Surah: Suratul A’araf

Ayah : 137

وَأَوۡرَثۡنَا ٱلۡقَوۡمَ ٱلَّذِينَ كَانُواْ يُسۡتَضۡعَفُونَ مَشَٰرِقَ ٱلۡأَرۡضِ وَمَغَٰرِبَهَا ٱلَّتِي بَٰرَكۡنَا فِيهَاۖ وَتَمَّتۡ كَلِمَتُ رَبِّكَ ٱلۡحُسۡنَىٰ عَلَىٰ بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ بِمَا صَبَرُواْۖ وَدَمَّرۡنَا مَا كَانَ يَصۡنَعُ فِرۡعَوۡنُ وَقَوۡمُهُۥ وَمَا كَانُواْ يَعۡرِشُونَ

Mutanen kuma da ake nuna musu fin qarfi a da, Muka gadar musu gabashi da yammacin qasar da Muka yi wa albarka; kuma kalmar Ubangijinka kyakkyawa sai ta tabbata a kan Banu Isra’ila saboda haqurin da suka yi; kuma Muka rushe abin da Fir’auna ya kasance yana yi shi da mutanensa, da abin da suka kasance suna ginawa



Surah: Suratul A’araf

Ayah : 138

وَجَٰوَزۡنَا بِبَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ ٱلۡبَحۡرَ فَأَتَوۡاْ عَلَىٰ قَوۡمٖ يَعۡكُفُونَ عَلَىٰٓ أَصۡنَامٖ لَّهُمۡۚ قَالُواْ يَٰمُوسَى ٱجۡعَل لَّنَآ إِلَٰهٗا كَمَا لَهُمۡ ءَالِهَةٞۚ قَالَ إِنَّكُمۡ قَوۡمٞ تَجۡهَلُونَ

Kuma sai Muka tsallakar da Banu Isra’ila kogi, sai suka tarar da waxansu mutane da suka duqufa a kan (bautar) gumakansu, suka ce: “Ya kai Musa, ka sa mana wani abin bauta, irin yadda waxannan suke da abubuwan bauta.” Sai ya ce: “Lalle ku mutane ne da kuke da jahilci



Surah: Suratul A’araf

Ayah : 139

إِنَّ هَـٰٓؤُلَآءِ مُتَبَّرٞ مَّا هُمۡ فِيهِ وَبَٰطِلٞ مَّا كَانُواْ يَعۡمَلُونَ

“Lalle waxannan abin da suke cikinsa halaka ne, kuma abin da suke aikatawa varna ce.”



Surah: Suratul A’araf

Ayah : 140

قَالَ أَغَيۡرَ ٱللَّهِ أَبۡغِيكُمۡ إِلَٰهٗا وَهُوَ فَضَّلَكُمۡ عَلَى ٱلۡعَٰلَمِينَ

Ya ce: “Shin yanzu wani wanda ba Allah ba zan nemo muku a matsayin abin bauta, alhali Shi ne Ya fifita ku a kan sauran talikai?”



Surah: Suratul A’araf

Ayah : 141

وَإِذۡ أَنجَيۡنَٰكُم مِّنۡ ءَالِ فِرۡعَوۡنَ يَسُومُونَكُمۡ سُوٓءَ ٱلۡعَذَابِ يُقَتِّلُونَ أَبۡنَآءَكُمۡ وَيَسۡتَحۡيُونَ نِسَآءَكُمۡۚ وَفِي ذَٰلِكُم بَلَآءٞ مِّن رَّبِّكُمۡ عَظِيمٞ

Kuma ku tuna lokacin da Muka tserar da ku daga mutanen Fir’auna, (waxanda) suke xanxana muku mummunar azaba; suna karkashe ‘ya’yanku maza, kuma suna barin ‘ya’yanku mata da rai, kuma lalle a cikin wannan akwai wata jarraba babba daga Ubangijinku



