ٱقۡرَأۡ بِٱسۡمِ رَبِّكَ ٱلَّذِي خَلَقَ
Ka yi karatu da sunan Ubangijinka, Wanda Ya yi halitta
Share :
خَلَقَ ٱلۡإِنسَٰنَ مِنۡ عَلَقٍ
Ya halicci mutum daga gudan jini[1]
1- Watau bayan yana xigon maniyyi.
ٱقۡرَأۡ وَرَبُّكَ ٱلۡأَكۡرَمُ
Ka yi karatu alhali Ubangijinka Shi ne mafi karamci