Surata: Suratuz Zariyat

O versículo : 1

وَٱلذَّـٰرِيَٰتِ ذَرۡوٗا

Na rantse da iskoki masu ta da qura



Surata: Suratuz Zariyat

O versículo : 2

فَٱلۡحَٰمِلَٰتِ وِقۡرٗا

Sannan da (giragizai) waxanda suke xauke da nauyin ruwa



Surata: Suratuz Zariyat

O versículo : 3

فَٱلۡجَٰرِيَٰتِ يُسۡرٗا

Da jiragen ruwa masu gudu a sauqaqe



Surata: Suratuz Zariyat

O versículo : 4

فَٱلۡمُقَسِّمَٰتِ أَمۡرًا

Da kuma mala’iku masu raba abubuwa



Surata: Suratuz Zariyat

O versículo : 5

إِنَّمَا تُوعَدُونَ لَصَادِقٞ

Lalle abin da ake yi muku alqawarinsa tabbas gaskiya ne



Surata: Suratuz Zariyat

O versículo : 6

وَإِنَّ ٱلدِّينَ لَوَٰقِعٞ

Kuma lalle sakamako tabbas mai afkuwa ne



Surata: Suratuz Zariyat

O versículo : 7

وَٱلسَّمَآءِ ذَاتِ ٱلۡحُبُكِ

Na rantse da sama ma’abociyar hanyoyi



Surata: Suratuz Zariyat

O versículo : 8

إِنَّكُمۡ لَفِي قَوۡلٖ مُّخۡتَلِفٖ

Lalle ku (mutanen Makka) tabbas kuna cikin magana mai sassavawa



Surata: Suratuz Zariyat

O versículo : 9

يُؤۡفَكُ عَنۡهُ مَنۡ أُفِكَ

Ana karkatar da wanda aka karkatar daga gare shi (Annabi ko Alqur’ani)



Surata: Suratuz Zariyat

O versículo : 10

قُتِلَ ٱلۡخَرَّـٰصُونَ

An la’anci maqaryata[1]


1- Watau game da Annabi () da kuma Alqur’ani.


Surata: Suratuz Zariyat

O versículo : 11

ٱلَّذِينَ هُمۡ فِي غَمۡرَةٖ سَاهُونَ

Waxanda suke rafkanannu a cikin jahilci



Surata: Suratuz Zariyat

O versículo : 12

يَسۡـَٔلُونَ أَيَّانَ يَوۡمُ ٱلدِّينِ

Suna tambayar yaushe ne ranar sakamako?



Surata: Suratuz Zariyat

O versículo : 13

يَوۡمَ هُمۡ عَلَى ٱلنَّارِ يُفۡتَنُونَ

A ranar da su za a azabtar da su kan wuta



Surata: Suratuz Zariyat

O versículo : 14

ذُوقُواْ فِتۡنَتَكُمۡ هَٰذَا ٱلَّذِي كُنتُم بِهِۦ تَسۡتَعۡجِلُونَ

(A ce da su): “Ku xanxani azabarku, wannan shi ne abin da kuka kasance kuna neman gaggautowarsa.”



Surata: Suratuz Zariyat

O versículo : 15

إِنَّ ٱلۡمُتَّقِينَ فِي جَنَّـٰتٖ وَعُيُونٍ

Lalle masu taqawa suna cikin gidajen Aljanna da idanuwan (ruwa)



Surata: Suratuz Zariyat

O versículo : 16

ءَاخِذِينَ مَآ ءَاتَىٰهُمۡ رَبُّهُمۡۚ إِنَّهُمۡ كَانُواْ قَبۡلَ ذَٰلِكَ مُحۡسِنِينَ

Suna masu kwasar abin da Ubangijinsu Ya ba su. Lalle su sun zamanto kafin wannan (ranar) masu kyautata ayyuka ne



Surata: Suratuz Zariyat

O versículo : 17

كَانُواْ قَلِيلٗا مِّنَ ٱلَّيۡلِ مَا يَهۡجَعُونَ

Sun kasance kaxan ne na dare suke bacci[1]


1- Watau sun kasance masu yawaita sallar dare.


