Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 93

أَلَّا تَتَّبِعَنِۖ أَفَعَصَيۡتَ أَمۡرِي

“Ka bi ni (don ka sanar da ni)? Ko kuwa ka sava umarnina ne?”



Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 94

قَالَ يَبۡنَؤُمَّ لَا تَأۡخُذۡ بِلِحۡيَتِي وَلَا بِرَأۡسِيٓۖ إِنِّي خَشِيتُ أَن تَقُولَ فَرَّقۡتَ بَيۡنَ بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ وَلَمۡ تَرۡقُبۡ قَوۡلِي

(Haruna) ya ce: “Ya xan’ummata, kada ka kama mini gemuna, da kuma (gashin) kaina; lalle ni na ji tsoron ka ce (da ni): ‘Ka rarraba kan Banu-Isra’ila, ba ka kuma kiyaye maganata ba.’”



Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 95

قَالَ فَمَا خَطۡبُكَ يَٰسَٰمِرِيُّ

(Musa) ya ce: “Mene ne lamarinka, ya Samiri?”



Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 96

قَالَ بَصُرۡتُ بِمَا لَمۡ يَبۡصُرُواْ بِهِۦ فَقَبَضۡتُ قَبۡضَةٗ مِّنۡ أَثَرِ ٱلرَّسُولِ فَنَبَذۡتُهَا وَكَذَٰلِكَ سَوَّلَتۡ لِي نَفۡسِي

Ya ce: “Na ga abin da ba su gani ba ne[1], sai na xebi danqi daga gurbin (qasar) sawun (goxiyar) Manzon (wato Jibrilu) sannan na watsa ta (a kan xan maraqin). Kamar haka kuwa raina ya qawata mini.”


1- Watau ya ga Mala’ika Jibrilu a kan dokinsa lokacin da ya zo hallaka Fir’auna da jama’arsa.


Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 97

قَالَ فَٱذۡهَبۡ فَإِنَّ لَكَ فِي ٱلۡحَيَوٰةِ أَن تَقُولَ لَا مِسَاسَۖ وَإِنَّ لَكَ مَوۡعِدٗا لَّن تُخۡلَفَهُۥۖ وَٱنظُرۡ إِلَىٰٓ إِلَٰهِكَ ٱلَّذِي ظَلۡتَ عَلَيۡهِ عَاكِفٗاۖ لَّنُحَرِّقَنَّهُۥ ثُمَّ لَنَنسِفَنَّهُۥ فِي ٱلۡيَمِّ نَسۡفًا

(Annabi Musa) ya ce: “To sai ka tafi, amma ka tabbatar cewa (sakamakonka) a rayuwar (da za ka yi) shi ne ka riqa cewa ‘la misasa’, (watau ba za ka tavu ba kuma ba za ka tava kowa ba)[1]; kuma lalle kana da qayyadajjen lokaci wanda ba za a sava maka ba; kuma ka dubi ubangijin naka wanda ka duqufa a kansa kana bauta; lalle za mu qona shi sannan tabbas za mu sheqar da shi cikin kogi.”


1- Watau ba zai iya gauraya da mutane ba; don ba zai iya tava kowa ba, ba kuma wanda zai iya tava jikinsa.


Surah: Suratu Xa Ha

Ayah : 98

إِنَّمَآ إِلَٰهُكُمُ ٱللَّهُ ٱلَّذِي لَآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَۚ وَسِعَ كُلَّ شَيۡءٍ عِلۡمٗا

Abin bautarku kawai shi ne Allah wanda babu wani abin bauta da gaskiya sai Shi. Ya yalwaci komai da iliminsa



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 52

۞وَأَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰ مُوسَىٰٓ أَنۡ أَسۡرِ بِعِبَادِيٓ إِنَّكُم مُّتَّبَعُونَ

Muka kuma yi wa Musa wahayi cewa: “Ka tafi cikin dare tare da bayina, lalle ku za a biyo bayanku.”



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 53

فَأَرۡسَلَ فِرۡعَوۡنُ فِي ٱلۡمَدَآئِنِ حَٰشِرِينَ

Sai Fir’auna ya aika zuwa birane don a tattaro (mayaqa)



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 54

إِنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ لَشِرۡذِمَةٞ قَلِيلُونَ

(Fir’auna yana cewa): “Lalle waxannan tabbas ‘yan tsirarin jama’a ne



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 55

وَإِنَّهُمۡ لَنَا لَغَآئِظُونَ

“Kuma haqiqa su lalle suna fusata mu



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 56

وَإِنَّا لَجَمِيعٌ حَٰذِرُونَ

“Lalle kuma mu tabbas gaba xayanmu masu kwana cikin shiri ne.”



