Surah: Suratul Hijr

Ayah : 73

فَأَخَذَتۡهُمُ ٱلصَّيۡحَةُ مُشۡرِقِينَ

Sai tsawa ta auka musu lokacin hudowar rana



Surah: Suratul Hijr

Ayah : 74

فَجَعَلۡنَا عَٰلِيَهَا سَافِلَهَا وَأَمۡطَرۡنَا عَلَيۡهِمۡ حِجَارَةٗ مِّن سِجِّيلٍ

Sai Muka mayar da samanta ya koma qasa, Muka kuma yi musu ruwan duwatsu soyayyu



Surah: Suratul Hijr

Ayah : 75

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَٰتٖ لِّلۡمُتَوَسِّمِينَ

Lalle a game da wannan tabbas akwai ayoyi ga masu hangen nesa



Surah: Suratul Hijr

Ayah : 76

وَإِنَّهَا لَبِسَبِيلٖ مُّقِيمٍ

Lalle kuma ita (alqaryar) tabbas tana kan wani gwadabe ne miqaqqe



Surah: Suratul Hijr

Ayah : 77

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗ لِّلۡمُؤۡمِنِينَ

Lalle a game da wannan tabbas akwai izina ga muminai



Surah: Suratul Anbiya

Ayah : 74

وَلُوطًا ءَاتَيۡنَٰهُ حُكۡمٗا وَعِلۡمٗا وَنَجَّيۡنَٰهُ مِنَ ٱلۡقَرۡيَةِ ٱلَّتِي كَانَت تَّعۡمَلُ ٱلۡخَبَـٰٓئِثَۚ إِنَّهُمۡ كَانُواْ قَوۡمَ سَوۡءٖ فَٰسِقِينَ

Luxu kuma Muka ba shi hukunci da ilimi, Muka kuma tserar da shi daga alqaryar nan da (mutanenta) suka zamanto suna aikata munanan ayyuka. Lallai su sun kasance mutanen banza ne fasiqai



Surah: Suratul Anbiya

Ayah : 75

وَأَدۡخَلۡنَٰهُ فِي رَحۡمَتِنَآۖ إِنَّهُۥ مِنَ ٱلصَّـٰلِحِينَ

Muka kuma shigar da shi cikin rahamarmu; lallai shi yana daga (cikin) mutane na gari



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 160

كَذَّبَتۡ قَوۡمُ لُوطٍ ٱلۡمُرۡسَلِينَ

Mutanen Luxu sun qaryata manzanni



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 161

إِذۡ قَالَ لَهُمۡ أَخُوهُمۡ لُوطٌ أَلَا تَتَّقُونَ

Lokacin da xan’uwansu Luxu ya ce da su: “Yanzu ba kwa kiyaye dokokin Allah ba?



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 162

إِنِّي لَكُمۡ رَسُولٌ أَمِينٞ

“Lalle ni Manzo ne amintacce gare ku



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 163

فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ

“To ku kiyaye dokokin Allah kuma ku bi ni



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 164

وَمَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ أَجۡرٍۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ

“Kuma ba na tambayar ku wani lada game da shi (isar da manzancin); ladana yana wajen Ubangijin talikai kawai



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 165

أَتَأۡتُونَ ٱلذُّكۡرَانَ مِنَ ٱلۡعَٰلَمِينَ

“Yanzu kwa riqa zaike wa maza daga halittu?



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 166

وَتَذَرُونَ مَا خَلَقَ لَكُمۡ رَبُّكُم مِّنۡ أَزۡوَٰجِكُمۚ بَلۡ أَنتُمۡ قَوۡمٌ عَادُونَ

“Kuma ku bar abin da Ubangijinku Ya halitta na matanku dominku? A’a, ku dai mutane ne masu qetare iyaka.”



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 167

قَالُواْ لَئِن لَّمۡ تَنتَهِ يَٰلُوطُ لَتَكُونَنَّ مِنَ ٱلۡمُخۡرَجِينَ

Suka ce: “Tabbas Luxu idan ba ka bar (faxar abin da kake faxa ba) haqiqa za ka kasance daga korarru (daga garin nan).”



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 168

قَالَ إِنِّي لِعَمَلِكُم مِّنَ ٱلۡقَالِينَ

(Luxu) ya ce: “Lalle ni ina cikin masu qyamar aikin nan naku



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 169

رَبِّ نَجِّنِي وَأَهۡلِي مِمَّا يَعۡمَلُونَ

“Ya Ubangijina, Ka tserar da ni da iyalina daga (sakamakon) abin da suke aikatawa.”