Surah: Suratul A’araf

Ayah : 148

وَٱتَّخَذَ قَوۡمُ مُوسَىٰ مِنۢ بَعۡدِهِۦ مِنۡ حُلِيِّهِمۡ عِجۡلٗا جَسَدٗا لَّهُۥ خُوَارٌۚ أَلَمۡ يَرَوۡاْ أَنَّهُۥ لَا يُكَلِّمُهُمۡ وَلَا يَهۡدِيهِمۡ سَبِيلًاۘ ٱتَّخَذُوهُ وَكَانُواْ ظَٰلِمِينَ

Mutanen Musa kuma a bayansa sun qera wani xan maraqi daga kayan adonsu mai surar jiki yana wata qara (don su bauta masa). Shin ba su ga cewa ba ya yi musu Magana, kuma ba ya iya shiryar da su wani tafarki? Sun riqe shi (a matsayin abin bauta), kuma sun tabbata azzalumai



Surah: Suratul A’araf

Ayah : 149

وَلَمَّا سُقِطَ فِيٓ أَيۡدِيهِمۡ وَرَأَوۡاْ أَنَّهُمۡ قَدۡ ضَلُّواْ قَالُواْ لَئِن لَّمۡ يَرۡحَمۡنَا رَبُّنَا وَيَغۡفِرۡ لَنَا لَنَكُونَنَّ مِنَ ٱلۡخَٰسِرِينَ

Kuma lokacin da suka yi nadama, suka gane cewa sun vata, sai suka ce: “Matuqar Ubangijinmu bai ji qan mu ba, kuma bai gafarta mana ba, lalle za mu kasance cikin hasararru.”



Surah: Suratul A’araf

Ayah : 150

وَلَمَّا رَجَعَ مُوسَىٰٓ إِلَىٰ قَوۡمِهِۦ غَضۡبَٰنَ أَسِفٗا قَالَ بِئۡسَمَا خَلَفۡتُمُونِي مِنۢ بَعۡدِيٓۖ أَعَجِلۡتُمۡ أَمۡرَ رَبِّكُمۡۖ وَأَلۡقَى ٱلۡأَلۡوَاحَ وَأَخَذَ بِرَأۡسِ أَخِيهِ يَجُرُّهُۥٓ إِلَيۡهِۚ قَالَ ٱبۡنَ أُمَّ إِنَّ ٱلۡقَوۡمَ ٱسۡتَضۡعَفُونِي وَكَادُواْ يَقۡتُلُونَنِي فَلَا تُشۡمِتۡ بِيَ ٱلۡأَعۡدَآءَ وَلَا تَجۡعَلۡنِي مَعَ ٱلۡقَوۡمِ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Lokacin kuma da Musa ya dawo wajen mutanensa a fusace yana mai damuwa, sai ya ce: “Tir da abin da kuka aikata bayana. Yanzu kwa gaggauto al’amarin Ubangijinku?” Sai ya jefar da allunan, ya kama kan xan’uwansa yana jan sa zuwa gare shi. Sai (Haruna) ya ce: “Ya kai xan’ummata, mutanen nan haqiqa sun raina ni, har ma sun kusa kashe ni, don haka kar ka sa maqiya su yi min dariya, kuma kada ka sa ni cikin mutane azzalumai.”



Surah: Suratul A’araf

Ayah : 151

قَالَ رَبِّ ٱغۡفِرۡ لِي وَلِأَخِي وَأَدۡخِلۡنَا فِي رَحۡمَتِكَۖ وَأَنتَ أَرۡحَمُ ٱلرَّـٰحِمِينَ

Sai ya ce: “Ya Ubangijina, Ka gafarta mini ni da xan’uwana, kuma Ka shigar da mu cikin rahamarka; kuma Kai ne Fiyayyen masu jin qai.”