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 57

فَأَخۡرَجۡنَٰهُم مِّن جَنَّـٰتٖ وَعُيُونٖ

(Allah Ya ce): Sai Muka fitar da su daga gonaki da kuma idandunan ruwa



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 58

وَكُنُوزٖ وَمَقَامٖ كَرِيمٖ

Da taskoki da kuma mazauni na alfarma



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 59

كَذَٰلِكَۖ وَأَوۡرَثۡنَٰهَا بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ

Kamar haka ne Muka gadar da su ga Banu-Isra’ila



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 60

فَأَتۡبَعُوهُم مُّشۡرِقِينَ

Sai suka bi bayansu a lokacin fitowar rana



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 61

فَلَمَّا تَرَـٰٓءَا ٱلۡجَمۡعَانِ قَالَ أَصۡحَٰبُ مُوسَىٰٓ إِنَّا لَمُدۡرَكُونَ

To lokacin da jama’ar biyu suka ga juna, sai sahabban Musa suka ce: “Lalle tabbas mu za a cim mana.”



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 62

قَالَ كَلَّآۖ إِنَّ مَعِيَ رَبِّي سَيَهۡدِينِ

(Musa) ya ce: “A’a; Ubangijina Yana tare da ni, zai kuwa shiryar da ni (hanyar tsira).”



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 63

فَأَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰ مُوسَىٰٓ أَنِ ٱضۡرِب بِّعَصَاكَ ٱلۡبَحۡرَۖ فَٱنفَلَقَ فَكَانَ كُلُّ فِرۡقٖ كَٱلطَّوۡدِ ٱلۡعَظِيمِ

Sai Muka yi wahayi ga Musa cewa: “Ka bugi kogin da sandarka;” (da ya buge shi) sai ya dare, kowanne yanki sai ya zama kamar qaton dutse



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 64

وَأَزۡلَفۡنَا ثَمَّ ٱلۡأٓخَرِينَ

Muka kuma kusantar da waxancan (watau mutanen Fir’auna) zuwa can (kusa da kogin)



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 65

وَأَنجَيۡنَا مُوسَىٰ وَمَن مَّعَهُۥٓ أَجۡمَعِينَ

Muka kuma tserar da Musa da waxanda suke tare da shi gaba xaya



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 66

ثُمَّ أَغۡرَقۡنَا ٱلۡأٓخَرِينَ

Sannan Muka nutsar da sauran mutanen (watau Fir’auna da mutanensa)



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 67

إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ

Lalle a game da wannan tabbas akwai aya; kuma yawancinsu ba su zamanto muminai ba



Surah: Suratus Shu’ara

Ayah : 197

أَوَلَمۡ يَكُن لَّهُمۡ ءَايَةً أَن يَعۡلَمَهُۥ عُلَمَـٰٓؤُاْ بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ

Yanzu bai ishe su aya ba cewa, malaman Banu- Isra’ila sun san shi?



Surah: Suratun Namli

Ayah : 76

إِنَّ هَٰذَا ٱلۡقُرۡءَانَ يَقُصُّ عَلَىٰ بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ أَكۡثَرَ ٱلَّذِي هُمۡ فِيهِ يَخۡتَلِفُونَ

Lalle wannan Alqur’anin yana labarta wa Banu-Isra’ila mafi yawan abin da suke savani a kansa



Surah: Suratu Ghafir

Ayah : 53

وَلَقَدۡ ءَاتَيۡنَا مُوسَى ٱلۡهُدَىٰ وَأَوۡرَثۡنَا بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ ٱلۡكِتَٰبَ

Kuma haqiqa Mun bai wa Musa shiriya, Muka kuwa gadar wa Banu-Isra’ila littafin (Attaura)



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 23

فَأَسۡرِ بِعِبَادِي لَيۡلًا إِنَّكُم مُّتَّبَعُونَ

Sai (aka ce masa): “Ka tafi da bayina da daddare, lalle ku za a biyo bayanku



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 24

وَٱتۡرُكِ ٱلۡبَحۡرَ رَهۡوًاۖ إِنَّهُمۡ جُندٞ مُّغۡرَقُونَ

“Kuma ka bar kogi a tsaye cak (bayan tsallakewa); lalle su runduna ne da za a nutsar.”



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 25

كَمۡ تَرَكُواْ مِن جَنَّـٰتٖ وَعُيُونٖ

Sun bar gonaki da kuma idanuwan ruwa masu yawa



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 26

وَزُرُوعٖ وَمَقَامٖ كَرِيمٖ

Da kuma shuke-shuke da wurin zama mai daraja



Surah: Suratud Dukhan

Ayah : 27

وَنَعۡمَةٖ كَانُواْ فِيهَا فَٰكِهِينَ

Da kuma kayan jin daxi da suka kasance masu ni’imtuwa da su