Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 1

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلۡمُدَّثِّرُ

Ya kai mai lulluva[1]


1- Shi ne Annabi () wanda ya lulluva da tufafinsa don tsoron mala’ikan da ya yi idon huxu da shi a karon farko a kogon Hira.


Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 2

قُمۡ فَأَنذِرۡ

Tashi ka yi gargaxi



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 3

وَرَبَّكَ فَكَبِّرۡ

Kuma ka girmama Ubangijinka



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 4

وَثِيَابَكَ فَطَهِّرۡ

Ka kuma tsarkake tufafinka



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 5

وَٱلرُّجۡزَ فَٱهۡجُرۡ

Ka kuma qaurace wa (bautar) gumaka



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 6

وَلَا تَمۡنُن تَسۡتَكۡثِرُ

Kada kuma ka goranta wa (Ubangijinka) da ganin yawan (ayyukanka na qwarai)[1]


1- Watau kada yawansu ya ruxe shi har ya yi rauni wajen tsayuwa da ayyukan da’awa.


Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 7

وَلِرَبِّكَ فَٱصۡبِرۡ

Ka kuma yi haquri game da Ubangijinka



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 8

فَإِذَا نُقِرَ فِي ٱلنَّاقُورِ

To idan an busa qaho



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 9

فَذَٰلِكَ يَوۡمَئِذٖ يَوۡمٌ عَسِيرٌ

To wannan ranar rana ce mai tsanani



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 10

عَلَى ٱلۡكَٰفِرِينَ غَيۡرُ يَسِيرٖ

A kan kafirai, ba mai sauqi ba ce



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 11

ذَرۡنِي وَمَنۡ خَلَقۡتُ وَحِيدٗا

Ka bar Ni da wanda Na halitta shi kaxai[1]


1- Watau a cikin mahaifiyarsa ba tare da dukiya ko ‘ya’ya ba. Shi ne Al-Walidu xan Mugira wanda ya addabi Annabi ().


Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 12

وَجَعَلۡتُ لَهُۥ مَالٗا مَّمۡدُودٗا

Na kuma yi masa baiwa da dukiya maxuxuwa



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 13

وَبَنِينَ شُهُودٗا

Da kuma ‘ya’ya masu halartar (tarurruka tare da shi)



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 14

وَمَهَّدتُّ لَهُۥ تَمۡهِيدٗا

Na kuma shimfixa masa (kyakkyawar rayuwa) iyakar shinfixawa



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 15

ثُمَّ يَطۡمَعُ أَنۡ أَزِيدَ

Sannan yake kwaxayin in qara (masa)



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 16

كَلَّآۖ إِنَّهُۥ كَانَ لِأٓيَٰتِنَا عَنِيدٗا

Faufau! Lalle shi ya kasance mai tsaurin kai ne ga ayoyinmu



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 17

سَأُرۡهِقُهُۥ صَعُودًا

Ba da daxewa ba zan xora masa (azaba) mai matsananciyar wahala



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 18

إِنَّهُۥ فَكَّرَ وَقَدَّرَ

Lalle shi ya yi tunani, ya kuma auna (a ransa)



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 19

فَقُتِلَ كَيۡفَ قَدَّرَ

Sai aka la’ane shi, yaya ya yi irin wannan awon?



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 20

ثُمَّ قُتِلَ كَيۡفَ قَدَّرَ

Sannan aka kuma la’antar sa, yaya ya yi wannan awon?



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 21

ثُمَّ نَظَرَ

Sannan ya yi nazari



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 22

ثُمَّ عَبَسَ وَبَسَرَ

Sannan ya xaure fuska, ya kuma murtuke



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 23

ثُمَّ أَدۡبَرَ وَٱسۡتَكۡبَرَ

Sannan ya ba da baya (daga imani) ya kuma yi girman kai



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 24

فَقَالَ إِنۡ هَٰذَآ إِلَّا سِحۡرٞ يُؤۡثَرُ

Sai ya ce: “Wannan (Alqur’ani) ba komai ba ne sai sihiri da aka samo (daga wasu)



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 25

إِنۡ هَٰذَآ إِلَّا قَوۡلُ ٱلۡبَشَرِ

“Wannan ba komai ba ne sai magana irin ta mutane.”



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 26

سَأُصۡلِيهِ سَقَرَ

(Allah ya ce): Da sannu zan shigar da shi (wutar) Saqara



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 27

وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا سَقَرُ

Me ya sanar da kai abin da ake ce wa Saqara?



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 28

لَا تُبۡقِي وَلَا تَذَرُ

Ba ta ragewa kuma ba ta barin (komai)



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 29

لَوَّاحَةٞ لِّلۡبَشَرِ

Mai xaxxaye fata ce



Surata: Suratul Muddassir

O versículo : 30

عَلَيۡهَا تِسۡعَةَ عَشَرَ

Akwai (mala’iku) goma sha tara suna tsaron ta