Surah: Suratul An’am

Ayah : 86

وَإِسۡمَٰعِيلَ وَٱلۡيَسَعَ وَيُونُسَ وَلُوطٗاۚ وَكُلّٗا فَضَّلۡنَا عَلَى ٱلۡعَٰلَمِينَ

Da Isma’ilu da Alyasa’u da Yunusu da Luxu. Kowanne daga cikinsu kuma Mun fifita shi a kan (sauran) talikai



Surah: Suratul A’araf

Ayah : 80

وَلُوطًا إِذۡ قَالَ لِقَوۡمِهِۦٓ أَتَأۡتُونَ ٱلۡفَٰحِشَةَ مَا سَبَقَكُم بِهَا مِنۡ أَحَدٖ مِّنَ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Kuma ka tuna Luxu lokacin da ya ce wa mutanensa: “Yanzu kwa riqa aikata mummunan aikin da babu wani mahaluqi a duniya da ya tava aikata irinsa gabaninku?



Surah: Suratul A’araf

Ayah : 81

إِنَّكُمۡ لَتَأۡتُونَ ٱلرِّجَالَ شَهۡوَةٗ مِّن دُونِ ٱلنِّسَآءِۚ بَلۡ أَنتُمۡ قَوۡمٞ مُّسۡرِفُونَ

“Lalle ku kuna zaike wa maza don sha’awa maimakon mata. A’a, ku mutane ne mavarnata.”



Surah: Suratul A’araf

Ayah : 82

وَمَا كَانَ جَوَابَ قَوۡمِهِۦٓ إِلَّآ أَن قَالُوٓاْ أَخۡرِجُوهُم مِّن قَرۡيَتِكُمۡۖ إِنَّهُمۡ أُنَاسٞ يَتَطَهَّرُونَ

Ba kuwa amsar da ta fito daga bakin mutanensa sai kawai suka ce: “Ku fitar da su daga garinku; lalle su mutane ne da suke nuna su masu tsarki ne.”



Surah: Suratul A’araf

Ayah : 83

فَأَنجَيۡنَٰهُ وَأَهۡلَهُۥٓ إِلَّا ٱمۡرَأَتَهُۥ كَانَتۡ مِنَ ٱلۡغَٰبِرِينَ

Sai Muka tserar da shi da iyalansa, in ban da matarsa, ita ta kasance cikin waxanda suka rage (a cikin azaba)



Surah: Suratul A’araf

Ayah : 84

وَأَمۡطَرۡنَا عَلَيۡهِم مَّطَرٗاۖ فَٱنظُرۡ كَيۡفَ كَانَ عَٰقِبَةُ ٱلۡمُجۡرِمِينَ

Sai Muka yi musu ruwan azaba; to duba ka ga yaya qarshen masu babban laifi ya kasance?



Surah: Suratu Hud

Ayah : 74

فَلَمَّا ذَهَبَ عَنۡ إِبۡرَٰهِيمَ ٱلرَّوۡعُ وَجَآءَتۡهُ ٱلۡبُشۡرَىٰ يُجَٰدِلُنَا فِي قَوۡمِ لُوطٍ

To lokacin da tsoro ya rabu da Ibrahimu, kuma albishir ya zo masa, (sai ya zama) yana muhawara da Mu[1] game da mutanen Luxu


1- Watau yana muhawara da mala’ikun Allah.


Surah: Suratu Hud

Ayah : 75

إِنَّ إِبۡرَٰهِيمَ لَحَلِيمٌ أَوَّـٰهٞ مُّنِيبٞ

Lalle Ibrahimu tabbas mai haquri ne mai yawan ambato Allah mai yawan komawa gare Shi



Surah: Suratu Hud

Ayah : 76

يَـٰٓإِبۡرَٰهِيمُ أَعۡرِضۡ عَنۡ هَٰذَآۖ إِنَّهُۥ قَدۡ جَآءَ أَمۡرُ رَبِّكَۖ وَإِنَّهُمۡ ءَاتِيهِمۡ عَذَابٌ غَيۡرُ مَرۡدُودٖ

Ya kai Ibrahimu, ka kau da kai daga wannan. Lalle umarnin Ubangijinka ya zo; lalle kuwa azaba wadda ba mai kawar da ita za ta zo musu



Surah: Suratu Hud

Ayah : 77

وَلَمَّا جَآءَتۡ رُسُلُنَا لُوطٗا سِيٓءَ بِهِمۡ وَضَاقَ بِهِمۡ ذَرۡعٗا وَقَالَ هَٰذَا يَوۡمٌ عَصِيبٞ

Lokacin kuma da manzanninmu suka zo wa Luxu, sai aka vata masa rai saboda su, kuma zuciyarsa ta yi qunci saboda su[1], ya kuma ce: “Wannan rana ce mawuyaciya!”


