Surata: Suratur Rahman

O versículo : 1

ٱلرَّحۡمَٰنُ

(Allah) Mai rahama



Surata: Suratur Rahman

O versículo : 2

عَلَّمَ ٱلۡقُرۡءَانَ

Shi Ya koyar da Alqur’ani



Surata: Suratur Rahman

O versículo : 3

خَلَقَ ٱلۡإِنسَٰنَ

Ya halicci mutum



Surata: Suratur Rahman

O versículo : 4

عَلَّمَهُ ٱلۡبَيَانَ

Ya koyar da shi bayani



Surata: Suratur Rahman

O versículo : 5

ٱلشَّمۡسُ وَٱلۡقَمَرُ بِحُسۡبَانٖ

Rana da wata (suna tafiya) a tsare



Surata: Suratur Rahman

O versículo : 6

وَٱلنَّجۡمُ وَٱلشَّجَرُ يَسۡجُدَانِ

Tsirrai da bishiyoyi suna yin sujjada[1]


1- Watau tsirrai waxanda ba sa tashi tsaye da bishiyoyi masu tsayawa a kan sandunansu.


Surata: Suratur Rahman

O versículo : 7

وَٱلسَّمَآءَ رَفَعَهَا وَوَضَعَ ٱلۡمِيزَانَ

Sama kuma Ya xaga ta, Ya kuma kafa adalci



Surata: Suratur Rahman

O versículo : 8

أَلَّا تَطۡغَوۡاْ فِي ٱلۡمِيزَانِ

Don kada ku yi zalunci a abin awo



Surata: Suratur Rahman

O versículo : 9

وَأَقِيمُواْ ٱلۡوَزۡنَ بِٱلۡقِسۡطِ وَلَا تُخۡسِرُواْ ٱلۡمِيزَانَ

Kuma ku tabbatar da awo da adalci kada kuma ku tauye abin awo



Surata: Suratur Rahman

O versículo : 10

وَٱلۡأَرۡضَ وَضَعَهَا لِلۡأَنَامِ

Qasa kuma Ya yi ta saboda talikai



Surata: Suratur Rahman

O versículo : 11

فِيهَا فَٰكِهَةٞ وَٱلنَّخۡلُ ذَاتُ ٱلۡأَكۡمَامِ

A cikinta akwai abin marmari da dabinai ma’abota kwasfa



Surata: Suratur Rahman

O versículo : 12

وَٱلۡحَبُّ ذُو ٱلۡعَصۡفِ وَٱلرَّيۡحَانُ

Da qwayoyi ma’abota qaiqayi da kuma ganyaye masu qanshi



Surata: Suratur Rahman

O versículo : 13

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

To da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Surata: Suratur Rahman

O versículo : 14

خَلَقَ ٱلۡإِنسَٰنَ مِن صَلۡصَٰلٖ كَٱلۡفَخَّارِ

Ya halicci mutum daga busasshen tavo kamar kasko



Surata: Suratur Rahman

O versículo : 15

وَخَلَقَ ٱلۡجَآنَّ مِن مَّارِجٖ مِّن نَّارٖ

Ya kuma halicci aljani daga harshen wuta



Surata: Suratur Rahman

O versículo : 16

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Surata: Suratur Rahman

O versículo : 17

رَبُّ ٱلۡمَشۡرِقَيۡنِ وَرَبُّ ٱلۡمَغۡرِبَيۡنِ

Ubangijin mahudar rana biyu da mafaxarta biyu[1]


1- Watau a lokacin sanyi da kuma lokacin zafi.


Surata: Suratur Rahman

O versículo : 18

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Surata: Suratur Rahman

O versículo : 19

مَرَجَ ٱلۡبَحۡرَيۡنِ يَلۡتَقِيَانِ

Ya gudanar da koguna guda biyu suna haxuwa (da juna)



Surata: Suratur Rahman

O versículo : 20

بَيۡنَهُمَا بَرۡزَخٞ لَّا يَبۡغِيَانِ

A tsakaninsu (kuma) akwai wani shamaki da ya hana su shiga juna



Surata: Suratur Rahman

O versículo : 21

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Surata: Suratur Rahman

O versículo : 22

يَخۡرُجُ مِنۡهُمَا ٱللُّؤۡلُؤُ وَٱلۡمَرۡجَانُ

Lu’ulu’u da murjani suna fita daga cikinsu



Surata: Suratur Rahman

O versículo : 23

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Surata: Suratur Rahman

O versículo : 24

وَلَهُ ٱلۡجَوَارِ ٱلۡمُنشَـَٔاتُ فِي ٱلۡبَحۡرِ كَٱلۡأَعۡلَٰمِ

Jiragen ruwa kuma da aka yi su suna gudu a cikin kogi kamar manya-manyan duwatsu nasa ne



Surata: Suratur Rahman

O versículo : 25

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Surata: Suratur Rahman

O versículo : 26

كُلُّ مَنۡ عَلَيۡهَا فَانٖ

Dukkan wanda yake kanta (qasar) qararre ne



Surata: Suratur Rahman

O versículo : 27

وَيَبۡقَىٰ وَجۡهُ رَبِّكَ ذُو ٱلۡجَلَٰلِ وَٱلۡإِكۡرَامِ

Fuskar Ubangijinka kuwa Ma’abocin girma da karamci ne kawai take wanzuwa



Surata: Suratur Rahman

O versículo : 28

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?



Surata: Suratur Rahman

O versículo : 29

يَسۡـَٔلُهُۥ مَن فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ كُلَّ يَوۡمٍ هُوَ فِي شَأۡنٖ

Duk wanda yake cikin sammai da qasa yana roqon Sa. Kowane lokacin Shi a cikin wani sha’ani yake



Surata: Suratur Rahman

O versículo : 30

فَبِأَيِّ ءَالَآءِ رَبِّكُمَا تُكَذِّبَانِ

Da waxanne ni’imomin Ubangijinku ne (ku mutane da aljannu) kuke qaryatawa?