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 170

فَنَجَّيۡنَٰهُ وَأَهۡلَهُۥٓ أَجۡمَعِينَ

Sai Muka tserar da shi da iyalinsa gaba xaya



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 171

إِلَّا عَجُوزٗا فِي ٱلۡغَٰبِرِينَ

Sai fa wata tsohuwa (watau matarsa) da ta (kasance tana) cikin hallakakku



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 172

ثُمَّ دَمَّرۡنَا ٱلۡأٓخَرِينَ

Sannan Muka hallaka sauran



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 173

وَأَمۡطَرۡنَا عَلَيۡهِم مَّطَرٗاۖ فَسَآءَ مَطَرُ ٱلۡمُنذَرِينَ

Muka kuma saukar musu da ruwa na azaba; to ruwan azabar waxanda aka yi wa gargaxi ya munana



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 174

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ

Lalle a game da wannan tabbas akwai aya; yawancinsu kuwa ba su zamanto muminai ba



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 175

وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ

Kuma lalle Ubangiijnka tabbas Shi ne Mabuwayi, Mai jin qai



Surah: Suratun Namli

Ayah : 54

وَلُوطًا إِذۡ قَالَ لِقَوۡمِهِۦٓ أَتَأۡتُونَ ٱلۡفَٰحِشَةَ وَأَنتُمۡ تُبۡصِرُونَ

Kuma ka (ambaci) Luxu lokacin da ya ce da mutanensa: “Yanzu kwa riqa zaike wa alfasha alhali kuwa kuna gani?



Surah: Suratun Namli

Ayah : 55

أَئِنَّكُمۡ لَتَأۡتُونَ ٱلرِّجَالَ شَهۡوَةٗ مِّن دُونِ ٱلنِّسَآءِۚ بَلۡ أَنتُمۡ قَوۡمٞ تَجۡهَلُونَ

“Yanzu kwa riqa zaike wa maza don sha’awa ba mata ba? A’a, ku dai wasu irin mutane ne da kuke da jahilci”



Surah: Suratun Namli

Ayah : 56

۞فَمَا كَانَ جَوَابَ قَوۡمِهِۦٓ إِلَّآ أَن قَالُوٓاْ أَخۡرِجُوٓاْ ءَالَ لُوطٖ مِّن قَرۡيَتِكُمۡۖ إِنَّهُمۡ أُنَاسٞ يَتَطَهَّرُونَ

To babu wata amsa da ta fito daga bakin mutanensa sai kawai suka ce: “Ku fitar da Luxu shi da iyalinsa daga alqaryarku; lalle su mutane ne da suke nuna su masu tsarki ne.”



Surah: Suratun Namli

Ayah : 57

فَأَنجَيۡنَٰهُ وَأَهۡلَهُۥٓ إِلَّا ٱمۡرَأَتَهُۥ قَدَّرۡنَٰهَا مِنَ ٱلۡغَٰبِرِينَ

Sai Muka tserar da shi tare da iyalinsa in ban da matarsa da Muka qaddara ta cikin hallakakku



Surah: Suratun Namli

Ayah : 58

وَأَمۡطَرۡنَا عَلَيۡهِم مَّطَرٗاۖ فَسَآءَ مَطَرُ ٱلۡمُنذَرِينَ

Muka kuma yi musu ruwan azaba; to ruwan azabar waxanda aka yi wa gargaxi ya munana



Surah: Suratul Ankabut

Ayah : 26

۞فَـَٔامَنَ لَهُۥ لُوطٞۘ وَقَالَ إِنِّي مُهَاجِرٌ إِلَىٰ رَبِّيٓۖ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡحَكِيمُ

Sai Luxu ya yi imani da shi. (Sai Ibrahimu) kuma ya ce: “Lalle ni mai yin hijira ne zuwa ga Ubangijina; lalle Shi Mabuwayi ne, Mai hikima.”



Surah: Suratul Ankabut

Ayah : 31

وَلَمَّا جَآءَتۡ رُسُلُنَآ إِبۡرَٰهِيمَ بِٱلۡبُشۡرَىٰ قَالُوٓاْ إِنَّا مُهۡلِكُوٓاْ أَهۡلِ هَٰذِهِ ٱلۡقَرۡيَةِۖ إِنَّ أَهۡلَهَا كَانُواْ ظَٰلِمِينَ

Lokacin kuwa da manzanninmu suka zo wa Ibrahimu da albishir[1], sai suka ce: “Lalle mu masu hallaka mutanen wannan alqaryar ne, lalle mutanenta sun kasance azzalumai.”


1- Albishir na samun haihuwar xansa Ishaq () da kuma jikansa Ya’aqub ().