Surata: Suratu Qaf 

O versículo : 1

قٓۚ وَٱلۡقُرۡءَانِ ٱلۡمَجِيدِ

QAF[1]. Na rantse da Alqur’ani mai girma


1- Duba Suratul Baqara, aya ta 1, hashiya ta 8.


Surata: Suratu Qaf 

O versículo : 2

بَلۡ عَجِبُوٓاْ أَن جَآءَهُم مُّنذِرٞ مِّنۡهُمۡ فَقَالَ ٱلۡكَٰفِرُونَ هَٰذَا شَيۡءٌ عَجِيبٌ

A’a, sun dai yi mamakin cewa, wani mai gargaxi daga cikinsu ya zo musu, sai kafirai suka ce: “Wannan abu ne mai ban mamaki!



Surata: Suratu Qaf 

O versículo : 3

أَءِذَا مِتۡنَا وَكُنَّا تُرَابٗاۖ ذَٰلِكَ رَجۡعُۢ بَعِيدٞ

“Yanzu idan muka mutu muka zama qasa, (a ce za a komo da mu)? Wannan komowa ce mai nisa!”



Surata: Suratu Qaf 

O versículo : 4

قَدۡ عَلِمۡنَا مَا تَنقُصُ ٱلۡأَرۡضُ مِنۡهُمۡۖ وَعِندَنَا كِتَٰبٌ حَفِيظُۢ

Haqiqa Mun san abin da qasa take cinyewa daga gare su; a wurinmu kuma akwai wani littafi mai kiyayewa[1]


1- Watau Lauhul Mahfuz.


Surata: Suratu Qaf 

O versículo : 5

بَلۡ كَذَّبُواْ بِٱلۡحَقِّ لَمَّا جَآءَهُمۡ فَهُمۡ فِيٓ أَمۡرٖ مَّرِيجٍ

A’a, sun dai qaryata gaskiya ne lokacin da ta zo musu, don haka suna cikin al’amari rikitacce[1]


1- Watau game da Manzon Allah (), wani lokaci su ce matsafi ne, wani lokaci kuma su ce boka ne, wani lokaci kuma su ce mawaqi ne.


Surata: Suratu Qaf 

O versículo : 6

أَفَلَمۡ يَنظُرُوٓاْ إِلَى ٱلسَّمَآءِ فَوۡقَهُمۡ كَيۡفَ بَنَيۡنَٰهَا وَزَيَّنَّـٰهَا وَمَا لَهَا مِن فُرُوجٖ

Yanzu ba sa duban sama da take sama da su (su ga) yadda Muka gina ta, Muka kuma qawata ta, ba ta kuma da wasu tsage-tsage?



Surata: Suratu Qaf 

O versículo : 7

وَٱلۡأَرۡضَ مَدَدۡنَٰهَا وَأَلۡقَيۡنَا فِيهَا رَوَٰسِيَ وَأَنۢبَتۡنَا فِيهَا مِن كُلِّ زَوۡجِۭ بَهِيجٖ

Qasa kuma Muka shimfixa ta, Muka kuma sanya turaku a cikinta, Muka kuma tsirar da kowane irin nau’in (tsiro) mai qayatarwa a cikinta



Surata: Suratu Qaf 

O versículo : 8

تَبۡصِرَةٗ وَذِكۡرَىٰ لِكُلِّ عَبۡدٖ مُّنِيبٖ

Don jan hankali da wa’azantarwa ga duk wani bawa mai mayar da al’amarinsa ga Allah



Surata: Suratu Qaf 

O versículo : 9

وَنَزَّلۡنَا مِنَ ٱلسَّمَآءِ مَآءٗ مُّبَٰرَكٗا فَأَنۢبَتۡنَا بِهِۦ جَنَّـٰتٖ وَحَبَّ ٱلۡحَصِيدِ

Muka kuma saukar da ruwa mai albarka daga sama sai Muka tsiro da lambuna da shi da kuma qwayoyin da ake girba



