Surah: Suratul Baqara

Ayah : 119

إِنَّآ أَرۡسَلۡنَٰكَ بِٱلۡحَقِّ بَشِيرٗا وَنَذِيرٗاۖ وَلَا تُسۡـَٔلُ عَنۡ أَصۡحَٰبِ ٱلۡجَحِيمِ

Lalle Mu Mun aiko ka da gaskiya, kana mai albishir kuma kana mai gargaxi, ba kuma za a tambaye ka ba game da ‘yan wutar Jahima



Surah: Suratu Yunus

Ayah : 63

ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَكَانُواْ يَتَّقُونَ

(Su ne) waxanda suka yi imani kuma suka kasance masu kiyaye dokokin Allah



Surah: Suratu Yunus

Ayah : 64

لَهُمُ ٱلۡبُشۡرَىٰ فِي ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَا وَفِي ٱلۡأٓخِرَةِۚ لَا تَبۡدِيلَ لِكَلِمَٰتِ ٱللَّهِۚ ذَٰلِكَ هُوَ ٱلۡفَوۡزُ ٱلۡعَظِيمُ

Suna da albishir a rayuwar duniya da kuma ta lahira. Babu wani sauyi ga kalmomin Allah. Wannan shi ne babban rabo



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 89

وَيَوۡمَ نَبۡعَثُ فِي كُلِّ أُمَّةٖ شَهِيدًا عَلَيۡهِم مِّنۡ أَنفُسِهِمۡۖ وَجِئۡنَا بِكَ شَهِيدًا عَلَىٰ هَـٰٓؤُلَآءِۚ وَنَزَّلۡنَا عَلَيۡكَ ٱلۡكِتَٰبَ تِبۡيَٰنٗا لِّكُلِّ شَيۡءٖ وَهُدٗى وَرَحۡمَةٗ وَبُشۡرَىٰ لِلۡمُسۡلِمِينَ

Kuma (ka tuna) ranar da za Mu tayar wa kowace al’umma da mai ba da shaida a kansu daga jinsinsu, Mu kuma zo da kai (Annabi Muhammadu) shaida a kan waxannan (wato al’ummarka). Kuma Mun saukar maka da Littafi ne (wato Alqur’ani) don bayani ga kowanne abu, kuma shiriya da rahama da bushara ga Musulmi



Surah: Suratun Nahl

Ayah : 102

قُلۡ نَزَّلَهُۥ رُوحُ ٱلۡقُدُسِ مِن رَّبِّكَ بِٱلۡحَقِّ لِيُثَبِّتَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَهُدٗى وَبُشۡرَىٰ لِلۡمُسۡلِمِينَ

Ka ce: “Ruhul Qudusi (watau Mala’ika Jibrilu) ne ya saukar da shi daga Ubangijinka da gaskiya don ya tabbatar da waxanda suka yi imani (a kan dugadugansu), kuma shiriya ne da albishir ga Musulmai.”



Surah: Suratul Isra’i

Ayah : 9

إِنَّ هَٰذَا ٱلۡقُرۡءَانَ يَهۡدِي لِلَّتِي هِيَ أَقۡوَمُ وَيُبَشِّرُ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ ٱلَّذِينَ يَعۡمَلُونَ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ أَنَّ لَهُمۡ أَجۡرٗا كَبِيرٗا

Lalle wannan Alqur’anin yana shiryarwa ne ga (hanya) mafi miqewa, yana kuma yi wa muminai waxanda suke yin kyawawan ayyuka albishir cewa, lalle suna da lada mai girma



Surah: Suratul Furqan

Ayah : 22

يَوۡمَ يَرَوۡنَ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةَ لَا بُشۡرَىٰ يَوۡمَئِذٖ لِّلۡمُجۡرِمِينَ وَيَقُولُونَ حِجۡرٗا مَّحۡجُورٗا

Ranar da za su ga mala’iku[1] a wannan ranar babu wani farin ciki ga masu laifi, za kuma su riqa cewa: “(Albishir daga Allah) haramun ne abin haramtawa ne (a gare su)”


1- Watau ranar mutuwarsu ko a cikin qaburburansu da ranar da za a kora su domin yi musu hisabi.


Surah: Suratun Namli

Ayah : 1

طسٓۚ تِلۡكَ ءَايَٰتُ ٱلۡقُرۡءَانِ وَكِتَابٖ مُّبِينٍ

XA SIN[1]. Waxannan ayoyin Alqur’ani ne kuma Littafi mabayyani


1- Duba Suratul Baqara, aya ta 1, hashiya ta 8.


Surah: Suratun Namli

Ayah : 2

هُدٗى وَبُشۡرَىٰ لِلۡمُؤۡمِنِينَ

(Kuma) shiriya da albishir ne ga muminai



Surah: Suratuz Zumar

Ayah : 17

وَٱلَّذِينَ ٱجۡتَنَبُواْ ٱلطَّـٰغُوتَ أَن يَعۡبُدُوهَا وَأَنَابُوٓاْ إِلَى ٱللَّهِ لَهُمُ ٱلۡبُشۡرَىٰۚ فَبَشِّرۡ عِبَادِ

Waxanda kuwa suka nisanci bautar xagutu[1], suka kuma koma ga Allah, suna da albishir (na Aljanna). To ka yi wa bayina aibishir


1- Xagutu, shi ne duk wani abu da bawa ya qetare iyakar Allah ta hanyansa.


Surah: Suratul Hadid

Ayah : 12

يَوۡمَ تَرَى ٱلۡمُؤۡمِنِينَ وَٱلۡمُؤۡمِنَٰتِ يَسۡعَىٰ نُورُهُم بَيۡنَ أَيۡدِيهِمۡ وَبِأَيۡمَٰنِهِمۖ بُشۡرَىٰكُمُ ٱلۡيَوۡمَ جَنَّـٰتٞ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ خَٰلِدِينَ فِيهَاۚ ذَٰلِكَ هُوَ ٱلۡفَوۡزُ ٱلۡعَظِيمُ

(Ka tuna) ranar da za ka ga muminai maza da muminai mata haskensu yana tafiya ta gabansu da ta damansu, (ana cewa da su): “Albishirinku a wannan rana (su ne) gidajen Aljanna da qoramu suke gudana ta qarqashinsu, kuna masu dawwama a cikinsu. Wannan shi ne rabo mai girma.”