Surata: Suratul Fajr

O versículo : 1

وَٱلۡفَجۡرِ

Na rantse da alfijir



Surata: Suratul Fajr

O versículo : 2

وَلَيَالٍ عَشۡرٖ

Da kuma darare goma[1]


1- Watau kwanaki goma na farkon watan Zulhijja.


Surata: Suratul Fajr

O versículo : 3

وَٱلشَّفۡعِ وَٱلۡوَتۡرِ

Da kuma abin da yake cika[1] da kuma mara[2]


1- Watau bibbiyu ko hurhuxu ko shida-shida da sauransu.


2- Watau xaya ko uku ko biyar da sauransu.


Surata: Suratul Fajr

O versículo : 4

وَٱلَّيۡلِ إِذَا يَسۡرِ

Da kuma dare lokacin da yake tafiya (cikin duhu)



Surata: Suratul Fajr

O versículo : 5

هَلۡ فِي ذَٰلِكَ قَسَمٞ لِّذِي حِجۡرٍ

Shin a game da waxannan akwai rantsuwa (mai gamsarwa) ga mai hankali[1]?


1- Watau duk mai hankali zai gamsu da waxannan rantse-rantse.


Surata: Suratul Fajr

O versículo : 6

أَلَمۡ تَرَ كَيۡفَ فَعَلَ رَبُّكَ بِعَادٍ

Shin ba ka ga yadda Ubangijinka Ya aikata ba ga Adawa?



Surata: Suratul Fajr

O versículo : 7

إِرَمَ ذَاتِ ٱلۡعِمَادِ

(Watau qabilar) Iramu ma’abociyar tsawo



Surata: Suratul Fajr

O versículo : 8

ٱلَّتِي لَمۡ يُخۡلَقۡ مِثۡلُهَا فِي ٱلۡبِلَٰدِ

Wadda ba a halicci irinta ba a cikin garuruwa (a tsananin qarfi)



Surata: Suratul Fajr

O versículo : 9

وَثَمُودَ ٱلَّذِينَ جَابُواْ ٱلصَّخۡرَ بِٱلۡوَادِ

Da kuma Samudawa waxanda suka fafe duwatsu a wurin da ake kira Wadil-Qura



Surata: Suratul Fajr

O versículo : 10

وَفِرۡعَوۡنَ ذِي ٱلۡأَوۡتَادِ

Da kuma Fir’auna ma’abocin turaku



Surata: Suratul Fajr

O versículo : 11

ٱلَّذِينَ طَغَوۡاْ فِي ٱلۡبِلَٰدِ

Waxanda suka yi xagawa a cikin garuruwa



Surata: Suratul Fajr

O versículo : 12

فَأَكۡثَرُواْ فِيهَا ٱلۡفَسَادَ

Suka kuma yawaita varna a cikinsu



Surata: Suratul Fajr

O versículo : 13

فَصَبَّ عَلَيۡهِمۡ رَبُّكَ سَوۡطَ عَذَابٍ

Sai Ubangijinka Ya saukar musu azaba mai tsanani



Surata: Suratul Fajr

O versículo : 14

إِنَّ رَبَّكَ لَبِٱلۡمِرۡصَادِ

Lalle Ubangijinka tabbas Yana nan a madakata[1]


1- Watau yana wurin da yake hangen xaukacin ayyukan bayinsa.


Surata: Suratul Fajr

O versículo : 15

فَأَمَّا ٱلۡإِنسَٰنُ إِذَا مَا ٱبۡتَلَىٰهُ رَبُّهُۥ فَأَكۡرَمَهُۥ وَنَعَّمَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّيٓ أَكۡرَمَنِ

Amma kuma mutum idan Ubangijinsa Ya jarrabe shi sai Ya karrama shi, Ya kuma yi masa ni’ima, sai ya ce: “Ubangijina Ya karrama ni.”