Surah: Suratul A’araf

Ayah : 152

إِنَّ ٱلَّذِينَ ٱتَّخَذُواْ ٱلۡعِجۡلَ سَيَنَالُهُمۡ غَضَبٞ مِّن رَّبِّهِمۡ وَذِلَّةٞ فِي ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَاۚ وَكَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلۡمُفۡتَرِينَ

Lalle waxannan da suka riqi xan maraqi (abin bauta) fushin Ubangijinsu zai same su da qasqanci a cikin rayuwar duniya. Kuma kamar haka ne Muke saka wa masu qage



Surah: Suratul A’araf

Ayah : 153

وَٱلَّذِينَ عَمِلُواْ ٱلسَّيِّـَٔاتِ ثُمَّ تَابُواْ مِنۢ بَعۡدِهَا وَءَامَنُوٓاْ إِنَّ رَبَّكَ مِنۢ بَعۡدِهَا لَغَفُورٞ رَّحِيمٞ

Waxanda kuma suka aikata munanan ayyuka, sannan suka tuba daga baya, kuma suka yi imani, lalle Ubangijinka bayansa (tuban), tabbas Mai gafara ne, Mai jin qai



Surah: Suratul A’araf

Ayah : 159

وَمِن قَوۡمِ مُوسَىٰٓ أُمَّةٞ يَهۡدُونَ بِٱلۡحَقِّ وَبِهِۦ يَعۡدِلُونَ

Kuma daga cikin mutanen Musa akwai wata jama’a waxanda suke shiryarwa da gaskiya, da kuma ita ne suke yin hukunci na adalci[1]


1- Su ne waxanda suka yi Imani da Annabi Muhammadu ().


Surah: Suratul A’araf

Ayah : 160

وَقَطَّعۡنَٰهُمُ ٱثۡنَتَيۡ عَشۡرَةَ أَسۡبَاطًا أُمَمٗاۚ وَأَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰ مُوسَىٰٓ إِذِ ٱسۡتَسۡقَىٰهُ قَوۡمُهُۥٓ أَنِ ٱضۡرِب بِّعَصَاكَ ٱلۡحَجَرَۖ فَٱنۢبَجَسَتۡ مِنۡهُ ٱثۡنَتَا عَشۡرَةَ عَيۡنٗاۖ قَدۡ عَلِمَ كُلُّ أُنَاسٖ مَّشۡرَبَهُمۡۚ وَظَلَّلۡنَا عَلَيۡهِمُ ٱلۡغَمَٰمَ وَأَنزَلۡنَا عَلَيۡهِمُ ٱلۡمَنَّ وَٱلسَّلۡوَىٰۖ كُلُواْ مِن طَيِّبَٰتِ مَا رَزَقۡنَٰكُمۡۚ وَمَا ظَلَمُونَا وَلَٰكِن كَانُوٓاْ أَنفُسَهُمۡ يَظۡلِمُونَ

Mun kuma karkasa su qabilu goma sha biyu daban-daban[1], sai Muka kuma yi wahayi ga Musa yayin da mutanensa suka nemi ya shayar da su ruwa cewa: “Ka doki dutse da sandarka,” sai idanun ruwa goma sha biyu suka vuvvugo daga jikinsa. Haqiqa kowace qabila ta san mashayarta. Muka kuma yi musu inuwa da girgije, kuma Muka saukar musu da darva da tsuntsayen salwa; (muka ce:) “Ku ci daga daddaxan abin da Muka arzurta ku da shi.” Kuma ba su zalunce Mu ba, sai dai kansu suka kasance suna zalunta


1- Su ne zuriyyar ‘ya’yan Annabi Ya’aqub () goma sha biyu.


Surah: Suratul A’araf

Ayah : 161

وَإِذۡ قِيلَ لَهُمُ ٱسۡكُنُواْ هَٰذِهِ ٱلۡقَرۡيَةَ وَكُلُواْ مِنۡهَا حَيۡثُ شِئۡتُمۡ وَقُولُواْ حِطَّةٞ وَٱدۡخُلُواْ ٱلۡبَابَ سُجَّدٗا نَّغۡفِرۡ لَكُمۡ خَطِيٓـَٰٔتِكُمۡۚ سَنَزِيدُ ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Kuma ka tuna lokacin da aka ce musu: “Ku zauna a wannan alqarya, kuma ku ci daga gare ta a duk inda kuka ga dama, ku kuma ce: Hixxa (wato Allah Ka share mana laifukanmu), ku kuma shiga ta qofar alqaryar kuna masu sujjada, za Mu gafarta muku zunubanku, kuma za Mu qara wa masu kyautatawa.”



