Surah: Suratul Ma’ida

Ayah : 116

وَإِذۡ قَالَ ٱللَّهُ يَٰعِيسَى ٱبۡنَ مَرۡيَمَ ءَأَنتَ قُلۡتَ لِلنَّاسِ ٱتَّخِذُونِي وَأُمِّيَ إِلَٰهَيۡنِ مِن دُونِ ٱللَّهِۖ قَالَ سُبۡحَٰنَكَ مَا يَكُونُ لِيٓ أَنۡ أَقُولَ مَا لَيۡسَ لِي بِحَقٍّۚ إِن كُنتُ قُلۡتُهُۥ فَقَدۡ عَلِمۡتَهُۥۚ تَعۡلَمُ مَا فِي نَفۡسِي وَلَآ أَعۡلَمُ مَا فِي نَفۡسِكَۚ إِنَّكَ أَنتَ عَلَّـٰمُ ٱلۡغُيُوبِ

Kuma (ka tuna) lokacin da Allah zai ce: “Ya kai Isa xan Maryamu, shin kai ne ka ce da mutane: ‘Ku riqe ni, ni da mahaifiyata a matsayin alloli biyu ban da Allah?’” Sai ya ce: “Tsarki ya tabbata gare Ka, bai dace ba a gare ni in faxi wani abu wanda ba ni da haqqin (faxar sa). Idan har na faxe shi, to haqiqa Ka riga Ka sani, Ka san abin da yake cikin raina, amma ni ban san abin da yake ranka ba. Lalle Kai ne Masanin abubuwan da suke voye



Surah: Suratul An’am

Ayah : 3

وَهُوَ ٱللَّهُ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَفِي ٱلۡأَرۡضِ يَعۡلَمُ سِرَّكُمۡ وَجَهۡرَكُمۡ وَيَعۡلَمُ مَا تَكۡسِبُونَ

Kuma Shi ne Allah a cikin sammai da kuma cikin qasa; Yana sane da abin da kuke voyewa da abin da kuke bayyanawa, kuma Yana sane da abin da kuke aikatawa



Surah: Suratul An’am

Ayah : 13

۞وَلَهُۥ مَا سَكَنَ فِي ٱلَّيۡلِ وَٱلنَّهَارِۚ وَهُوَ ٱلسَّمِيعُ ٱلۡعَلِيمُ

“Kuma abin da ya nutsu a cikin dare ko rana nasa ne, kuma Shi ne Mai ji, Mai yawan sani.”



Surah: Suratul An’am

Ayah : 59

۞وَعِندَهُۥ مَفَاتِحُ ٱلۡغَيۡبِ لَا يَعۡلَمُهَآ إِلَّا هُوَۚ وَيَعۡلَمُ مَا فِي ٱلۡبَرِّ وَٱلۡبَحۡرِۚ وَمَا تَسۡقُطُ مِن وَرَقَةٍ إِلَّا يَعۡلَمُهَا وَلَا حَبَّةٖ فِي ظُلُمَٰتِ ٱلۡأَرۡضِ وَلَا رَطۡبٖ وَلَا يَابِسٍ إِلَّا فِي كِتَٰبٖ مُّبِينٖ

“Kuma mabuxan gaibu a wurinsa suke Shi kaxai[1], babu wanda ya san su sai Shi. Kuma Ya san qididdigar abin da yake kan tudu da na ruwa. Kuma babu wani ganyen itace da zai faxo, face sai Ya san da shi, kuma ba wata qwaya da take cikin duhun qasa, kuma ba wani xanyen abu ko busasshe, face (bayaninsa) yana cikin Littafi mabayyani


1- Mabuxan gaibu biyar ne babu wanda ya san su sai Allah. Su ne suka zo a qarshen Suratu Luqman aya ta 34.


