Surata: Suratul Mulk

O versículo : 1

تَبَٰرَكَ ٱلَّذِي بِيَدِهِ ٱلۡمُلۡكُ وَهُوَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٌ

Wanda mulki yake a hannunsa alhairansa sun yawaita, kuma Shi Mai iko ne a kan komai



Surata: Suratul Mulk

O versículo : 2

ٱلَّذِي خَلَقَ ٱلۡمَوۡتَ وَٱلۡحَيَوٰةَ لِيَبۡلُوَكُمۡ أَيُّكُمۡ أَحۡسَنُ عَمَلٗاۚ وَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡغَفُورُ

Wanda Ya halicci mutuwa da rayuwa don Ya jarraba ku (Ya bayyana) wane ne a cikinku ya fi kyakkyawan aiki? Shi kuma Mabuwayi ne, Mai gafara



Surata: Suratul Mulk

O versículo : 3

ٱلَّذِي خَلَقَ سَبۡعَ سَمَٰوَٰتٖ طِبَاقٗاۖ مَّا تَرَىٰ فِي خَلۡقِ ٱلرَّحۡمَٰنِ مِن تَفَٰوُتٖۖ فَٱرۡجِعِ ٱلۡبَصَرَ هَلۡ تَرَىٰ مِن فُطُورٖ

Wanda Ya halicci sammai bakwai hawa-hawa; ba za ka ga wata tangarxa cikin halittar (Allah) Mai rahama ba. Ka maimaita dubanka, shin za ka ga wata tsaga?



Surata: Suratul Mulk

O versículo : 4

ثُمَّ ٱرۡجِعِ ٱلۡبَصَرَ كَرَّتَيۡنِ يَنقَلِبۡ إِلَيۡكَ ٱلۡبَصَرُ خَاسِئٗا وَهُوَ حَسِيرٞ

Sannan ka sake mayar da gani sau da yawa, ganin zai dawo maka a qasqance, shi kuma yana a dakushe (bai ga wata tsaga ba)



Surata: Suratul Mulk

O versículo : 5

وَلَقَدۡ زَيَّنَّا ٱلسَّمَآءَ ٱلدُّنۡيَا بِمَصَٰبِيحَ وَجَعَلۡنَٰهَا رُجُومٗا لِّلشَّيَٰطِينِۖ وَأَعۡتَدۡنَا لَهُمۡ عَذَابَ ٱلسَّعِيرِ

Kuma haqiqa Mun qawata saman duniya da taurari Muka sanya su kuma ababan jifan shaixanu[1]; Muka kuma tanadar musu azabar (wutar) Sa’ira


1- Watau jifar shaixanu masu qoqarin satar ji su qona su.


Surata: Suratul Mulk

O versículo : 6

وَلِلَّذِينَ كَفَرُواْ بِرَبِّهِمۡ عَذَابُ جَهَنَّمَۖ وَبِئۡسَ ٱلۡمَصِيرُ

Waxanda kuma suka kafirce wa Ubangijinsu suna da azabar Jahannama; makoma kuwa ta munana



Surata: Suratul Mulk

O versículo : 7

إِذَآ أُلۡقُواْ فِيهَا سَمِعُواْ لَهَا شَهِيقٗا وَهِيَ تَفُورُ

Idan aka jefa su a cikinta sai su ji kururuwarta, tana tafarfasa



Surata: Suratul Mulk

O versículo : 8

تَكَادُ تَمَيَّزُ مِنَ ٱلۡغَيۡظِۖ كُلَّمَآ أُلۡقِيَ فِيهَا فَوۡجٞ سَأَلَهُمۡ خَزَنَتُهَآ أَلَمۡ يَأۡتِكُمۡ نَذِيرٞ

Tana kusa da ta kekkece saboda tsananin fushi; duk sanda aka jefa wata tawaga a cikinta sai masu tsaron ta su tambaye su: “Shin mai gargaxi bai zo muku ba?”



Surata: Suratul Mulk

O versículo : 9

قَالُواْ بَلَىٰ قَدۡ جَآءَنَا نَذِيرٞ فَكَذَّبۡنَا وَقُلۡنَا مَا نَزَّلَ ٱللَّهُ مِن شَيۡءٍ إِنۡ أَنتُمۡ إِلَّا فِي ضَلَٰلٖ كَبِيرٖ

Sai su ce, “E, haka ne, haqiqa mai gargaxi ya zo mana, sai muka qaryata, muka kuma ce, Allah bai saukar da wani abu ba, ba kwa a kan komai sai vata mai girma.”



Surata: Suratul Mulk

O versículo : 10

وَقَالُواْ لَوۡ كُنَّا نَسۡمَعُ أَوۡ نَعۡقِلُ مَا كُنَّا فِيٓ أَصۡحَٰبِ ٱلسَّعِيرِ

Suka kuma ce: “Da mun kasance muna fahimta ko kuma muna hankalta, to da ba mu kasance cikin ‘yan (wutar) Sa’ira ba.”



