Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 121

وَإِذۡ غَدَوۡتَ مِنۡ أَهۡلِكَ تُبَوِّئُ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ مَقَٰعِدَ لِلۡقِتَالِۗ وَٱللَّهُ سَمِيعٌ عَلِيمٌ

Kuma ka tuna lokacin da ka yi sammako daga wajen iyalinka, ka je kana shirya wa muminai wuraren tsayuwarsu don yaqi[1]. Allah kuwa Mai ji ne, Masani


1- Watau lokacin fitarsa zuwa yaqin Uhudu shekara ta uku bayan hijira.


Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 122

إِذۡ هَمَّت طَّآئِفَتَانِ مِنكُمۡ أَن تَفۡشَلَا وَٱللَّهُ وَلِيُّهُمَاۗ وَعَلَى ٱللَّهِ فَلۡيَتَوَكَّلِ ٱلۡمُؤۡمِنُونَ

Tuna lokacin da waxansu qungiyoyi guda biyu daga cikinku suka yi niyyar su ja da baya[1], amma Allah ne Majivincin lamarinsu. Sai muminai su dogara ga Allah kaxai


1- Qungiyoyin muminai biyu da suka yi nufin su janye daga wannan yaqi, su ne qabilun Banu Salima da na Banu Harisa, sai dai kuma Allah ya kafe dugadugansu.


Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 123

وَلَقَدۡ نَصَرَكُمُ ٱللَّهُ بِبَدۡرٖ وَأَنتُمۡ أَذِلَّةٞۖ فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ لَعَلَّكُمۡ تَشۡكُرُونَ

Kuma tabbas haqiqa Allah Ya taimake ku a (yaqin) Badar, alhalin kuna raunana, to ku ji tsoron Allah don ku zamanto masu godiya a gare Shi



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 124

إِذۡ تَقُولُ لِلۡمُؤۡمِنِينَ أَلَن يَكۡفِيَكُمۡ أَن يُمِدَّكُمۡ رَبُّكُم بِثَلَٰثَةِ ءَالَٰفٖ مِّنَ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةِ مُنزَلِينَ

Ka tuna lokacin da kake ce wa muminai: “Shin bai ishe ku ba idan Ubangijinku Ya kawo muku agajin mala’iku dubu uku waxanda za a saukar da su (daga sama)?”



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 125

بَلَىٰٓۚ إِن تَصۡبِرُواْ وَتَتَّقُواْ وَيَأۡتُوكُم مِّن فَوۡرِهِمۡ هَٰذَا يُمۡدِدۡكُمۡ رَبُّكُم بِخَمۡسَةِ ءَالَٰفٖ مِّنَ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةِ مُسَوِّمِينَ

Haka ne, idan har za ku yi haquri, kuma ku yi taqawa, kuma (kafirai) suka auko muku cikin gaggawa a wannan lokacin, to Ubangijinku zai qaro muku agaji da mala’iku dubu biyar masu alamomi



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 126

وَمَا جَعَلَهُ ٱللَّهُ إِلَّا بُشۡرَىٰ لَكُمۡ وَلِتَطۡمَئِنَّ قُلُوبُكُم بِهِۦۗ وَمَا ٱلنَّصۡرُ إِلَّا مِنۡ عِندِ ٱللَّهِ ٱلۡعَزِيزِ ٱلۡحَكِيمِ

Kuma Allah bai sanya wannan ba sai don albishir a gare ku, kuma domin zukatanku su nutsu da shi. Kuma nasara ba ta zuwa daga kowa sai daga Allah Mabuwayi, Mai hikima



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 127

لِيَقۡطَعَ طَرَفٗا مِّنَ ٱلَّذِينَ كَفَرُوٓاْ أَوۡ يَكۡبِتَهُمۡ فَيَنقَلِبُواْ خَآئِبِينَ

Domin Ya karya lagon wani vangare na kafirai ko Ya qasqantar da su, sai su juya da baya suna tavavvu



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 128

لَيۡسَ لَكَ مِنَ ٱلۡأَمۡرِ شَيۡءٌ أَوۡ يَتُوبَ عَلَيۡهِمۡ أَوۡ يُعَذِّبَهُمۡ فَإِنَّهُمۡ ظَٰلِمُونَ