Surah: Suratul An’am

Ayah : 60

وَهُوَ ٱلَّذِي يَتَوَفَّىٰكُم بِٱلَّيۡلِ وَيَعۡلَمُ مَا جَرَحۡتُم بِٱلنَّهَارِ ثُمَّ يَبۡعَثُكُمۡ فِيهِ لِيُقۡضَىٰٓ أَجَلٞ مُّسَمّٗىۖ ثُمَّ إِلَيۡهِ مَرۡجِعُكُمۡ ثُمَّ يُنَبِّئُكُم بِمَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ

“Kuma Shi ne Yake karvar rayukanku da daddare[1], kuma Ya san abin da kuka aikata da rana, sannan Ya tayar da ku a cikinta (ranar), har zuwa lokacin da zai zartar da wani ajali sananne, sannan zuwa gare Shi ne makomarku take, sannan zai ba ku labarin abin da kuka kasance kuna aikatawa


1- Watau lokacin barcinku; ya riqe ran da ya hukunta masa mutuwa, ya sako wanda lokacin mutuwarsa bai zo ba. duba Suratuz Zumar aya ta 42.


Surah: Suratul An’am

Ayah : 80

وَحَآجَّهُۥ قَوۡمُهُۥۚ قَالَ أَتُحَـٰٓجُّوٓنِّي فِي ٱللَّهِ وَقَدۡ هَدَىٰنِۚ وَلَآ أَخَافُ مَا تُشۡرِكُونَ بِهِۦٓ إِلَّآ أَن يَشَآءَ رَبِّي شَيۡـٔٗاۚ وَسِعَ رَبِّي كُلَّ شَيۡءٍ عِلۡمًاۚ أَفَلَا تَتَذَكَّرُونَ

Kuma mutanensa sun yi jayayya da shi; (sai) ya ce: “Shin yanzu kwa riqa jayayya da ni game da (kaxaitakar) Allah, alhalin kuwa Ya shiryar da ni? Kuma ba na jin tsoron abin da kuke sanya wa Allah kishiya da shi, sai abin da Ubangijina Ya ga dama. Kuma ilimin Ubangijina ya yalwaci komai. Shin ba za ku wa’azantu ba?



Surah: Suratul An’am

Ayah : 117

إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعۡلَمُ مَن يَضِلُّ عَن سَبِيلِهِۦۖ وَهُوَ أَعۡلَمُ بِٱلۡمُهۡتَدِينَ

Lalle Ubangijinka Shi ne Mafi sanin waxanda suke vace wa tafarkinsa, kuma Shi ne Mafi sanin shiryayyu



Surah: Suratul An’am

Ayah : 119

وَمَا لَكُمۡ أَلَّا تَأۡكُلُواْ مِمَّا ذُكِرَ ٱسۡمُ ٱللَّهِ عَلَيۡهِ وَقَدۡ فَصَّلَ لَكُم مَّا حَرَّمَ عَلَيۡكُمۡ إِلَّا مَا ٱضۡطُرِرۡتُمۡ إِلَيۡهِۗ وَإِنَّ كَثِيرٗا لَّيُضِلُّونَ بِأَهۡوَآئِهِم بِغَيۡرِ عِلۡمٍۚ إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعۡلَمُ بِٱلۡمُعۡتَدِينَ

Kuma me ya sa ba za ku ci abin da aka ambaci sunan Allah a kansa ba, alhali Ya bayyana muku abin da Ya haramta muku, sai fa abin da kuka matsu game da shi[1]? Kuma lalle yawancinsu ba shakka suna vatar da waxansu ne ta hanyar bin son zuciyarsu, ba tare da ilimi ba. Lalle Ubangijinka Shi ne Mafi sanin masu qetare iyaka


1- A halin larura an halatta wa Musulmi ya ci abin da aka haramta masa gwargwadon wannan larurar kaxai.


Surah: Suratul An’am

Ayah : 124

وَإِذَا جَآءَتۡهُمۡ ءَايَةٞ قَالُواْ لَن نُّؤۡمِنَ حَتَّىٰ نُؤۡتَىٰ مِثۡلَ مَآ أُوتِيَ رُسُلُ ٱللَّهِۘ ٱللَّهُ أَعۡلَمُ حَيۡثُ يَجۡعَلُ رِسَالَتَهُۥۗ سَيُصِيبُ ٱلَّذِينَ أَجۡرَمُواْ صَغَارٌ عِندَ ٱللَّهِ وَعَذَابٞ شَدِيدُۢ بِمَا كَانُواْ يَمۡكُرُونَ

Kuma idan wata aya ta zo musu, sai su ce: “Ba za mu yi imani ba, har sai an ba mu kwatankwacin abin da aka ba wa manzannin Allah.” Ai Allah Shi ne Mafi sanin inda ya dace Ya sanya manzancinsa. Da sannu qasqanci daga Allah zai auka wa waxanda suka aikata manyan laifuka da kuma azaba mai tsanani, saboda abin da suka kasance suna shiryawa na makirci



