Surah: Suratul Baqara

Ayah : 275

ٱلَّذِينَ يَأۡكُلُونَ ٱلرِّبَوٰاْ لَا يَقُومُونَ إِلَّا كَمَا يَقُومُ ٱلَّذِي يَتَخَبَّطُهُ ٱلشَّيۡطَٰنُ مِنَ ٱلۡمَسِّۚ ذَٰلِكَ بِأَنَّهُمۡ قَالُوٓاْ إِنَّمَا ٱلۡبَيۡعُ مِثۡلُ ٱلرِّبَوٰاْۗ وَأَحَلَّ ٱللَّهُ ٱلۡبَيۡعَ وَحَرَّمَ ٱلرِّبَوٰاْۚ فَمَن جَآءَهُۥ مَوۡعِظَةٞ مِّن رَّبِّهِۦ فَٱنتَهَىٰ فَلَهُۥ مَا سَلَفَ وَأَمۡرُهُۥٓ إِلَى ٱللَّهِۖ وَمَنۡ عَادَ فَأُوْلَـٰٓئِكَ أَصۡحَٰبُ ٱلنَّارِۖ هُمۡ فِيهَا خَٰلِدُونَ

Waxanda suke cin riba ba za su tashi ba (daga qaburburansu) sai kamar tashin mutumin da Shaixan yake bige shi da hauka. Hakan zai faru ne don sun ce: “Lalle kasuwanci kamar riba yake.” Kuma Allah Ya halatta kasuwanci, kuma Ya haramta riba. To duk wanda wa’azi ya zo masa daga wurin Ubangijinsa, sai ya daina, to abin da ya wuce a baya ya zama nasa, kuma al’amarinsa yana wurin Allah; wanda kuma ya sake komawa daga baya, to waxannan su ne ma’abota wuta, suna masu dawwama a cikinta



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 276

يَمۡحَقُ ٱللَّهُ ٱلرِّبَوٰاْ وَيُرۡبِي ٱلصَّدَقَٰتِۗ وَٱللَّهُ لَا يُحِبُّ كُلَّ كَفَّارٍ أَثِيمٍ

Allah Yana shafe albarkar riba, Yana kuma havaka sadaqa. Kuma Allah ba Ya son dukkan wani mai yawan kafircewa, mai yawan savo



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 277

إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ وَأَقَامُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَءَاتَوُاْ ٱلزَّكَوٰةَ لَهُمۡ أَجۡرُهُمۡ عِندَ رَبِّهِمۡ وَلَا خَوۡفٌ عَلَيۡهِمۡ وَلَا هُمۡ يَحۡزَنُونَ

Lalle waxanda suka yi imani kuma suka yi ayyuka nagari kuma suka tsayar da salla, kuma suka bayar da zakka, to suna da ladansu a wajen Ubangijinsu, kuma babu jin tsoro a gare su, kuma ba za su yi baqin ciki ba



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 278

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ ٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَذَرُواْ مَا بَقِيَ مِنَ ٱلرِّبَوٰٓاْ إِن كُنتُم مُّؤۡمِنِينَ

Ya ku waxanda suka yi imani, ku kiyaye dokokin Allah, kuma ku rabu da abin da ya yi ragowa na riba in har kun kasance muminai



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 279

فَإِن لَّمۡ تَفۡعَلُواْ فَأۡذَنُواْ بِحَرۡبٖ مِّنَ ٱللَّهِ وَرَسُولِهِۦۖ وَإِن تُبۡتُمۡ فَلَكُمۡ رُءُوسُ أَمۡوَٰلِكُمۡ لَا تَظۡلِمُونَ وَلَا تُظۡلَمُونَ

Idan kuwa ba ku aikata haka ba, to ku saurari wani yaqi daga Allah da Manzonsa; idan kuwa kun tuba, to uwar kuxin taku ce, ba za ku yi zalunci ba, ku ma kuma ba za a zalunce ku ba



Surah: Suratul Baqara

Ayah : 280

وَإِن كَانَ ذُو عُسۡرَةٖ فَنَظِرَةٌ إِلَىٰ مَيۡسَرَةٖۚ وَأَن تَصَدَّقُواْ خَيۡرٞ لَّكُمۡ إِن كُنتُمۡ تَعۡلَمُونَ

Kuma idan (mai cin bashin) ya kasance ma’abocin matsi, to sai a yi masa jinkiri zuwa lokacin da zai sami sauqi, kuma in da za ku yi sadaqa shi ya fi alheri a gare ku in kun kasance kuna da masaniya



Surah: Suratu Ali-Imran

Ayah : 130

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لَا تَأۡكُلُواْ ٱلرِّبَوٰٓاْ أَضۡعَٰفٗا مُّضَٰعَفَةٗۖ وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ لَعَلَّكُمۡ تُفۡلِحُونَ

Ya ku waxanda suka yi imani, kada ku ci riba ninki-ba-ninkin, kuma ku kiyaye dokokin Allah don ku rabauta



Surah: Suratun Nisa’i

Ayah : 161

وَأَخۡذِهِمُ ٱلرِّبَوٰاْ وَقَدۡ نُهُواْ عَنۡهُ وَأَكۡلِهِمۡ أَمۡوَٰلَ ٱلنَّاسِ بِٱلۡبَٰطِلِۚ وَأَعۡتَدۡنَا لِلۡكَٰفِرِينَ مِنۡهُمۡ عَذَابًا أَلِيمٗا

Da kuma cin riba da suke yi, tare da cewa an hana su cin ta, da kuma yadda suke cin dukiyar mutane ta hanyar cuta, Mun kuwa yi tanadin azaba mai raxaxi ga kafirai daga cikinsu



Surah: Suratur Rum

Ayah : 39

وَمَآ ءَاتَيۡتُم مِّن رِّبٗا لِّيَرۡبُوَاْ فِيٓ أَمۡوَٰلِ ٱلنَّاسِ فَلَا يَرۡبُواْ عِندَ ٱللَّهِۖ وَمَآ ءَاتَيۡتُم مِّن زَكَوٰةٖ تُرِيدُونَ وَجۡهَ ٱللَّهِ فَأُوْلَـٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡمُضۡعِفُونَ

Kuma abin da kuka bayar na riba don ya qaru a cikin dukiyoyin mutane, to ba ya qaruwa a wurin Allah[1]; abin kuma da kuka bayar na zakka kuna masu nufin Fuskar Allah, to waxannan su ne masu ninninka (ladansu)


1- Da yawa daga cikin malamai sun fassara wannan gavar da cewa, ana nufin wanda zai bayar da kyauta yana nufin a mayar masa da fiye da abin da ya bayar, to ba shi da lada a wurin Allah.