Ba ka da komai cikin lamarin, ko dai (Allah) Ya karvi tubansu, ko Ya yi musu azaba, lalle su dai azzalumai ne



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 129

وَلِلَّهِ مَا فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَمَا فِي ٱلۡأَرۡضِۚ يَغۡفِرُ لِمَن يَشَآءُ وَيُعَذِّبُ مَن يَشَآءُۚ وَٱللَّهُ غَفُورٞ رَّحِيمٞ

Kuma abin da yake cikin sammai da kuma abin da yake cikin qasa na Allah ne. Yana yin gafara ga wanda Ya ga dama, Yana kuma yin azaba ga wanda Ya ga dama. Kuma Allah Mai gafara ne, Mai jin qai



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 130

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لَا تَأۡكُلُواْ ٱلرِّبَوٰٓاْ أَضۡعَٰفٗا مُّضَٰعَفَةٗۖ وَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ لَعَلَّكُمۡ تُفۡلِحُونَ

Ya ku waxanda suka yi imani, kada ku ci riba ninki-ba-ninkin, kuma ku kiyaye dokokin Allah don ku rabauta



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 131

وَٱتَّقُواْ ٱلنَّارَ ٱلَّتِيٓ أُعِدَّتۡ لِلۡكَٰفِرِينَ

Kuma ku kiyayi wuta wadda aka riga aka yi tanadinta domin kafirai



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 132

وَأَطِيعُواْ ٱللَّهَ وَٱلرَّسُولَ لَعَلَّكُمۡ تُرۡحَمُونَ

Kuma ku bi Allah da Manzo don a ji qan ku (a ranar tashin alqiyama)



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 133

۞وَسَارِعُوٓاْ إِلَىٰ مَغۡفِرَةٖ مِّن رَّبِّكُمۡ وَجَنَّةٍ عَرۡضُهَا ٱلسَّمَٰوَٰتُ وَٱلۡأَرۡضُ أُعِدَّتۡ لِلۡمُتَّقِينَ

Kuma ku yi gaggawa zuwa ga neman gafara ta musamman daga wajen Ubangijinku, da kuma Aljanna wadda faxinta yake daidai da sammai da qasa, an yi tanadinta domin masu taqawa



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 134

ٱلَّذِينَ يُنفِقُونَ فِي ٱلسَّرَّآءِ وَٱلضَّرَّآءِ وَٱلۡكَٰظِمِينَ ٱلۡغَيۡظَ وَٱلۡعَافِينَ عَنِ ٱلنَّاسِۗ وَٱللَّهُ يُحِبُّ ٱلۡمُحۡسِنِينَ

(Su ne) waxanda suke ciyarwa a cikin halin yalwa da halin qunci, kuma masu voye fushi kuma masu yin afuwa ga mutane. Allah kuwa Yana son masu kyautatawa



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 135

وَٱلَّذِينَ إِذَا فَعَلُواْ فَٰحِشَةً أَوۡ ظَلَمُوٓاْ أَنفُسَهُمۡ ذَكَرُواْ ٱللَّهَ فَٱسۡتَغۡفَرُواْ لِذُنُوبِهِمۡ وَمَن يَغۡفِرُ ٱلذُّنُوبَ إِلَّا ٱللَّهُ وَلَمۡ يُصِرُّواْ عَلَىٰ مَا فَعَلُواْ وَهُمۡ يَعۡلَمُونَ

(Su ne) kuma waxanda idan sun aikata mummunan aiki, ko suka zalunci kansu, nan take sai su tuna da Allah, sai su nemi gafarar zunubansu. Wane ne kuwa mai gafarta zunubbai in ba Allah ba? Kuma ba sa zarcewa a kan abin da suka yi, alhali suna sane



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 136

أُوْلَـٰٓئِكَ جَزَآؤُهُم مَّغۡفِرَةٞ مِّن رَّبِّهِمۡ وَجَنَّـٰتٞ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ خَٰلِدِينَ فِيهَاۚ وَنِعۡمَ أَجۡرُ ٱلۡعَٰمِلِينَ