Surah: Suratul A’araf

Ayah : 7

فَلَنَقُصَّنَّ عَلَيۡهِم بِعِلۡمٖۖ وَمَا كُنَّا غَآئِبِينَ

Kuma lalle za Mu ba su labarin (komai) da ilimi; kuma ba Mu zamanto ba ma nan ba



Surah: Suratul A’araf

Ayah : 52

وَلَقَدۡ جِئۡنَٰهُم بِكِتَٰبٖ فَصَّلۡنَٰهُ عَلَىٰ عِلۡمٍ هُدٗى وَرَحۡمَةٗ لِّقَوۡمٖ يُؤۡمِنُونَ

Lalle haqiqa kuma Mun zo musu da littafin[1] da Muka bayyana shi filla-filla bisa ilimi da shiriya da rahama ga mutanen da suke yin imani


1- Watau Alqur’ani mai girma.


Surah: Suratul A’araf

Ayah : 89

قَدِ ٱفۡتَرَيۡنَا عَلَى ٱللَّهِ كَذِبًا إِنۡ عُدۡنَا فِي مِلَّتِكُم بَعۡدَ إِذۡ نَجَّىٰنَا ٱللَّهُ مِنۡهَاۚ وَمَا يَكُونُ لَنَآ أَن نَّعُودَ فِيهَآ إِلَّآ أَن يَشَآءَ ٱللَّهُ رَبُّنَاۚ وَسِعَ رَبُّنَا كُلَّ شَيۡءٍ عِلۡمًاۚ عَلَى ٱللَّهِ تَوَكَّلۡنَاۚ رَبَّنَا ٱفۡتَحۡ بَيۡنَنَا وَبَيۡنَ قَوۡمِنَا بِٱلۡحَقِّ وَأَنتَ خَيۡرُ ٱلۡفَٰتِحِينَ

“Haqiqa mun qirqiri qarya, mun jingina wa Allah, in har muka komo cikin addininku, bayan kuwa Allah Ya tserar da mu daga gare shi. Kuma ba ma zai yiwu ba mu koma cikinsa sai dai idan Allah Ubangijinmu ne Ya ga dama. Kuma ilimin Ubangijinmu Ya yalwaci komai. Ga Allah kaxai muka dogara. Ya Ubangijinmu, Ka yi hukunci tsakaninmu da mutanenmu da gaskiya, kuma Kai ne Fiyayyen masu hukunci.”



Surah: Suratul A’araf

Ayah : 187

يَسۡـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلسَّاعَةِ أَيَّانَ مُرۡسَىٰهَاۖ قُلۡ إِنَّمَا عِلۡمُهَا عِندَ رَبِّيۖ لَا يُجَلِّيهَا لِوَقۡتِهَآ إِلَّا هُوَۚ ثَقُلَتۡ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ لَا تَأۡتِيكُمۡ إِلَّا بَغۡتَةٗۗ يَسۡـَٔلُونَكَ كَأَنَّكَ حَفِيٌّ عَنۡهَاۖ قُلۡ إِنَّمَا عِلۡمُهَا عِندَ ٱللَّهِ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَ ٱلنَّاسِ لَا يَعۡلَمُونَ

Suna tambayar ka game da tashin alqiyama yaushe ne matabbatarta take? Ka ce: “Sanin lokacinta yana wajen Ubangijina; ba mai bayyanar da lokacinta sai Shi. Ta yi nauyi a cikin sammai da qasa. Ba za ta zo muku ba sai katsahan.” Suna tambayar ka kamar ka nace a kanta, ka ce: “Iliminta yana wajen Allah kaxai”, sai dai da yawa daga cikin mutane ba su sani ba



Surah: Suratul Anfal

Ayah : 53

ذَٰلِكَ بِأَنَّ ٱللَّهَ لَمۡ يَكُ مُغَيِّرٗا نِّعۡمَةً أَنۡعَمَهَا عَلَىٰ قَوۡمٍ حَتَّىٰ يُغَيِّرُواْ مَا بِأَنفُسِهِمۡ وَأَنَّ ٱللَّهَ سَمِيعٌ عَلِيمٞ

