖ قَالَتَا لَا نَسۡقِي حَتَّىٰ يُصۡدِرَ ٱلرِّعَآءُۖ وَأَبُونَا شَيۡخٞ كَبِيرٞ

Lokacin da kuma ya iso mashayar ruwa ta Madyana sai ya sami wani gungun mutane suna shayar (da dabbobinsu), ya kuma sami wasu mata su biyu a gefensu suna kare (dabbobinsu); sai ya ce (da su): “Me ya same ku ne?” Sai suka ce: “Mu ai ba ma shayarwa har sai duk makiyaya sun watse, kuma mahaifinmu tsoho ne tukub.”



Surah: Suratul Ankabut

Ayah : 36

وَإِلَىٰ مَدۡيَنَ أَخَاهُمۡ شُعَيۡبٗا فَقَالَ يَٰقَوۡمِ ٱعۡبُدُواْ ٱللَّهَ وَٱرۡجُواْ ٱلۡيَوۡمَ ٱلۡأٓخِرَ وَلَا تَعۡثَوۡاْ فِي ٱلۡأَرۡضِ مُفۡسِدِينَ

Mun kuma (aika wa mutanen) Madyana xan’uwansu Shu’aibu, sai ya ce: “Ya ku mutanena, ku bauta wa Allah, kuma ku yi fatan (kyakkyawan samakon) ranar lahira, kada kuma ku riqa yaxa varna a bayan qasa.”



Surah: Suratul Ankabut

Ayah : 37

فَكَذَّبُوهُ فَأَخَذَتۡهُمُ ٱلرَّجۡفَةُ فَأَصۡبَحُواْ فِي دَارِهِمۡ جَٰثِمِينَ

Sai suka qaryata shi, sai girgizar qasa ta kama su, suka wayi gari duddurqushe (matattu) cikin gidajensu



Surah: Suratu Sad

Ayah : 13

وَثَمُودُ وَقَوۡمُ لُوطٖ وَأَصۡحَٰبُ لۡـَٔيۡكَةِۚ أُوْلَـٰٓئِكَ ٱلۡأَحۡزَابُ

Da kuma Samudawa da mutanen Luxu da mutanen Sarqaqiya[1]. Waxannan su ne al’ummun


1- Su ne mutanen Annabi Shu’aibu ().


Surah: Suratu Qaf 

Ayah : 14

وَأَصۡحَٰبُ ٱلۡأَيۡكَةِ وَقَوۡمُ تُبَّعٖۚ كُلّٞ كَذَّبَ ٱلرُّسُلَ فَحَقَّ وَعِيدِ

Da kuma ma’abota surquqi[1] da mutanen Tubba’u[2]. Kowannensu ya qaryata manzanni, sai azabata ta tabbata (a kansu)


1- Watau mutanen Annabi Shu’aibu ().


2- Tubba’u shi ne sarkin Yaman.1- Watau mutanen Annabi Shu’aibu ().


2- Tubba’u shi ne sarkin Yaman.