Surata: Suratul Fajr

O versículo : 16

وَأَمَّآ إِذَا مَا ٱبۡتَلَىٰهُ فَقَدَرَ عَلَيۡهِ رِزۡقَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّيٓ أَهَٰنَنِ

Amma kuma idan Ya jarrabe shi sai Ya quntata masa a arzikinsa, sai ya ce: “Ubangijina Ya wulaqanta ni.”



Surata: Suratul Fajr

O versículo : 17

كَلَّاۖ بَل لَّا تُكۡرِمُونَ ٱلۡيَتِيمَ

Faufau, ba haka ba ne; ku ba kwa karrama maraya ne



Surata: Suratul Fajr

O versículo : 18

وَلَا تَحَـٰٓضُّونَ عَلَىٰ طَعَامِ ٱلۡمِسۡكِينِ

Kuma ba kwa kwaxaitar da juna kan ciyar da miskinai



Surata: Suratul Fajr

O versículo : 19

وَتَأۡكُلُونَ ٱلتُّرَاثَ أَكۡلٗا لَّمّٗا

Kuma kuna cinye dukiyar gadon marayu mummunan ci



Surata: Suratul Fajr

O versículo : 20

وَتُحِبُّونَ ٱلۡمَالَ حُبّٗا جَمّٗا

Kuma kuna son dukiya so mai yawa



Surata: Suratul Fajr

O versículo : 21

كَلَّآۖ إِذَا دُكَّتِ ٱلۡأَرۡضُ دَكّٗا دَكّٗا

Ba haka ne ba, idan aka girgiza qasa matuqar girgiza



Surata: Suratul Fajr

O versículo : 22

وَجَآءَ رَبُّكَ وَٱلۡمَلَكُ صَفّٗا صَفّٗا

Ubangijinka kuma Ya zo[1] tare da mala’iku sahu-sahu


1- Watau don yin hukunci a tsakanin bayinsa.


Surata: Suratul Fajr

O versículo : 23

وَجِاْيٓءَ يَوۡمَئِذِۭ بِجَهَنَّمَۚ يَوۡمَئِذٖ يَتَذَكَّرُ ٱلۡإِنسَٰنُ وَأَنَّىٰ لَهُ ٱلذِّكۡرَىٰ

Aka kuma zo da Jahannama a wannan ranar. To fa a wannan ranar ne mutum zai tuna (sakacinsa), ta yaya wannan tunawar za ta yi masa amfani?



Surata: Suratul Fajr

O versículo : 24

يَقُولُ يَٰلَيۡتَنِي قَدَّمۡتُ لِحَيَاتِي

Zai ce: “Kaitona, ina ma da na gabatar (da ayyukan alheri) a rayuwata!”



Surata: Suratul Fajr

O versículo : 25

فَيَوۡمَئِذٖ لَّا يُعَذِّبُ عَذَابَهُۥٓ أَحَدٞ

To a wannan ranar ba wani xaya da zai yi azaba irin azabarsa (watau Allah)



Surata: Suratul Fajr

O versículo : 26

وَلَا يُوثِقُ وَثَاقَهُۥٓ أَحَدٞ

Ba kuma xaya da zai yi xauri irin xaurinsa



Surata: Suratul Fajr

O versículo : 27

يَـٰٓأَيَّتُهَا ٱلنَّفۡسُ ٱلۡمُطۡمَئِنَّةُ

(Za a ce): Ya kai wannan rai mai nutsuwa



Surata: Suratul Fajr

O versículo : 28

ٱرۡجِعِيٓ إِلَىٰ رَبِّكِ رَاضِيَةٗ مَّرۡضِيَّةٗ

Ka koma zuwa ga Ubangijinka kana mai yarda (da sakamako), abin yarda



Surata: Suratul Fajr

O versículo : 29

فَٱدۡخُلِي فِي عِبَٰدِي

Don haka ka shiga cikin bayina



Surata: Suratul Fajr

O versículo : 30

وَٱدۡخُلِي جَنَّتِي

Ka kuma shiga Aljannata