Wannan (kuwa) saboda Allah bai kasance Mai canza wata ni’ima da Ya yi wa wasu mutane ba har sai sun canja halayensu, lalle Allah kuma Mai ji ne Masani



Surah: Suratul Anfal

Ayah : 60

وَأَعِدُّواْ لَهُم مَّا ٱسۡتَطَعۡتُم مِّن قُوَّةٖ وَمِن رِّبَاطِ ٱلۡخَيۡلِ تُرۡهِبُونَ بِهِۦ عَدُوَّ ٱللَّهِ وَعَدُوَّكُمۡ وَءَاخَرِينَ مِن دُونِهِمۡ لَا تَعۡلَمُونَهُمُ ٱللَّهُ يَعۡلَمُهُمۡۚ وَمَا تُنفِقُواْ مِن شَيۡءٖ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ يُوَفَّ إِلَيۡكُمۡ وَأَنتُمۡ لَا تُظۡلَمُونَ

Ku yi musu tanadin abin da kuke iyawa na qarfi da kuma tanadin xaurarrun dawakai, kuna tsorata maqiya Allah kuma maqiyanku da shi (tanadin), har kuma da wasu ban da su da ba ku san su ba, Allah ne kawai Ya san su. Kuma duk irin abin da kuka ciyar cikin hanyar Allah za a cika muku (ladanku) ba kuwa za a zalunce ku ba



Surah: Suratut Tauba

Ayah : 44

لَا يَسۡتَـٔۡذِنُكَ ٱلَّذِينَ يُؤۡمِنُونَ بِٱللَّهِ وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡأٓخِرِ أَن يُجَٰهِدُواْ بِأَمۡوَٰلِهِمۡ وَأَنفُسِهِمۡۗ وَٱللَّهُ عَلِيمُۢ بِٱلۡمُتَّقِينَ

Waxanda suka yi imani da Allah da ranar lahira ba sa neman izininka don kada su yi yaqi da dukiyoyinsu da kawunansu. Allah kuwa yana sane da masu taqawa



Surah: Suratut Tauba

Ayah : 47

لَوۡ خَرَجُواْ فِيكُم مَّا زَادُوكُمۡ إِلَّا خَبَالٗا وَلَأَوۡضَعُواْ خِلَٰلَكُمۡ يَبۡغُونَكُمُ ٱلۡفِتۡنَةَ وَفِيكُمۡ سَمَّـٰعُونَ لَهُمۡۗ وَٱللَّهُ عَلِيمُۢ بِٱلظَّـٰلِمِينَ

Da sun fito cikinku xin, to ba abin da za su qare ku da shi sai tavarvarewa, kuma lalle da sun yi ta shige da fice a tsakaninku suna qoqarin haifar muku da fitina, a cikinku kuma akwai masu jiyo musu (wato abokan gaba) magana. Allah kuwa Masanin azzalumai ne



Surah: Suratut Tauba

Ayah : 78

أَلَمۡ يَعۡلَمُوٓاْ أَنَّ ٱللَّهَ يَعۡلَمُ سِرَّهُمۡ وَنَجۡوَىٰهُمۡ وَأَنَّ ٱللَّهَ عَلَّـٰمُ ٱلۡغُيُوبِ

Yanzu ba su sani ba cewa, lalle Allah Ya san asirinsu da kuma ganawar da suke yi, lalle kuma Allah Shi ne cikakken Masanin gaibu?



Surah: Suratut Tauba

Ayah : 101

وَمِمَّنۡ حَوۡلَكُم مِّنَ ٱلۡأَعۡرَابِ مُنَٰفِقُونَۖ وَمِنۡ أَهۡلِ ٱلۡمَدِينَةِ مَرَدُواْ عَلَى ٱلنِّفَاقِ لَا تَعۡلَمُهُمۡۖ نَحۡنُ نَعۡلَمُهُمۡۚ سَنُعَذِّبُهُم مَّرَّتَيۡنِ ثُمَّ يُرَدُّونَ إِلَىٰ عَذَابٍ عَظِيمٖ

Kuma daga mutanen qauye waxanda suke kewaye da ku akwai munafukai, haka kuma daga mutan Madina; sun qware a kan munafunci, kai ba ka san su ba; Mu ne Muka san su. Za Mu azabtar da su sau biyu, sannan a komar da su zuwa ga azaba mai girma



