Surata: Suratud Dhuha

O versículo : 1

وَٱلضُّحَىٰ

Na rantse da lokacin hantsi



Surata: Suratud Dhuha

O versículo : 2

وَٱلَّيۡلِ إِذَا سَجَىٰ

Da kuma dare idan ya yi tsit[1]


1- Watau ya lulluve komai da duhunsa, mutane su shiga mazaunansu don su yi barci.


Surata: Suratud Dhuha

O versículo : 3

مَا وَدَّعَكَ رَبُّكَ وَمَا قَلَىٰ

Ubangijinka bai bar ka ba, kuma bai qi ka ba



Surata: Suratud Dhuha

O versículo : 4

وَلَلۡأٓخِرَةُ خَيۡرٞ لَّكَ مِنَ ٱلۡأُولَىٰ

Kuma lalle lahira ta fi maka alheri a kan duniya



Surata: Suratud Dhuha

O versículo : 5

وَلَسَوۡفَ يُعۡطِيكَ رَبُّكَ فَتَرۡضَىٰٓ

Kuma lalle Ubangijinka zai ba ka har sai ka yarda (da abin da Ya ba ka)



Surata: Suratud Dhuha

O versículo : 6

أَلَمۡ يَجِدۡكَ يَتِيمٗا فَـَٔاوَىٰ

Shin bai same ka maraya ba sai Ya haxa ka (da mai kula da kai)?



Surata: Suratud Dhuha

O versículo : 7

وَوَجَدَكَ ضَآلّٗا فَهَدَىٰ

Ya kuma same ka marashin shiriya Ya shiryar (da kai)?



Surata: Suratud Dhuha

O versículo : 8

وَوَجَدَكَ عَآئِلٗا فَأَغۡنَىٰ

Ya kuma same ka matalauci Ya wadata (ka)?



Surata: Suratud Dhuha

O versículo : 9

فَأَمَّا ٱلۡيَتِيمَ فَلَا تَقۡهَرۡ

Don haka maraya fa kada ka yi masa fin qarfi



Surata: Suratud Dhuha

O versículo : 10

وَأَمَّا ٱلسَّآئِلَ فَلَا تَنۡهَرۡ

Mai tambaya[1] kuma kada ka daka masa tsawa


1- Watau mai neman taimako saboda buqata, ko mai tambaya don neman sani.


Surata: Suratud Dhuha

O versículo : 11

وَأَمَّا بِنِعۡمَةِ رَبِّكَ فَحَدِّثۡ

Amma kuma game da ni’imar Ubangijinka sai ka ba da labari