Surata: Suratuz Zariyat

O versículo : 18

وَبِٱلۡأَسۡحَارِ هُمۡ يَسۡتَغۡفِرُونَ

A gefin asuba kuma su suna neman gafara



Surata: Suratuz Zariyat

O versículo : 19

وَفِيٓ أَمۡوَٰلِهِمۡ حَقّٞ لِّلسَّآئِلِ وَٱلۡمَحۡرُومِ

A cikin dukiyoyinsu kuma akwai wani haqqi na mai bara da mai kamewa daga yin ta



Surata: Suratuz Zariyat

O versículo : 20

وَفِي ٱلۡأَرۡضِ ءَايَٰتٞ لِّلۡمُوقِنِينَ

A cikin qasa kuma akwai ayoyi ga masu sakankancewa



Surata: Suratuz Zariyat

O versículo : 21

وَفِيٓ أَنفُسِكُمۡۚ أَفَلَا تُبۡصِرُونَ

Da kuma cikin kawunanku. Yanzu ba kwa lura ba?



Surata: Suratuz Zariyat

O versículo : 22

وَفِي ٱلسَّمَآءِ رِزۡقُكُمۡ وَمَا تُوعَدُونَ

A cikin sammai kuma akwai arzikinku da kuma abin da aka yi muku alkawarinsa



Surata: Suratuz Zariyat

O versículo : 23

فَوَرَبِّ ٱلسَّمَآءِ وَٱلۡأَرۡضِ إِنَّهُۥ لَحَقّٞ مِّثۡلَ مَآ أَنَّكُمۡ تَنطِقُونَ

To na rantse da Ubangijin sammai da qasa, lalle shi (abin da ake yi muku gargaxinsa) tabbas gaskiya ne kamar dai yadda kuke yin magana



Surata: Suratuz Zariyat

O versículo : 24

هَلۡ أَتَىٰكَ حَدِيثُ ضَيۡفِ إِبۡرَٰهِيمَ ٱلۡمُكۡرَمِينَ

Shin labarin baqin Ibrahimu masu girma[1] ya zo maka?


1- Su ne mala’iku da Allah ya aiko.


Surata: Suratuz Zariyat

O versículo : 25

إِذۡ دَخَلُواْ عَلَيۡهِ فَقَالُواْ سَلَٰمٗاۖ قَالَ سَلَٰمٞ قَوۡمٞ مُّنكَرُونَ

Lokacin da suka shiga wurinsa sai suka ce: “Muna maka sallama;” ya ce: “Aminci ya tabbata gare ku, (ku) mutane ne da ba sanannu ba.”



Surata: Suratuz Zariyat

O versículo : 26

فَرَاغَ إِلَىٰٓ أَهۡلِهِۦ فَجَآءَ بِعِجۡلٖ سَمِينٖ

Sai ya saxaxa da sauri zuwa ga iyalinsa, sai ya zo da wani xan maraqi mai mai



Surata: Suratuz Zariyat

O versículo : 27

فَقَرَّبَهُۥٓ إِلَيۡهِمۡ قَالَ أَلَا تَأۡكُلُونَ

Sai ya kusanta shi gare su, ya ce: “Yanzu ba za ku ci ba?”



Surata: Suratuz Zariyat

O versículo : 28

فَأَوۡجَسَ مِنۡهُمۡ خِيفَةٗۖ قَالُواْ لَا تَخَفۡۖ وَبَشَّرُوهُ بِغُلَٰمٍ عَلِيمٖ

(Da suka qi ci) sai ya tsorata da su, suka ce: “Kada ka tsorata;” suka kuma yi masa albishir da samun yaro mai ilimi[1]


1- Watau Annabi Ishaq ().


Surata: Suratuz Zariyat

O versículo : 29

فَأَقۡبَلَتِ ٱمۡرَأَتُهُۥ فِي صَرَّةٖ فَصَكَّتۡ وَجۡهَهَا وَقَالَتۡ عَجُوزٌ عَقِيمٞ

Sannan sai matarsa ta gabato su cikin wata qara, sai ta mari fuskarta ta ce: “Yanzu tsohuwa bakarara (ita ce za ta haihu?)”



Surata: Suratuz Zariyat

O versículo : 30

قَالُواْ كَذَٰلِكِ قَالَ رَبُّكِۖ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلۡحَكِيمُ ٱلۡعَلِيمُ

Suka ce, “Kamar haka Ubangijinki Ya ce, lalle Shi Mai hikima ne, Masani.”