Surah: Suratut Tauba

Ayah : 115

وَمَا كَانَ ٱللَّهُ لِيُضِلَّ قَوۡمَۢا بَعۡدَ إِذۡ هَدَىٰهُمۡ حَتَّىٰ يُبَيِّنَ لَهُم مَّا يَتَّقُونَۚ إِنَّ ٱللَّهَ بِكُلِّ شَيۡءٍ عَلِيمٌ

Allah kuwa ba zai tava vatar da wasu mutane ba bayan Ya riga Ya shiryar da su, har sai Ya bayyana musu abin da za su kiyaye. Lalle Allah Masanin komai ne



Surah: Suratu Yunus

Ayah : 36

وَمَا يَتَّبِعُ أَكۡثَرُهُمۡ إِلَّا ظَنًّاۚ إِنَّ ٱلظَّنَّ لَا يُغۡنِي مِنَ ٱلۡحَقِّ شَيۡـًٔاۚ إِنَّ ٱللَّهَ عَلِيمُۢ بِمَا يَفۡعَلُونَ

Yawancinsu kuma ba abin da suke bi sai zato. Lalle zato ba ya wadatar da komai game da gaskiya. Lalle Allah Masanin abin da suke aikatawa ne



Surah: Suratu Yunus

Ayah : 40

وَمِنۡهُم مَّن يُؤۡمِنُ بِهِۦ وَمِنۡهُم مَّن لَّا يُؤۡمِنُ بِهِۦۚ وَرَبُّكَ أَعۡلَمُ بِٱلۡمُفۡسِدِينَ

Daga cikinsu kuma akwai wanda yake yin imani da shi (Alqur’ani), akwai kuma wanda ba ya yin imani da shi. Ubangijinka kuma Shi ne Mafi sanin mavarnata



Surah: Suratu Yunus

Ayah : 61

وَمَا تَكُونُ فِي شَأۡنٖ وَمَا تَتۡلُواْ مِنۡهُ مِن قُرۡءَانٖ وَلَا تَعۡمَلُونَ مِنۡ عَمَلٍ إِلَّا كُنَّا عَلَيۡكُمۡ شُهُودًا إِذۡ تُفِيضُونَ فِيهِۚ وَمَا يَعۡزُبُ عَن رَّبِّكَ مِن مِّثۡقَالِ ذَرَّةٖ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَلَا فِي ٱلسَّمَآءِ وَلَآ أَصۡغَرَ مِن ذَٰلِكَ وَلَآ أَكۡبَرَ إِلَّا فِي كِتَٰبٖ مُّبِينٍ

Kuma babu wani al’amari da (kai Annabi) kake zamantowa cikinsa, babu kuma wani abu na Alqur’ani da kake karantawa, kuma babu wani abu da kuke aikatawa (kai da al’ummarka), sai Mun zamanto Muna kallon ku lokacin da kuke kutsawa cikinsa. Kuma babu wani abu da yake voye wa Ubangijinka daidai da qwayar komayya, a qasa ko a sama ko kuma mafi qanqanta ko mafi girma daga wancan (abin) sai fa yana cikin litttafi mabayyani (Lauhul-Mahafuzu)



Surah: Suratu Hud

Ayah : 5

أَلَآ إِنَّهُمۡ يَثۡنُونَ صُدُورَهُمۡ لِيَسۡتَخۡفُواْ مِنۡهُۚ أَلَا حِينَ يَسۡتَغۡشُونَ ثِيَابَهُمۡ يَعۡلَمُ مَا يُسِرُّونَ وَمَا يُعۡلِنُونَۚ إِنَّهُۥ عَلِيمُۢ بِذَاتِ ٱلصُّدُورِ

Ku saurara! Lalle su suna karkatar da qirazansu don su voye masa (Allah). Ku saurara! Ai lokacin da suke lulluva da tufafinsu Yana sane da abin da suke voyewa da kuma abin da suke bayyanawa. Lalle Shi (Allah) Masanin abin da yake cikin zukata ne



Surah: Suratu Hud

Ayah : 6

۞وَمَا مِن دَآبَّةٖ فِي ٱلۡأَرۡضِ إِلَّا عَلَى ٱللَّهِ رِزۡقُهَا وَيَعۡلَمُ مُسۡتَقَرَّهَا وَمُسۡتَوۡدَعَهَاۚ كُلّٞ فِي كِتَٰبٖ مُّبِينٖ

Kuma babu wata dabba a ban qasa face arzikinta yana hannun Allah, kuma Yana sane da matabbatarta da ma’ajiyarta[1]. Dukkanin wannan yana nan a cikin littafi mabayyani (shi ne Lauhul Mahafuzu)


1- Watau ya san wurin zamansu da wurin tafiye-tafiyensu, ya san inda za su mutu a binne su.