Surah: Suratul A’araf

Ayah : 162

فَبَدَّلَ ٱلَّذِينَ ظَلَمُواْ مِنۡهُمۡ قَوۡلًا غَيۡرَ ٱلَّذِي قِيلَ لَهُمۡ فَأَرۡسَلۡنَا عَلَيۡهِمۡ رِجۡزٗا مِّنَ ٱلسَّمَآءِ بِمَا كَانُواْ يَظۡلِمُونَ

Sai waxanda suka yi zalunci a cikinsu suka canja magana daban da wadda aka faxa musu, sai Muka aiko musu da wata azaba daga sama, saboda abin da suka kasance suna yi na zalunci



Surah: Suratul A’araf

Ayah : 163

وَسۡـَٔلۡهُمۡ عَنِ ٱلۡقَرۡيَةِ ٱلَّتِي كَانَتۡ حَاضِرَةَ ٱلۡبَحۡرِ إِذۡ يَعۡدُونَ فِي ٱلسَّبۡتِ إِذۡ تَأۡتِيهِمۡ حِيتَانُهُمۡ يَوۡمَ سَبۡتِهِمۡ شُرَّعٗا وَيَوۡمَ لَا يَسۡبِتُونَ لَا تَأۡتِيهِمۡۚ كَذَٰلِكَ نَبۡلُوهُم بِمَا كَانُواْ يَفۡسُقُونَ

Kuma ka tambaye su game da (mutanen) alqaryar nan wadda take dab da gavar teku, yayin da suke qetare iyaka a ranar Asabar, yayin da kifayensu suke zuwa a ranar Asabar baja-baja, amma ranar da ba Asabar ba kuwa ba sa zuwa. Kamar haka ne muka jarrabe su saboda abin da suka kasance suna yi na fasiqanci



Surah: Suratul A’araf

Ayah : 164

وَإِذۡ قَالَتۡ أُمَّةٞ مِّنۡهُمۡ لِمَ تَعِظُونَ قَوۡمًا ٱللَّهُ مُهۡلِكُهُمۡ أَوۡ مُعَذِّبُهُمۡ عَذَابٗا شَدِيدٗاۖ قَالُواْ مَعۡذِرَةً إِلَىٰ رَبِّكُمۡ وَلَعَلَّهُمۡ يَتَّقُونَ

Kuma ka tuna lokacin da wata jama’a cikinsu suka ce: “Don me za ku riqa wa’azi ga waxansu mutanen da idan Allah Ya ga dama sai Ya hallakar da su ko Ya yi musu azaba mai tsanani?” Sai suka ce: “Don yanke hanzari ne a wurin Ubangijinku ko watakila kuma sa kiyaye dokokin Allah.”



Surah: Suratul A’araf

Ayah : 165

فَلَمَّا نَسُواْ مَا ذُكِّرُواْ بِهِۦٓ أَنجَيۡنَا ٱلَّذِينَ يَنۡهَوۡنَ عَنِ ٱلسُّوٓءِ وَأَخَذۡنَا ٱلَّذِينَ ظَلَمُواْ بِعَذَابِۭ بَـِٔيسِۭ بِمَا كَانُواْ يَفۡسُقُونَ

To yayin da suka yi watsi da abin da aka yi musu wa’azi da shi, sai Muka tserar da waxanda suke hana mummunan aiki, Muka kuma kama waxanda suka yi zalunci, da wata mummunar azaba, saboda abin da suka riqa yi na fasiqanci



Surah: Suratul A’araf

Ayah : 166

فَلَمَّا عَتَوۡاْ عَن مَّا نُهُواْ عَنۡهُ قُلۡنَا لَهُمۡ كُونُواْ قِرَدَةً خَٰسِـِٔينَ

To yayin da suka yi tsaurin kai a kan abin da aka hana su, sai Muka ce da su: “Ku zama birrai, qasqantattu.”