1- Watau ya shiga damuwa domin ya san mutanensa ba za su qyale su ba.


Surah: Suratu Hud

Ayah : 78

وَجَآءَهُۥ قَوۡمُهُۥ يُهۡرَعُونَ إِلَيۡهِ وَمِن قَبۡلُ كَانُواْ يَعۡمَلُونَ ٱلسَّيِّـَٔاتِۚ قَالَ يَٰقَوۡمِ هَـٰٓؤُلَآءِ بَنَاتِي هُنَّ أَطۡهَرُ لَكُمۡۖ فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَلَا تُخۡزُونِ فِي ضَيۡفِيٓۖ أَلَيۡسَ مِنكُمۡ رَجُلٞ رَّشِيدٞ

Mutanensa kuwa suka zo masa suna gaggawa, da ma ko can sun zamanto suna yin munanan ayyuka[1]. Ya ce: “Ya ku mutanena, ga ‘ya’yana nan mata, su suka fi tsarkaka a gare ku (ba maza ba), to ku kiyayi Allah, kada ku kunyata ni game da baqina. Yanzu a cikinku ba wani mutum mai hankali?”


1- Watau neman maza da yi musu fyaxe.


Surah: Suratu Hud

Ayah : 79

قَالُواْ لَقَدۡ عَلِمۡتَ مَا لَنَا فِي بَنَاتِكَ مِنۡ حَقّٖ وَإِنَّكَ لَتَعۡلَمُ مَا نُرِيدُ

Suka ce: “Haqiqa ka sani ba mu da wani haqqi (na sha’awa) ga ‘ya’yanka mata, lalle kuma tabbas ka san abin da muke nufi!”



Surah: Suratu Hud

Ayah : 80

قَالَ لَوۡ أَنَّ لِي بِكُمۡ قُوَّةً أَوۡ ءَاوِيٓ إِلَىٰ رُكۡنٖ شَدِيدٖ

Ya ce: “Ina ma ina da qarfi da zan hana ku, ko kuwa ina da wata qaqqarfar majingina (da zan dogara da ita)?”



Surah: Suratu Hud

Ayah : 81

قَالُواْ يَٰلُوطُ إِنَّا رُسُلُ رَبِّكَ لَن يَصِلُوٓاْ إِلَيۡكَۖ فَأَسۡرِ بِأَهۡلِكَ بِقِطۡعٖ مِّنَ ٱلَّيۡلِ وَلَا يَلۡتَفِتۡ مِنكُمۡ أَحَدٌ إِلَّا ٱمۡرَأَتَكَۖ إِنَّهُۥ مُصِيبُهَا مَآ أَصَابَهُمۡۚ إِنَّ مَوۡعِدَهُمُ ٱلصُّبۡحُۚ أَلَيۡسَ ٱلصُّبۡحُ بِقَرِيبٖ

(Baqin) suka ce: “Ya Luxu, lalle mu manzannin Ubangijinka ne; ba za su iya isowa gare ka ba; don haka sai ka tafi kai da iyalanka cikin wani yanki na dare, kada kuwa xaya daga cikinku ya waiwaya, sai matarka kawai. Lalle ita kam abin da ya same su zai same ta. Lalle lokacin da aka xebar musu asuba ne kawai; shin asuba ba kurkusa take ba?



Surah: Suratu Hud

Ayah : 82

فَلَمَّا جَآءَ أَمۡرُنَا جَعَلۡنَا عَٰلِيَهَا سَافِلَهَا وَأَمۡطَرۡنَا عَلَيۡهَا حِجَارَةٗ مِّن سِجِّيلٖ مَّنضُودٖ

To lokacin da umarninmu ya zo sai Muka mai da samanta qasa (wato alqaryar), Muka kuma yi mata ruwan duwatsu irin na soyayyen yumvu wasu bayan wasu



Surah: Suratu Hud

Ayah : 83

مُّسَوَّمَةً عِندَ رَبِّكَۖ وَمَا هِيَ مِنَ ٱلظَّـٰلِمِينَ بِبَعِيدٖ

Waxanda aka yi wa alama daga Ubangijinka. Ba kuwa nesa (dutsen) yake da azzalumai ba



Surah: Suratul Hijr

Ayah : 59

إِلَّآ ءَالَ لُوطٍ إِنَّا لَمُنَجُّوهُمۡ أَجۡمَعِينَ

“In ban da iyalin Luxu, lalle tabbas za mu tserar da su baki xaya



Surah: Suratul Hijr

Ayah : 60

إِلَّا ٱمۡرَأَتَهُۥ قَدَّرۡنَآ إِنَّهَا لَمِنَ ٱلۡغَٰبِرِينَ

“Sai fa matarsa ita kam mun qaddara cewa tabbas za ta zama cikin halakakku.”