Surah: Suratu Hud

Ayah : 14

فَإِلَّمۡ يَسۡتَجِيبُواْ لَكُمۡ فَٱعۡلَمُوٓاْ أَنَّمَآ أُنزِلَ بِعِلۡمِ ٱللَّهِ وَأَن لَّآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَۖ فَهَلۡ أَنتُم مُّسۡلِمُونَ

To idan ba su amsa muku ba, to ku tabbatar cewa lalle an saukar da shi ne (Alqur’ani) da sanin Allah, kuma babu wani abin bauta da gaskiya sai Shi, To shin yanzu za ku miqa wuya?



Surah: Suratu Hud

Ayah : 31

وَلَآ أَقُولُ لَكُمۡ عِندِي خَزَآئِنُ ٱللَّهِ وَلَآ أَعۡلَمُ ٱلۡغَيۡبَ وَلَآ أَقُولُ إِنِّي مَلَكٞ وَلَآ أَقُولُ لِلَّذِينَ تَزۡدَرِيٓ أَعۡيُنُكُمۡ لَن يُؤۡتِيَهُمُ ٱللَّهُ خَيۡرًاۖ ٱللَّهُ أَعۡلَمُ بِمَا فِيٓ أَنفُسِهِمۡ إِنِّيٓ إِذٗا لَّمِنَ ٱلظَّـٰلِمِينَ

“Ba kuma zan ce da ku ina da taskokin Allah ba, ban kuma san gaibu ba, kuma ba zan ce lalle ni mala’ika ne ba, ba kuma zan ce wa waxanda idanuwanku suke wulaqantawa, Allah ba zai ba su wani alheri ba. Allah ne Ya fi sanin abin da yake zukatansu. Idan na yi haka, to lalle na zamanto daga cikin azzalumai.”



Surah: Suratur Ra’ad

Ayah : 8

ٱللَّهُ يَعۡلَمُ مَا تَحۡمِلُ كُلُّ أُنثَىٰ وَمَا تَغِيضُ ٱلۡأَرۡحَامُ وَمَا تَزۡدَادُۚ وَكُلُّ شَيۡءٍ عِندَهُۥ بِمِقۡدَارٍ

Allah Yana sane da abin da (mahaifar) kowace mace take xauke da shi da kuma abin da mahaifa take ragewa da wanda take qarawa[1]; kowane abu kuma a wurinsa yana da gwargwado


1- Watau ana nufin lokacin haihuwarta, ko dai ta haihu kafin cikar wata tara, ko ta haihu bayan cikar wa’adin cikinta, ko xan ya zo cikakke da qoshin lafiya, ko kuma da wata nakasa ko rashin lafiya.


Surah: Suratur Ra’ad

Ayah : 9

عَٰلِمُ ٱلۡغَيۡبِ وَٱلشَّهَٰدَةِ ٱلۡكَبِيرُ ٱلۡمُتَعَالِ

(Shi) Masanin abin da ke voye da na sarari ne, Mai girma, Mai cikar xaukaka



Surah: Suratur Ra’ad

Ayah : 42

وَقَدۡ مَكَرَ ٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِهِمۡ فَلِلَّهِ ٱلۡمَكۡرُ جَمِيعٗاۖ يَعۡلَمُ مَا تَكۡسِبُ كُلُّ نَفۡسٖۗ وَسَيَعۡلَمُ ٱلۡكُفَّـٰرُ لِمَنۡ عُقۡبَى ٱلدَّارِ

Haqiqa kuma waxanda suke gabaninsu sun qulla makirci, (sakamakon) qulle-qulle dukkaninsa ga Allah yake; Yana sane da abin da kowane rai yake aikatawa. Ba da daxewa ba kuma kafirai za su san wane ne mai kyakkyawan gidan (qarshe)