Surata: Suratul Mulk

O versículo : 11

فَٱعۡتَرَفُواْ بِذَنۢبِهِمۡ فَسُحۡقٗا لِّأَصۡحَٰبِ ٱلسَّعِيرِ

Sai suka amsa laifinsu, sai (a ce da su): “Can dai da ‘yan (wutar) Sa’ira.”



Surata: Suratul Mulk

O versículo : 12

إِنَّ ٱلَّذِينَ يَخۡشَوۡنَ رَبَّهُم بِٱلۡغَيۡبِ لَهُم مَّغۡفِرَةٞ وَأَجۡرٞ كَبِيرٞ

Lalle waxanda suke tsoron Ubangijinsu ba tare da suna ganin sa ba, suna da gafara da kuma lada mai girma



Surata: Suratul Mulk

O versículo : 13

وَأَسِرُّواْ قَوۡلَكُمۡ أَوِ ٱجۡهَرُواْ بِهِۦٓۖ إِنَّهُۥ عَلِيمُۢ بِذَاتِ ٱلصُّدُورِ

Da ku voye zancenku ko ku bayyana shi, lalle Shi Masanin abin da yake cikin zukata ne



Surata: Suratul Mulk

O versículo : 14

أَلَا يَعۡلَمُ مَنۡ خَلَقَ وَهُوَ ٱللَّطِيفُ ٱلۡخَبِيرُ

Yanzu wanda ya yi halitta ba zai san ta ba? Shi ne kuma Mai tausasawa Masani



Surata: Suratul Mulk

O versículo : 15

هُوَ ٱلَّذِي جَعَلَ لَكُمُ ٱلۡأَرۡضَ ذَلُولٗا فَٱمۡشُواْ فِي مَنَاكِبِهَا وَكُلُواْ مِن رِّزۡقِهِۦۖ وَإِلَيۡهِ ٱلنُّشُورُ

Shi ne wanda Ya sanya muku qasa horarriya[1], saboda haka ku yi tafiya a cikin sasanninta kuma ku ci daga arzikinta; makoma kuwa zuwa gare Shi take


1- Watau ta zamanto mai sauqin zama da rayuwa a kanta, ba tare da tana tangal-tangal da su ba.


Surata: Suratul Mulk

O versículo : 16

ءَأَمِنتُم مَّن فِي ٱلسَّمَآءِ أَن يَخۡسِفَ بِكُمُ ٱلۡأَرۡضَ فَإِذَا هِيَ تَمُورُ

Yanzu kun amince cewa wanda Yake sama Ya kifar da qasa da ku, sai kawai ku gan ta tana ta tambal-tambal?



Surata: Suratul Mulk

O versículo : 17

أَمۡ أَمِنتُم مَّن فِي ٱلسَّمَآءِ أَن يُرۡسِلَ عَلَيۡكُمۡ حَاصِبٗاۖ فَسَتَعۡلَمُونَ كَيۡفَ نَذِيرِ

Ko kuma kun amince cewa wanda Yake sama Ya aiko muku da guguwa mai tsakwankwani? To da sannu za ku san yadda (sakamakon) gargaxina zai zama



Surata: Suratul Mulk

O versículo : 18

وَلَقَدۡ كَذَّبَ ٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِهِمۡ فَكَيۡفَ كَانَ نَكِيرِ

Haqiqa kuma waxanda suke gabaninku sun qaryata, to yaya (sakamakon) nuna qin amincewata ya zama?



Surata: Suratul Mulk

O versículo : 19

أَوَلَمۡ يَرَوۡاْ إِلَى ٱلطَّيۡرِ فَوۡقَهُمۡ صَـٰٓفَّـٰتٖ وَيَقۡبِضۡنَۚ مَا يُمۡسِكُهُنَّ إِلَّا ٱلرَّحۡمَٰنُۚ إِنَّهُۥ بِكُلِّ شَيۡءِۭ بَصِيرٌ

Shin ba sa ganin tsuntsaye a samansu suna shimfixa (fikafikansu) suna kuma rufe su? Ba wanda yake riqe da su sai (Allah) Mai rahama. Lalle Shi Mai ganin komai ne



Surata: Suratul Mulk

O versículo : 20

أَمَّنۡ هَٰذَا ٱلَّذِي هُوَ جُندٞ لَّكُمۡ يَنصُرُكُم مِّن دُونِ ٱلرَّحۡمَٰنِۚ إِنِ ٱلۡكَٰفِرُونَ إِلَّا فِي غُرُورٍ