Waxannan sakamakonsu shi ne gafara ta musamman daga Ubangijinsu, da gidajen Aljanna waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu, suna masu dawwama a cikinsu. Kuma madalla da sakamakon masu aiki



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 137

قَدۡ خَلَتۡ مِن قَبۡلِكُمۡ سُنَنٞ فَسِيرُواْ فِي ٱلۡأَرۡضِ فَٱنظُرُواْ كَيۡفَ كَانَ عَٰقِبَةُ ٱلۡمُكَذِّبِينَ

Haqiqa sunnoni (na Allah) sun riga sun shuxe gabaninku, to sai ku yi tafiya cikin qasa, sai ku duba ku ga yaya qarshen masu qaryatawa ya zama?



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 138

هَٰذَا بَيَانٞ لِّلنَّاسِ وَهُدٗى وَمَوۡعِظَةٞ لِّلۡمُتَّقِينَ

Wannan bayani ne don mutane, kuma shiriya ce da kuma wa’azi ga masu taqawa



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 139

وَلَا تَهِنُواْ وَلَا تَحۡزَنُواْ وَأَنتُمُ ٱلۡأَعۡلَوۡنَ إِن كُنتُم مُّؤۡمِنِينَ

Kuma kada ku yi rauni, kada kuma ku yi baqin ciki, kuma ku ne mafiya xaukaka in dai har kun kasance muminai



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 140

إِن يَمۡسَسۡكُمۡ قَرۡحٞ فَقَدۡ مَسَّ ٱلۡقَوۡمَ قَرۡحٞ مِّثۡلُهُۥۚ وَتِلۡكَ ٱلۡأَيَّامُ نُدَاوِلُهَا بَيۡنَ ٱلنَّاسِ وَلِيَعۡلَمَ ٱللَّهُ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَيَتَّخِذَ مِنكُمۡ شُهَدَآءَۗ وَٱللَّهُ لَا يُحِبُّ ٱلظَّـٰلِمِينَ

Idan ma wani miki ne ya same ku a jiki, to haqiqa miki irinsa ya sami mutanen (Makka). Kuma waxannan kwanaki ne da muke jujjuya su tsakanin mutane domin Allah Ya bayyanar da waxanda suka yi imani (a gane su), kuma Ya riqi shahidai a cikinku. Allah kuwa ba Ya son azzalumai



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 141

وَلِيُمَحِّصَ ٱللَّهُ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَيَمۡحَقَ ٱلۡكَٰفِرِينَ

Kuma don Allah Ya tace waxanda suka yi imani, kuma don Ya halakar da kafirai



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 142

أَمۡ حَسِبۡتُمۡ أَن تَدۡخُلُواْ ٱلۡجَنَّةَ وَلَمَّا يَعۡلَمِ ٱللَّهُ ٱلَّذِينَ جَٰهَدُواْ مِنكُمۡ وَيَعۡلَمَ ٱلصَّـٰبِرِينَ

Yanzu kuna tsammanin za ku shiga Aljanna ne alhalin Allah bai bayyanar da masu yin jihadi daga cikinku ba, kuma bai bayyanar da masu haquri ba



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 143

وَلَقَدۡ كُنتُمۡ تَمَنَّوۡنَ ٱلۡمَوۡتَ مِن قَبۡلِ أَن تَلۡقَوۡهُ فَقَدۡ رَأَيۡتُمُوهُ وَأَنتُمۡ تَنظُرُونَ

Kuma haqiqa kun kasance a da can kuna ta burin mutuwa tun kafin ku gamu da ita, to haqiqa (a yau) ga ta kun gan ta alhali kuna kallo da ido



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 144

وَمَا مُحَمَّدٌ إِلَّا رَسُولٞ قَدۡ خَلَتۡ مِن قَبۡلِهِ ٱلرُّسُلُۚ أَفَإِيْن مَّاتَ أَوۡ قُتِلَ ٱنقَلَبۡتُمۡ عَلَىٰٓ أَعۡقَٰبِكُمۡۚ وَمَن يَنقَلِبۡ عَلَىٰ عَقِبَيۡهِ فَلَن يَضُرَّ ٱللَّهَ شَيۡـٔٗاۚ وَسَيَجۡزِي ٱللَّهُ ٱلشَّـٰكِرِينَ