Surah: Suratul A’araf

Ayah : 167

وَإِذۡ تَأَذَّنَ رَبُّكَ لَيَبۡعَثَنَّ عَلَيۡهِمۡ إِلَىٰ يَوۡمِ ٱلۡقِيَٰمَةِ مَن يَسُومُهُمۡ سُوٓءَ ٱلۡعَذَابِۗ إِنَّ رَبَّكَ لَسَرِيعُ ٱلۡعِقَابِ وَإِنَّهُۥ لَغَفُورٞ رَّحِيمٞ

Kuma ka tuna lokacin da Ubangijinka Ya yi shela, lalle zai aiko musu da wanda zai xanxana musu mummunar azaba, har ya zuwa ranar tashin alqiyama. Lalle Ubangijinka Mai gaggawar uquba ne, kuma lalle shi tabbas Mai gafara ne, Mai jin qai



Surah: Suratul A’araf

Ayah : 168

وَقَطَّعۡنَٰهُمۡ فِي ٱلۡأَرۡضِ أُمَمٗاۖ مِّنۡهُمُ ٱلصَّـٰلِحُونَ وَمِنۡهُمۡ دُونَ ذَٰلِكَۖ وَبَلَوۡنَٰهُم بِٱلۡحَسَنَٰتِ وَٱلسَّيِّـَٔاتِ لَعَلَّهُمۡ يَرۡجِعُونَ

Kuma Mun rarraba su qabilu daban-daban a bayan qasa; a cikinsu akwai salihai, kuma daga cikinsu akwai koma bayan haka; kuma Mun jarrabe su da kyawawan abubuwa da munana, don su komo (zuwa hanya)



Surah: Suratul A’araf

Ayah : 169

فَخَلَفَ مِنۢ بَعۡدِهِمۡ خَلۡفٞ وَرِثُواْ ٱلۡكِتَٰبَ يَأۡخُذُونَ عَرَضَ هَٰذَا ٱلۡأَدۡنَىٰ وَيَقُولُونَ سَيُغۡفَرُ لَنَا وَإِن يَأۡتِهِمۡ عَرَضٞ مِّثۡلُهُۥ يَأۡخُذُوهُۚ أَلَمۡ يُؤۡخَذۡ عَلَيۡهِم مِّيثَٰقُ ٱلۡكِتَٰبِ أَن لَّا يَقُولُواْ عَلَى ٱللَّهِ إِلَّا ٱلۡحَقَّ وَدَرَسُواْ مَا فِيهِۗ وَٱلدَّارُ ٱلۡأٓخِرَةُ خَيۡرٞ لِّلَّذِينَ يَتَّقُونَۚ أَفَلَا تَعۡقِلُونَ

Sai waxansu bara-gurbi suka maye bayansu, sun gaji littafin (Attaura), suna karvar abin duniya, suna kuma cewa: “Za a gafarta mana.” Kuma idan wani abin duniyar irinsa ya zo musu sai su sake karvar sa. Shin yanzu ba a xauki alqawari daga wurinsu ba a cikin littafin (Attaura) cewa, kada su faxi wata magana game da Allah sai gaskiya, kuma sun karanta abin da yake cikinsa? Kuma lalle gidan lahira shi ne mafi alheri ga dukkan waxanda suke da taqawa. Shin ba za ku hankalta ba?



Surah: Suratul A’araf

Ayah : 170

وَٱلَّذِينَ يُمَسِّكُونَ بِٱلۡكِتَٰبِ وَأَقَامُواْ ٱلصَّلَوٰةَ إِنَّا لَا نُضِيعُ أَجۡرَ ٱلۡمُصۡلِحِينَ

Waxanda kuwa suke riqo da Littafi, kuma suke tsayar da salla, to lalle Mu ba ma tozarta ladan masu gyara



Surah: Suratul A’araf

Ayah : 171

۞وَإِذۡ نَتَقۡنَا ٱلۡجَبَلَ فَوۡقَهُمۡ كَأَنَّهُۥ ظُلَّةٞ وَظَنُّوٓاْ أَنَّهُۥ وَاقِعُۢ بِهِمۡ خُذُواْ مَآ ءَاتَيۡنَٰكُم بِقُوَّةٖ وَٱذۡكُرُواْ مَا فِيهِ لَعَلَّكُمۡ تَتَّقُونَ

Ka tuna kuma lokacin da Muka xaga dutse a samansu kamar girgije, kuma suka sakankance cewa zai rikito musu, (Muka ce da su): “Ku riqe abin da Muka ba ku da kyau, kuma ku tuna abin da yake cikinsa, don su zamo masu kiyaye dokokin Allah.”



