Surata: Suratul Buruj

O versículo : 1

وَٱلسَّمَآءِ ذَاتِ ٱلۡبُرُوجِ

Na rantse da sama ma’abociyar manziloli[1]


1- Watau manziloli na rana da wata da taurari.


Surata: Suratul Buruj

O versículo : 2

وَٱلۡيَوۡمِ ٱلۡمَوۡعُودِ

Da ranar da aka yi alqawarin zuwanta[1]


1- Watau ranar alqiyama.


Surata: Suratul Buruj

O versículo : 3

وَشَاهِدٖ وَمَشۡهُودٖ

Da mai shaida[1] da kuma abin yi wa shaida


1- Watau kamar Annabi da zai ba da shaida game da al’ummarsa.


Surata: Suratul Buruj

O versículo : 4

قُتِلَ أَصۡحَٰبُ ٱلۡأُخۡدُودِ

An la’anci ma’abota rami (na azabtar da muminai)[1]


1- Wani azzalumin sarki ne da aka yi a Najrana ta qasar Yaman kafin aiko Annabi () wanda aka haqa masa rami aka hura wuta, ya riqa jefa muminai a cikinsa yana qona su da ransu.


Surata: Suratul Buruj

O versículo : 5

ٱلنَّارِ ذَاتِ ٱلۡوَقُودِ

Na wuta mai ruruwa



Surata: Suratul Buruj

O versículo : 6

إِذۡ هُمۡ عَلَيۡهَا قُعُودٞ

Yayin da suke zaune a gefenta



Surata: Suratul Buruj

O versículo : 7

وَهُمۡ عَلَىٰ مَا يَفۡعَلُونَ بِٱلۡمُؤۡمِنِينَ شُهُودٞ

Alhali su suna kallon abin da suke aikata wa muminai



Surata: Suratul Buruj

O versículo : 8

وَمَا نَقَمُواْ مِنۡهُمۡ إِلَّآ أَن يُؤۡمِنُواْ بِٱللَّهِ ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡحَمِيدِ

Babu kuwa abin da suke tuhumar su da shi sai don kawai sun yi imani da Allah Mabuwayi, Sha-yabo



Surata: Suratul Buruj

O versículo : 9

ٱلَّذِي لَهُۥ مُلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ وَٱللَّهُ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ شَهِيدٌ

Wanda Yake da mulkin sammai da qasa. Allah kuma Mai ganin komai ne



Surata: Suratul Buruj

O versículo : 10

إِنَّ ٱلَّذِينَ فَتَنُواْ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ وَٱلۡمُؤۡمِنَٰتِ ثُمَّ لَمۡ يَتُوبُواْ فَلَهُمۡ عَذَابُ جَهَنَّمَ وَلَهُمۡ عَذَابُ ٱلۡحَرِيقِ

Lalle waxanda suka azabtar da muminai maza da muminai mata sannan ba su tuba ba, to suna da azabar Jahannama, suna kuma da azabar quna



Surata: Suratul Buruj

O versículo : 11

إِنَّ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ لَهُمۡ جَنَّـٰتٞ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُۚ ذَٰلِكَ ٱلۡفَوۡزُ ٱلۡكَبِيرُ

Lalle waxanda suka yi imani suka kuma yi ayyuka nagari suna da gidajen Aljanna waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu. Wannan kuwa shi ne babban rabo



Surata: Suratul Buruj

O versículo : 12

إِنَّ بَطۡشَ رَبِّكَ لَشَدِيدٌ

Lalle damqar Ubangijinka tabbas mai tsanani ce



Surata: Suratul Buruj

O versículo : 13

إِنَّهُۥ هُوَ يُبۡدِئُ وَيُعِيدُ

Lalle Shi ne Yake farar (da komai) Yake kuma dawo (da shi)



Surata: Suratul Buruj

O versículo : 14

وَهُوَ ٱلۡغَفُورُ ٱلۡوَدُودُ

Shi ne kuma Mai gafara, Mai qaunar (bayinsa na qwarai)



Surata: Suratul Buruj

O versículo : 15

ذُو ٱلۡعَرۡشِ ٱلۡمَجِيدُ

Ma’abocin Al’arshi Mai girma



Surata: Suratul Buruj

O versículo : 16

فَعَّالٞ لِّمَا يُرِيدُ

Mai aikata abin da Yake nufi



Surata: Suratul Buruj

O versículo : 17

هَلۡ أَتَىٰكَ حَدِيثُ ٱلۡجُنُودِ

Shin labarin rundunoni ya zo maka?



Surata: Suratul Buruj

O versículo : 18

فِرۡعَوۡنَ وَثَمُودَ

(Su ne) Fir’auna da Samudawa



Surata: Suratul Buruj

O versículo : 19

بَلِ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ فِي تَكۡذِيبٖ

A’a, su dai waxanda suka kafirta suna cikin qaryatawa ne



Surata: Suratul Buruj

O versículo : 20

وَٱللَّهُ مِن وَرَآئِهِم مُّحِيطُۢ

Allah kuwa Yana kewaye da su (da iliminsa)



Surata: Suratul Buruj

O versículo : 21

بَلۡ هُوَ قُرۡءَانٞ مَّجِيدٞ

A’a, shi dai Alqur’ani ne mai girma



Surata: Suratul Buruj

O versículo : 22

فِي لَوۡحٖ مَّحۡفُوظِۭ

A cikin Lauhul-Mahafuzu