Kuma Muhammadu ba wani ne ba face Manzo kaxai wanda manzanni haqiqa sun shuxe gabaninsa. Shin yanzu idan ya mutu ko aka kashe shi, sai ku juya baya a kan dugaduganku? Duk kuwa wanda ya juya baya a kan dugadugansa to ba zai cuci Allah da komai ba. Kuma da sannu Allah zai saka wa masu godiya



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 145

وَمَا كَانَ لِنَفۡسٍ أَن تَمُوتَ إِلَّا بِإِذۡنِ ٱللَّهِ كِتَٰبٗا مُّؤَجَّلٗاۗ وَمَن يُرِدۡ ثَوَابَ ٱلدُّنۡيَا نُؤۡتِهِۦ مِنۡهَا وَمَن يُرِدۡ ثَوَابَ ٱلۡأٓخِرَةِ نُؤۡتِهِۦ مِنۡهَاۚ وَسَنَجۡزِي ٱلشَّـٰكِرِينَ

Kuma babu wani rai da zai mutu sai da izinin Allah, rubutaccen abu ne qayyadajje. Kuma duk wanda yake nufin sakamakon duniya, za Mu ba shi daga gare ta, wanda kuma yake nufin sakamakon lahira, to za Mu ba shi daga gare ta. Kuma da sannu za Mu saka ma masu godiya



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 146

وَكَأَيِّن مِّن نَّبِيّٖ قَٰتَلَ مَعَهُۥ رِبِّيُّونَ كَثِيرٞ فَمَا وَهَنُواْ لِمَآ أَصَابَهُمۡ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِ وَمَا ضَعُفُواْ وَمَا ٱسۡتَكَانُواْۗ وَٱللَّهُ يُحِبُّ ٱلصَّـٰبِرِينَ

Kuma sau da yawa an sami wani annabi (daga cikin annabawa), mabiya masu yawa sun yi yaqi tare da shi, amma ba su tava yin rauni ba saboda abin da ya same su a tafarkin Allah, kuma ba su tava yin ragwanci ba, kuma ba su tava miqa wuya ba. Kuma Allah Yana son masu haquri



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 147

وَمَا كَانَ قَوۡلَهُمۡ إِلَّآ أَن قَالُواْ رَبَّنَا ٱغۡفِرۡ لَنَا ذُنُوبَنَا وَإِسۡرَافَنَا فِيٓ أَمۡرِنَا وَثَبِّتۡ أَقۡدَامَنَا وَٱنصُرۡنَا عَلَى ٱلۡقَوۡمِ ٱلۡكَٰفِرِينَ

Kuma ba su da wata magana sai faxar: “Ya Ubangijinmu, Ka gafarta mana zunubanmu da qetare iyakar da muka yi cikin lamurranmu, kuma Ka tabbatar da dugaduganmu, kuma Ka taimake mu a kan mutunen da suke kafirai



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 148

فَـَٔاتَىٰهُمُ ٱللَّهُ ثَوَابَ ٱلدُّنۡيَا وَحُسۡنَ ثَوَابِ ٱلۡأٓخِرَةِۗ وَٱللَّهُ يُحِبُّ ٱلۡمُحۡسِنِينَ

Sai Allah Ya ba su ladan duniya da kyakkyawan lada na lahira. Kuma Allah Yana son masu kyautatawa



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 149

يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُوٓاْ إِن تُطِيعُواْ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ يَرُدُّوكُمۡ عَلَىٰٓ أَعۡقَٰبِكُمۡ فَتَنقَلِبُواْ خَٰسِرِينَ

Ya ku waxanda suka yi imani, idan har kuka yi biyayya ga waxanda suka kafirta, to za su mayar da ku baya a kan dugaduganku, sai ku juya kuna hasararru



Surata: Suratu Ali-Imran

O versículo : 150

بَلِ ٱللَّهُ مَوۡلَىٰكُمۡۖ وَهُوَ خَيۡرُ ٱلنَّـٰصِرِينَ

A’a, Allah Shi ne Majivincin lamarinku; kuma Shi ne Fiyayyen masu taimako