Surata: Suratu Qaf 

O versículo : 10

وَٱلنَّخۡلَ بَاسِقَٰتٖ لَّهَا طَلۡعٞ نَّضِيدٞ

Da kuma itatuwan dabinai dogwaye da suke da ‘ya’ya dodo-dodo



Surata: Suratu Qaf 

O versículo : 11

رِّزۡقٗا لِّلۡعِبَادِۖ وَأَحۡيَيۡنَا بِهِۦ بَلۡدَةٗ مَّيۡتٗاۚ كَذَٰلِكَ ٱلۡخُرُوجُ

Don arzuta bayi, Muka kuma raya busasshen gari da shi. Kamar haka ne fitowa (daga qabari) take



Surata: Suratu Qaf 

O versículo : 12

كَذَّبَتۡ قَبۡلَهُمۡ قَوۡمُ نُوحٖ وَأَصۡحَٰبُ ٱلرَّسِّ وَثَمُودُ

Mutanen Nuhu da ma’abota rijiyar Rassu da Samudawa (duka) sun qaryata (annabawa) a gabaninsu (watau mutanen Makka)



Surata: Suratu Qaf 

O versículo : 13

وَعَادٞ وَفِرۡعَوۡنُ وَإِخۡوَٰنُ لُوطٖ

Da kuma Adawa da Fir’auna da ‘yan’uwan Luxu (su ma sun qaryata)



Surata: Suratu Qaf 

O versículo : 14

وَأَصۡحَٰبُ ٱلۡأَيۡكَةِ وَقَوۡمُ تُبَّعٖۚ كُلّٞ كَذَّبَ ٱلرُّسُلَ فَحَقَّ وَعِيدِ

Da kuma ma’abota surquqi[1] da mutanen Tubba’u[2]. Kowannensu ya qaryata manzanni, sai azabata ta tabbata (a kansu)


1- Watau mutanen Annabi Shu’aibu ().


2- Tubba’u shi ne sarkin Yaman.1- Watau mutanen Annabi Shu’aibu ().


2- Tubba’u shi ne sarkin Yaman.


Surata: Suratu Qaf 

O versículo : 15

أَفَعَيِينَا بِٱلۡخَلۡقِ ٱلۡأَوَّلِۚ بَلۡ هُمۡ فِي لَبۡسٖ مِّنۡ خَلۡقٖ جَدِيدٖ

Shin Mun gaza ne da halittar farko? A’a, su dai suna cikin shakka ne game da sake halitta



Surata: Suratu Qaf 

O versículo : 16

وَلَقَدۡ خَلَقۡنَا ٱلۡإِنسَٰنَ وَنَعۡلَمُ مَا تُوَسۡوِسُ بِهِۦ نَفۡسُهُۥۖ وَنَحۡنُ أَقۡرَبُ إِلَيۡهِ مِنۡ حَبۡلِ ٱلۡوَرِيدِ

Haqiqa kuma Mun halicci mutum, kuma Mun san abin da ransa yake saqa masa; kuma Mu Muka fi kusa da shi fiye da jijiyar wuyansa



Surata: Suratu Qaf 

O versículo : 17

إِذۡ يَتَلَقَّى ٱلۡمُتَلَقِّيَانِ عَنِ ٱلۡيَمِينِ وَعَنِ ٱلشِّمَالِ قَعِيدٞ

Yayin da (mala’iku biyu) masu haxuwa suka haxu ta dama da ta hagu suna zaune



Surata: Suratu Qaf 

O versículo : 18

مَّا يَلۡفِظُ مِن قَوۡلٍ إِلَّا لَدَيۡهِ رَقِيبٌ عَتِيدٞ

Ba wata magana da zai furta face a tare da shi akwai (mala’ika) mai kula kuma halartacce



Surata: Suratu Qaf 

O versículo : 19

وَجَآءَتۡ سَكۡرَةُ ٱلۡمَوۡتِ بِٱلۡحَقِّۖ ذَٰلِكَ مَا كُنتَ مِنۡهُ تَحِيدُ

Kuma magagin mutuwa ya zo da gaskiya; wannan ne abin da ka kasance kana kakkauce wa



Surata: Suratu Qaf 

O versículo : 20

وَنُفِخَ فِي ٱلصُّورِۚ ذَٰلِكَ يَوۡمُ ٱلۡوَعِيدِ

Aka kuma yi busa a qaho[1]. Wannan ita ce ranar narko


1- Watau busa ta biyu.