Ko kuwa wace runduna ce kuke da ita da za ta taimaka muku ba (Allah) Mai rahama ba? Su dai kafirai ba sa kan komai sai ruxi



Surata: Suratul Mulk

O versículo : 21

أَمَّنۡ هَٰذَا ٱلَّذِي يَرۡزُقُكُمۡ إِنۡ أَمۡسَكَ رِزۡقَهُۥۚ بَل لَّجُّواْ فِي عُتُوّٖ وَنُفُورٍ

Ko kuwa wane ne zai arzuta ku idan (Allah) Ya riqe arzikinsa? A’a, kawai dai sun yi zurfi ne cikin taurin kai da fanxarewa



Surata: Suratul Mulk

O versículo : 22

أَفَمَن يَمۡشِي مُكِبًّا عَلَىٰ وَجۡهِهِۦٓ أَهۡدَىٰٓ أَمَّن يَمۡشِي سَوِيًّا عَلَىٰ صِرَٰطٖ مُّسۡتَقِيمٖ

Shin wanda yake tafiya a kife a kan fuskarsa shi ya fi zama a kan daidai ko kuma wanda yake tafiya a miqe kan hanya madaidaiciya?



Surata: Suratul Mulk

O versículo : 23

قُلۡ هُوَ ٱلَّذِيٓ أَنشَأَكُمۡ وَجَعَلَ لَكُمُ ٱلسَّمۡعَ وَٱلۡأَبۡصَٰرَ وَٱلۡأَفۡـِٔدَةَۚ قَلِيلٗا مَّا تَشۡكُرُونَ

Ka ce: “Shi ne (Allah) Wanda Ya fare ku Ya kuma sanya muku ji da gani da zukata; kaxan ne kawai kuke godewa.”



Surata: Suratul Mulk

O versículo : 24

قُلۡ هُوَ ٱلَّذِي ذَرَأَكُمۡ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَإِلَيۡهِ تُحۡشَرُونَ

Ka ce: “Shi ne wanda Ya halicce ku a kan qasa, kuma zuwa gare Shi za a tattara ku.”



Surata: Suratul Mulk

O versículo : 25

وَيَقُولُونَ مَتَىٰ هَٰذَا ٱلۡوَعۡدُ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ

Suna kuma cewa: “Yaushe ne wannan alqawarin, idan kun kasance masu gaskiya?”



Surata: Suratul Mulk

O versículo : 26

قُلۡ إِنَّمَا ٱلۡعِلۡمُ عِندَ ٱللَّهِ وَإِنَّمَآ أَنَا۠ نَذِيرٞ مُّبِينٞ

Ka ce: “Saninsa yana wurin Allah kawai, kuma ni kawai mai gargaxi ne mai bayyana (gargaxin).”



Surata: Suratul Mulk

O versículo : 27

فَلَمَّا رَأَوۡهُ زُلۡفَةٗ سِيٓـَٔتۡ وُجُوهُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ وَقِيلَ هَٰذَا ٱلَّذِي كُنتُم بِهِۦ تَدَّعُونَ

To lokacin da za su gan shi a kurkusa, sai fuskokin waxanda suka kafirce suka yi baqi, aka kuma ce: “Wannan ne abin da kuka kasance kuna neman zuwansa.”



Surata: Suratul Mulk

O versículo : 28

قُلۡ أَرَءَيۡتُمۡ إِنۡ أَهۡلَكَنِيَ ٱللَّهُ وَمَن مَّعِيَ أَوۡ رَحِمَنَا فَمَن يُجِيرُ ٱلۡكَٰفِرِينَ مِنۡ عَذَابٍ أَلِيمٖ

Ka ce: “Ku ba ni labari, idan Allah Ya hallaka ni da waxanda suke tare da ni, ko kuma Ya ji qan mu, to wane ne zai kare kafirai daga azaba mai raxaxi?”



Surata: Suratul Mulk

O versículo : 29

قُلۡ هُوَ ٱلرَّحۡمَٰنُ ءَامَنَّا بِهِۦ وَعَلَيۡهِ تَوَكَّلۡنَاۖ فَسَتَعۡلَمُونَ مَنۡ هُوَ فِي ضَلَٰلٖ مُّبِينٖ

Ka ce: “Shi ne (Allah) Mai rahama, mun yi imani da Shi, kuma a gare Shi muka dogara, to da sannu za ku san shin wane ne yake cikin vata mabayyani?”



Surata: Suratul Mulk

O versículo : 30

قُلۡ أَرَءَيۡتُمۡ إِنۡ أَصۡبَحَ مَآؤُكُمۡ غَوۡرٗا فَمَن يَأۡتِيكُم بِمَآءٖ مَّعِينِۭ

Ka ce: “Ku ba ni labari, idan ruwanku ya wayi gari a qafe, to wane ne zai zo muku da ruwa mai vuvvugowa?”