Surata: Suratun Najm

O versículo : 1

وَٱلنَّجۡمِ إِذَا هَوَىٰ

Na rantse da tauraro yayin da ya faxi



Surata: Suratun Najm

O versículo : 2

مَا ضَلَّ صَاحِبُكُمۡ وَمَا غَوَىٰ

Mutumin naku[1] bai vata ba, kuma bai kauce hanya ba


1- Watau Annabi Muhammadu ().


Surata: Suratun Najm

O versículo : 3

وَمَا يَنطِقُ عَنِ ٱلۡهَوَىٰٓ

Kuma ba ya yin magana bisa son rai



Surata: Suratun Najm

O versículo : 4

إِنۡ هُوَ إِلَّا وَحۡيٞ يُوحَىٰ

Shi (Alqur’ani) ba wani abu ne ba in ban da wahayi da ake yiwo (masa)



Surata: Suratun Najm

O versículo : 5

عَلَّمَهُۥ شَدِيدُ ٱلۡقُوَىٰ

Mai tsananin qarfi ne (watau Jibrilu) ya koyar da shi



Surata: Suratun Najm

O versículo : 6

ذُو مِرَّةٖ فَٱسۡتَوَىٰ

Mai kyawawan halitta ne, sai ya daidaita



Surata: Suratun Najm

O versículo : 7

وَهُوَ بِٱلۡأُفُقِ ٱلۡأَعۡلَىٰ

Alhali kuwa shi yana a sassa na can sama



Surata: Suratun Najm

O versículo : 8

ثُمَّ دَنَا فَتَدَلَّىٰ

Sannan sai ya kusanto, sai ya qara matsawa[1]


1- Watau Jibrilu () ya kusanto Annabi () ya matso kusa don yi masa wahayi.


Surata: Suratun Najm

O versículo : 9

فَكَانَ قَابَ قَوۡسَيۡنِ أَوۡ أَدۡنَىٰ

Sai ya kasance kamar kusancin kamu biyu ko qasa da haka



Surata: Suratun Najm

O versículo : 10

فَأَوۡحَىٰٓ إِلَىٰ عَبۡدِهِۦ مَآ أَوۡحَىٰ

Sannan (Allah) Ya yiyo wahayin abin da Ya yi wahayi zuwa ga Bawansa (Ma’aiki)



Surata: Suratun Najm

O versículo : 11

مَا كَذَبَ ٱلۡفُؤَادُ مَا رَأَىٰٓ

Zuciyar (ta Ma’aiki) ba ta yi qaryar abin da ta gani ba



Surata: Suratun Najm

O versículo : 12

أَفَتُمَٰرُونَهُۥ عَلَىٰ مَا يَرَىٰ

Yanzu kwa riqa jayayya da shi kan abin da yake gani?



Surata: Suratun Najm

O versículo : 13

وَلَقَدۡ رَءَاهُ نَزۡلَةً أُخۡرَىٰ

Haqiqa ya gan shi (Jibrilu) a wani karon ma[1]


1- Watau lokacin Isra’i da Mi’iraji, inda ya gan shi a halittarsa ta asali.


Surata: Suratun Najm

O versículo : 14

عِندَ سِدۡرَةِ ٱلۡمُنتَهَىٰ

A wurin Magaryar tuqewa



Surata: Suratun Najm

O versículo : 15

عِندَهَا جَنَّةُ ٱلۡمَأۡوَىٰٓ

A wurinta ne Aljannar makoma take



Surata: Suratun Najm

O versículo : 16

إِذۡ يَغۡشَى ٱلسِّدۡرَةَ مَا يَغۡشَىٰ

A yayin da abin da ya lulluve Magaryar (na ban mamaki) ya lulluve ta



Surata: Suratun Najm

O versículo : 17

مَا زَاغَ ٱلۡبَصَرُ وَمَا طَغَىٰ

Ganin (nasa) bai karkace ba, kuma bai zarme ba



Surata: Suratun Najm

O versículo : 18

لَقَدۡ رَأَىٰ مِنۡ ءَايَٰتِ رَبِّهِ ٱلۡكُبۡرَىٰٓ

Haqiqa ya ga wasu ayoyin Ubangijinsa manya-manya



Surata: Suratun Najm

O versículo : 19

أَفَرَءَيۡتُمُ ٱللَّـٰتَ وَٱلۡعُزَّىٰ

Ku ba ni labarin (gumakan) Lata da Uzza



Surata: Suratun Najm

O versículo : 20

وَمَنَوٰةَ ٱلثَّالِثَةَ ٱلۡأُخۡرَىٰٓ

Da Manata cikon ta ukunsu



Surata: Suratun Najm

O versículo : 21

أَلَكُمُ ٱلذَّكَرُ وَلَهُ ٱلۡأُنثَىٰ

Yanzu xa namiji zai zama naku, Shi kuma Ya tashi da ‘ya mace?