Surah: Suratu Yunus

Ayah : 83

فَمَآ ءَامَنَ لِمُوسَىٰٓ إِلَّا ذُرِّيَّةٞ مِّن قَوۡمِهِۦ عَلَىٰ خَوۡفٖ مِّن فِرۡعَوۡنَ وَمَلَإِيْهِمۡ أَن يَفۡتِنَهُمۡۚ وَإِنَّ فِرۡعَوۡنَ لَعَالٖ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَإِنَّهُۥ لَمِنَ ٱلۡمُسۡرِفِينَ

To ba wanda ya yi imani da Musa sai wasu ‘yan samari daga mutanensa don tsoron kada Fir’auna da mutanensa su azabtar da su. Kuma lalle Fir’auna ya tabbata mai girman kai ne a bayan qasa. Lalle kuma shi yana cikin mavarnata



Surah: Suratu Yunus

Ayah : 84

وَقَالَ مُوسَىٰ يَٰقَوۡمِ إِن كُنتُمۡ ءَامَنتُم بِٱللَّهِ فَعَلَيۡهِ تَوَكَّلُوٓاْ إِن كُنتُم مُّسۡلِمِينَ

Musa kuma ya ce: “Ya ku mutanena, idan har kun yi imani da Allah, to a gare Shi kawai za ku dogara in kun kasance Musulmai



Surah: Suratu Yunus

Ayah : 85

فَقَالُواْ عَلَى ٱللَّهِ تَوَكَّلۡنَا رَبَّنَا لَا تَجۡعَلۡنَا فِتۡنَةٗ لِّلۡقَوۡمِ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Sai suka ce: “Ga Allah kaxai muka dogara. Ya Ubangijinmu, kada ka sanya mu zama fitina ga mutane azzalumai



Surah: Suratu Yunus

Ayah : 86

وَنَجِّنَا بِرَحۡمَتِكَ مِنَ ٱلۡقَوۡمِ ٱلۡكَٰفِرِينَ

“Ka kuma tserar da mu da rahamarka daga mutane kafirai.”



Surah: Suratu Yunus

Ayah : 87

وَأَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰ مُوسَىٰ وَأَخِيهِ أَن تَبَوَّءَا لِقَوۡمِكُمَا بِمِصۡرَ بُيُوتٗا وَٱجۡعَلُواْ بُيُوتَكُمۡ قِبۡلَةٗ وَأَقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَۗ وَبَشِّرِ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

Kuma Muka yi wa Musa wahayi shi da xan’uwansa cewa: “Ku tanadar wa mutanenku gidaje a Masar, ku kuma sanya gidajenku wurin salla.” Ka kuma yi wa muminai albishir (da samun nasara)



Surah: Suratu Yunus

Ayah : 88

وَقَالَ مُوسَىٰ رَبَّنَآ إِنَّكَ ءَاتَيۡتَ فِرۡعَوۡنَ وَمَلَأَهُۥ زِينَةٗ وَأَمۡوَٰلٗا فِي ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَا رَبَّنَا لِيُضِلُّواْ عَن سَبِيلِكَۖ رَبَّنَا ٱطۡمِسۡ عَلَىٰٓ أَمۡوَٰلِهِمۡ وَٱشۡدُدۡ عَلَىٰ قُلُوبِهِمۡ فَلَا يُؤۡمِنُواْ حَتَّىٰ يَرَوُاْ ٱلۡعَذَابَ ٱلۡأَلِيمَ

Musa kuma ya ce: “Ya Ubangijinmu, lalle Ka bai wa Fir’auna da mutanensa kayan ado da kuma dukiyoyi a rayuwar duniya; ya Ubangijimu, don su vatar (da jama’a) daga hanyarka; ya Ubangijimu, Ka shafe dukiyoyinsu Ka kuma qeqasar da zukatansu ba za su yi imani ba har sai sun ga azaba mai raxaxi.”