Surata: Suratu Qaf 

O versículo : 21

وَجَآءَتۡ كُلُّ نَفۡسٖ مَّعَهَا سَآئِقٞ وَشَهِيدٞ

Kuma kowane rai ya zo a tare da shi akwai mai kora da mai shaida[1]


1- Watau mala’iku biyu tare da kowane mutum, xaya yana kora shi; xaya kuma mai ba da shaida game da shi.


Surata: Suratu Qaf 

O versículo : 22

لَّقَدۡ كُنتَ فِي غَفۡلَةٖ مِّنۡ هَٰذَا فَكَشَفۡنَا عَنكَ غِطَآءَكَ فَبَصَرُكَ ٱلۡيَوۡمَ حَدِيدٞ

Haqiqa ka kasance a cikin gafala game da wannan, sai Muka yaye maka yanarka, to ganinka a yau tangaran yake



Surata: Suratu Qaf 

O versículo : 23

وَقَالَ قَرِينُهُۥ هَٰذَا مَا لَدَيَّ عَتِيدٌ

Mala’ikan da yake tare da shi kuma ya ce: “Wannan shi ne abin da yake hallare a tare da ni.”



Surata: Suratu Qaf 

O versículo : 24

أَلۡقِيَا فِي جَهَنَّمَ كُلَّ كَفَّارٍ عَنِيدٖ

(Aka ce da mala’ikun): “Ku jefa duk wani kafiri mai taurin kai cikin Jahannama



Surata: Suratu Qaf 

O versículo : 25

مَّنَّاعٖ لِّلۡخَيۡرِ مُعۡتَدٖ مُّرِيبٍ

“Mai yawan hana alheri, mai ta’addanci, mai shakka



Surata: Suratu Qaf 

O versículo : 26

ٱلَّذِي جَعَلَ مَعَ ٱللَّهِ إِلَٰهًا ءَاخَرَ فَأَلۡقِيَاهُ فِي ٱلۡعَذَابِ ٱلشَّدِيدِ

“Wanda ya sanya wani abin bauta daban tare da Allah, saboda haka ku jefa shi cikin azaba mai tsanani.”



Surata: Suratu Qaf 

O versículo : 27

۞قَالَ قَرِينُهُۥ رَبَّنَا مَآ أَطۡغَيۡتُهُۥ وَلَٰكِن كَانَ فِي ضَلَٰلِۭ بَعِيدٖ

Shaixaninsa ya ce: “Ya Ubangijina, ni ban vatar da shi ba, sai dai kawai ya kasance cikin vata mai nisa.”



Surata: Suratu Qaf 

O versículo : 28

قَالَ لَا تَخۡتَصِمُواْ لَدَيَّ وَقَدۡ قَدَّمۡتُ إِلَيۡكُم بِٱلۡوَعِيدِ

(Allah) ya ce: “Kada ku yi husuma a gabana, haqiqa tuni Na gabatar muku da gargaxin azaba



Surata: Suratu Qaf 

O versículo : 29

مَا يُبَدَّلُ ٱلۡقَوۡلُ لَدَيَّ وَمَآ أَنَا۠ بِظَلَّـٰمٖ لِّلۡعَبِيدِ

“Ba a sauya magana a gabana, kuma Ni ba mai zaluntar bayi ba ne.”



Surata: Suratu Qaf 

O versículo : 30

يَوۡمَ نَقُولُ لِجَهَنَّمَ هَلِ ٱمۡتَلَأۡتِ وَتَقُولُ هَلۡ مِن مَّزِيدٖ

A ranar da za Mu ce da Jahannama: “Shin kin cika?” (Ita) kuma ta ce: “Shin akwai wani qari?”