Surah: Suratul Hijr

Ayah : 61

فَلَمَّا جَآءَ ءَالَ لُوطٍ ٱلۡمُرۡسَلُونَ

To lokacin da manzannin suka zo wa iyalin Luxu



Surah: Suratul Hijr

Ayah : 62

قَالَ إِنَّكُمۡ قَوۡمٞ مُّنكَرُونَ

Ya ce: “Lalle ku wasu mutane ne da ba a san su ba.”



Surah: Suratul Hijr

Ayah : 63

قَالُواْ بَلۡ جِئۡنَٰكَ بِمَا كَانُواْ فِيهِ يَمۡتَرُونَ

Suka ce: “A’a, mu mun zo maka ne da abin da (mutanenka) suke kokwanto game da shi



Surah: Suratul Hijr

Ayah : 64

وَأَتَيۡنَٰكَ بِٱلۡحَقِّ وَإِنَّا لَصَٰدِقُونَ

“Mun kuma zo maka da dahir, lalle kuma tabbas mu masu gaskiya ne



Surah: Suratul Hijr

Ayah : 65

فَأَسۡرِ بِأَهۡلِكَ بِقِطۡعٖ مِّنَ ٱلَّيۡلِ وَٱتَّبِعۡ أَدۡبَٰرَهُمۡ وَلَا يَلۡتَفِتۡ مِنكُمۡ أَحَدٞ وَٱمۡضُواْ حَيۡثُ تُؤۡمَرُونَ

“Sai ka tafi da iyalinka cikin wani yankin dare ka kuma riqa bin su a baya, kada kuwa xaya daga cikinku ya waiwaya, kuma ku tafi inda aka umarce ku.”



Surah: Suratul Hijr

Ayah : 66

وَقَضَيۡنَآ إِلَيۡهِ ذَٰلِكَ ٱلۡأَمۡرَ أَنَّ دَابِرَ هَـٰٓؤُلَآءِ مَقۡطُوعٞ مُّصۡبِحِينَ

Muka kuwa sanar da shi abin da Muka qaddara na wannan al’amari cewa, qarshen waxannan zai yanke ne da asuba



Surah: Suratul Hijr

Ayah : 67

وَجَآءَ أَهۡلُ ٱلۡمَدِينَةِ يَسۡتَبۡشِرُونَ

Mutanen garin kuma suka zo suna murna (da ganin baqin)



Surah: Suratul Hijr

Ayah : 68

قَالَ إِنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ ضَيۡفِي فَلَا تَفۡضَحُونِ

Ya ce: “Lalle waxannan baqina ne, kada fa ku kunyata ni



Surah: Suratul Hijr

Ayah : 69

وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَلَا تُخۡزُونِ

“Kuma ku kiyaye dokokin Allah, kada ku tozarta ni[1].”


1- Annabi Luxu ya yi wannan maganar ne kafin ya san cewa waxannan baqi nasa mala’iku ne.


Surah: Suratul Hijr

Ayah : 70

قَالُوٓاْ أَوَلَمۡ نَنۡهَكَ عَنِ ٱلۡعَٰلَمِينَ

Suka ce: “Ashe ba mu hana ka (ka saukar da) mutane (baqi ba)?”



Surah: Suratul Hijr

Ayah : 71

قَالَ هَـٰٓؤُلَآءِ بَنَاتِيٓ إِن كُنتُمۡ فَٰعِلِينَ

Ya ce: “Ga ‘ya’yana nan (ku aura)[1] idan kun kasance masu aikata (haka)


1- Yana nufin matan al’ummarsa.


Surah: Suratul Hijr

Ayah : 72

لَعَمۡرُكَ إِنَّهُمۡ لَفِي سَكۡرَتِهِمۡ يَعۡمَهُونَ

“Na rantse da rayuwarka lalle su tabbas suna cikin mayensu suna ta ximuwa.”