Surata: Suratus Shu’ara

O versículo : 211

وَمَا يَنۢبَغِي لَهُمۡ وَمَا يَسۡتَطِيعُونَ

Kuma bai kamace su ba, ba kuma za su iya ba



Surata: Suratus Shu’ara

O versículo : 212

إِنَّهُمۡ عَنِ ٱلسَّمۡعِ لَمَعۡزُولُونَ

Lalle su ababen kangewa ne daga jin (wahayi)



Surata: Suratus Shu’ara

O versículo : 213

فَلَا تَدۡعُ مَعَ ٱللَّهِ إِلَٰهًا ءَاخَرَ فَتَكُونَ مِنَ ٱلۡمُعَذَّبِينَ

To kada ka bauta wa wani tare da Allah, sai ka zamanto daga waxanda za a yi wa azaba



Surata: Suratus Shu’ara

O versículo : 214

وَأَنذِرۡ عَشِيرَتَكَ ٱلۡأَقۡرَبِينَ

Kuma ka gargaxi danginka mafiya kusanci



Surata: Suratus Shu’ara

O versículo : 215

وَٱخۡفِضۡ جَنَاحَكَ لِمَنِ ٱتَّبَعَكَ مِنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ

Ka kuma tausasa ga wanda ya bi ka daga muminai



Surata: Suratus Shu’ara

O versículo : 216

فَإِنۡ عَصَوۡكَ فَقُلۡ إِنِّي بَرِيٓءٞ مِّمَّا تَعۡمَلُونَ

To idan suka sava maka sai ka ce: “Ni lalle ba ruwana da abin da kuke aikatawa.”



Surata: Suratus Shu’ara

O versículo : 217

وَتَوَكَّلۡ عَلَى ٱلۡعَزِيزِ ٱلرَّحِيمِ

Ka kuma dogara ga Mabuwayi, Mai rahama



Surata: Suratus Shu’ara

O versículo : 218

ٱلَّذِي يَرَىٰكَ حِينَ تَقُومُ

Wanda Yake ganin ka yayin da kake tashi (don yin salla)



Surata: Suratus Shu’ara

O versículo : 219

وَتَقَلُّبَكَ فِي ٱلسَّـٰجِدِينَ

Da kuma (yayin) jujjuyawarka cikin masu sujjada[1]


1- Watau masallata a sallar jam’i.


Surata: Suratus Shu’ara

O versículo : 220

إِنَّهُۥ هُوَ ٱلسَّمِيعُ ٱلۡعَلِيمُ

Haqiqa Shi Mai ji ne, Masani



Surata: Suratus Shu’ara

O versículo : 221

هَلۡ أُنَبِّئُكُمۡ عَلَىٰ مَن تَنَزَّلُ ٱلشَّيَٰطِينُ

Shin ba Na ba ku labari ba game da wanda shexanu suke saukar masa?



Surata: Suratus Shu’ara

O versículo : 222

تَنَزَّلُ عَلَىٰ كُلِّ أَفَّاكٍ أَثِيمٖ

Suna sauka ne a kan duk wani maqaryaci mai yawan laifi



Surata: Suratus Shu’ara

O versículo : 223

يُلۡقُونَ ٱلسَّمۡعَ وَأَكۡثَرُهُمۡ كَٰذِبُونَ

Suna jefa wa (bokaye) abin da suka sato jinsa, yawancinsu kuwa maqaryata ne



Surata: Suratus Shu’ara

O versículo : 224

وَٱلشُّعَرَآءُ يَتَّبِعُهُمُ ٱلۡغَاوُۥنَ

Mawaqa kuwa vatattu ne suke bin su



Surata: Suratus Shu’ara

O versículo : 225

أَلَمۡ تَرَ أَنَّهُمۡ فِي كُلِّ وَادٖ يَهِيمُونَ

Ba ka ga cewa su kutsawa suke yi cikin kowanne kwari ba[1]?


1- Watau suna kutsawa cikin kowane saqo-saqo na waqe-waqe, wani lokaci ta hanyar yabo, wani lokaci kuma ya hanyar zambo ko alfahari, su faxi qarya da gaskiya.


Surata: Suratus Shu’ara

O versículo : 226

وَأَنَّهُمۡ يَقُولُونَ مَا لَا يَفۡعَلُونَ

Lalle kuma suna faxar abin da ba sa aikatawa



Surata: Suratus Shu’ara

O versículo : 227

إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ وَذَكَرُواْ ٱللَّهَ كَثِيرٗا وَٱنتَصَرُواْ مِنۢ بَعۡدِ مَا ظُلِمُواْۗ وَسَيَعۡلَمُ ٱلَّذِينَ ظَلَمُوٓاْ أَيَّ مُنقَلَبٖ يَنقَلِبُونَ

Sai dai waxanda suka yi imani kuma suka yi aiki nagari, kuma suka ambaci Allah da yawa, suka kuma yi sakayya bayan an zalunce su[1]. Waxanda suka yi zalunci kuwa ba da daxewa ba za su san kowace makomar za su koma


1- Watau mawaqan Musulmi waxanda suke mayar da martani a kan mawaqan kafirai masu sukan Musulunci.