Surata: Suratun Najm

O versículo : 22

تِلۡكَ إِذٗا قِسۡمَةٞ ضِيزَىٰٓ

Idan haka ne wannan rabon na zalunci ne[1]


1- Domin ya qunshi Fifita mahaluki a kan Mahalicci.


Surata: Suratun Najm

O versículo : 23

إِنۡ هِيَ إِلَّآ أَسۡمَآءٞ سَمَّيۡتُمُوهَآ أَنتُمۡ وَءَابَآؤُكُم مَّآ أَنزَلَ ٱللَّهُ بِهَا مِن سُلۡطَٰنٍۚ إِن يَتَّبِعُونَ إِلَّا ٱلظَّنَّ وَمَا تَهۡوَى ٱلۡأَنفُسُۖ وَلَقَدۡ جَآءَهُم مِّن رَّبِّهِمُ ٱلۡهُدَىٰٓ

Su ba komai ba ne face sunaye da kuka sa musu, ku da iyayenku, Allah bai saukar muku da wata hujja ba game da su. Ba abin da suke bi sai zato da son zuciya. Haqiqa kuwa shiriya ta zo musu daga Ubangijinsu



Surata: Suratun Najm

O versículo : 24

أَمۡ لِلۡإِنسَٰنِ مَا تَمَنَّىٰ

Ko kuwa sai mutum ya sami abin da yake buri ne?



Surata: Suratun Najm

O versículo : 25

فَلِلَّهِ ٱلۡأٓخِرَةُ وَٱلۡأُولَىٰ

To lahira da duniya duka na Allah ne



Surata: Suratun Najm

O versículo : 26

۞وَكَم مِّن مَّلَكٖ فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ لَا تُغۡنِي شَفَٰعَتُهُمۡ شَيۡـًٔا إِلَّا مِنۢ بَعۡدِ أَن يَأۡذَنَ ٱللَّهُ لِمَن يَشَآءُ وَيَرۡضَىٰٓ

Mala’iku nawa ne a cikin sammai cetonsu ba ya amfanar da komai sai da izinin Allah ga waxanda Ya ga dama Ya kuma yarda (da shi)?



Surata: Suratun Najm

O versículo : 27

إِنَّ ٱلَّذِينَ لَا يُؤۡمِنُونَ بِٱلۡأٓخِرَةِ لَيُسَمُّونَ ٱلۡمَلَـٰٓئِكَةَ تَسۡمِيَةَ ٱلۡأُنثَىٰ

Lalle waxanda ba sa yin imani da ranar lahira suna kiran mala’iku da sunan mata



Surata: Suratun Najm

O versículo : 28

وَمَا لَهُم بِهِۦ مِنۡ عِلۡمٍۖ إِن يَتَّبِعُونَ إِلَّا ٱلظَّنَّۖ وَإِنَّ ٱلظَّنَّ لَا يُغۡنِي مِنَ ٱلۡحَقِّ شَيۡـٔٗا

Kuma ba su da wani ilimi game da haka; ba abin da suke bi sai zato; shi kuma zato, lalle ba ya wadatar da komai game da gaskiya



Surata: Suratun Najm

O versículo : 29

فَأَعۡرِضۡ عَن مَّن تَوَلَّىٰ عَن ذِكۡرِنَا وَلَمۡ يُرِدۡ إِلَّا ٱلۡحَيَوٰةَ ٱلدُّنۡيَا

Sai ka kau da kai daga duk wanda ya ba da baya daga ambatonmu, bai kuma yi nufin komai ba sai rayuwar duniya



Surata: Suratun Najm

O versículo : 30

ذَٰلِكَ مَبۡلَغُهُم مِّنَ ٱلۡعِلۡمِۚ إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعۡلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِۦ وَهُوَ أَعۡلَمُ بِمَنِ ٱهۡتَدَىٰ

Wannan ne maqurar iliminsu. Lalle Ubangijinka Shi ne Ya fi sanin wanda ya vace daga hanyarsa kuma Shi Ya fi sanin wanda ya shiriya