Surata: Suratul Anbiya

O versículo : 1

ٱقۡتَرَبَ لِلنَّاسِ حِسَابُهُمۡ وَهُمۡ فِي غَفۡلَةٖ مُّعۡرِضُونَ

Lokacin yi wa mutane hisabi ya kusanto, alhali suna cikin gafala (suna) masu bijirewa



Surata: Suratul Anbiya

O versículo : 2

مَا يَأۡتِيهِم مِّن ذِكۡرٖ مِّن رَّبِّهِم مُّحۡدَثٍ إِلَّا ٱسۡتَمَعُوهُ وَهُمۡ يَلۡعَبُونَ

Ba wata tunatarwa sabowa (wato Alqur’ani) da za ta zo musu daga Ubangijinsu face sai sun saurare ta suna masu wasa



Surata: Suratul Anbiya

O versículo : 3

لَاهِيَةٗ قُلُوبُهُمۡۗ وَأَسَرُّواْ ٱلنَّجۡوَى ٱلَّذِينَ ظَلَمُواْ هَلۡ هَٰذَآ إِلَّا بَشَرٞ مِّثۡلُكُمۡۖ أَفَتَأۡتُونَ ٱلسِّحۡرَ وَأَنتُمۡ تُبۡصِرُونَ

Zukatansu suna cikin gafala. Waxanda suka yi zalunci kuma suka voye abin da suka tattauna (na cewa): “Wannan ba wani ne in ban da mutum kamarku; yanzu kwa riqa bin sihiri alhali kuwa ku kuna gani?”



Surata: Suratul Anbiya

O versículo : 4

قَالَ رَبِّي يَعۡلَمُ ٱلۡقَوۡلَ فِي ٱلسَّمَآءِ وَٱلۡأَرۡضِۖ وَهُوَ ٱلسَّمِيعُ ٱلۡعَلِيمُ

Ya ce: “Ubangijina Yana sane da (kowace) magana a cikin sammai da qasa; Shi kuwa Mai ji ne, Masani



Surata: Suratul Anbiya

O versículo : 5

بَلۡ قَالُوٓاْ أَضۡغَٰثُ أَحۡلَٰمِۭ بَلِ ٱفۡتَرَىٰهُ بَلۡ هُوَ شَاعِرٞ فَلۡيَأۡتِنَا بِـَٔايَةٖ كَمَآ أُرۡسِلَ ٱلۡأَوَّلُونَ

A’a, cewa dai suka yi: “Ai (shi Alqur’ani) tarkacen mafarki ne, a’a, shi (Muhammadu) qago shi ya yi, a’a, shi mawaqi dai ne, to sai ya zo mana da wata aya kamar yadda aka aiko wa mutanen farko.”



Surata: Suratul Anbiya

O versículo : 6

مَآ ءَامَنَتۡ قَبۡلَهُم مِّن قَرۡيَةٍ أَهۡلَكۡنَٰهَآۖ أَفَهُمۡ يُؤۡمِنُونَ

Ai babu wata al’umma da ta yi imani a gabaninsu wadda Muka hallaka; shin yanzu su za su yi imani?



Surata: Suratul Anbiya

O versículo : 7

وَمَآ أَرۡسَلۡنَا قَبۡلَكَ إِلَّا رِجَالٗا نُّوحِيٓ إِلَيۡهِمۡۖ فَسۡـَٔلُوٓاْ أَهۡلَ ٱلذِّكۡرِ إِن كُنتُمۡ لَا تَعۡلَمُونَ

Kuma ba Mu aiko (wasu manzanni) gabaninka ba sai mazaje da Muke yi musu wahayi; to ku tambayi ma’abota sani idan ya zamana ku ba ku sani ba



Surata: Suratul Anbiya

O versículo : 8

وَمَا جَعَلۡنَٰهُمۡ جَسَدٗا لَّا يَأۡكُلُونَ ٱلطَّعَامَ وَمَا كَانُواْ خَٰلِدِينَ

Kuma ba Mu sanya su jiki ne da ba sa cin abinci ba, kuma ba su zamanto masu dawwama ba



Surata: Suratul Anbiya

O versículo : 9

ثُمَّ صَدَقۡنَٰهُمُ ٱلۡوَعۡدَ فَأَنجَيۡنَٰهُمۡ وَمَن نَّشَآءُ وَأَهۡلَكۡنَا ٱلۡمُسۡرِفِينَ

Sannan Muka cika musu alqawari, sai Muka tserar da su da waxanda Muke ga damar (tserarwa) kuma Muka hallakar da mavarnata



Surata: Suratul Anbiya

O versículo : 10

لَقَدۡ أَنزَلۡنَآ إِلَيۡكُمۡ كِتَٰبٗا فِيهِ ذِكۡرُكُمۡۚ أَفَلَا تَعۡقِلُونَ

Haqiqa Mun saukar muku da littafi (wanda) a cikinsa akwai xaukakarku[1]; me ya sa ba kwa hankalta?


1- Watau za su samu xaukaka duniya da lahira idan sun yi imani da shi, suka yi aiki da karantarwarsa.


Surata: Suratul Anbiya

O versículo : 11

وَكَمۡ قَصَمۡنَا مِن قَرۡيَةٖ كَانَتۡ ظَالِمَةٗ وَأَنشَأۡنَا بَعۡدَهَا قَوۡمًا ءَاخَرِينَ

Al’ummu nawa ne kuma Muka hallakar (waxanda) suka kasance azzulumai, Muka kuma halicci wasu mutanen daban bayansu?



Surata: Suratul Anbiya

O versículo : 12

فَلَمَّآ أَحَسُّواْ بَأۡسَنَآ إِذَا هُم مِّنۡهَا يَرۡكُضُونَ

Lokacin da suka fara jin azabarmu sai ga su suna guje mata



Surata: Suratul Anbiya

O versículo : 13

لَا تَرۡكُضُواْ وَٱرۡجِعُوٓاْ إِلَىٰ مَآ أُتۡرِفۡتُمۡ فِيهِ وَمَسَٰكِنِكُمۡ لَعَلَّكُمۡ تُسۡـَٔلُونَ

(Aka ce da su): “Kada ku gudu, ku dawo zuwa ga abin da aka ni’imta ku da shi, da kuma gidajenku don a yi muku tambayoyi[1].”


1- Watau a kan rayuwarsu ta tamore da bushasha. Ana faxa musu haka a cikin izgili da tsokana.


Surata: Suratul Anbiya

O versículo : 14

قَالُواْ يَٰوَيۡلَنَآ إِنَّا كُنَّا ظَٰلِمِينَ

Suka ce: “Kaiconmu, lallai mu kam mun kasance azzalumai!”



Surata: Suratul Anbiya

O versículo : 15

فَمَا زَالَت تِّلۡكَ دَعۡوَىٰهُمۡ حَتَّىٰ جَعَلۡنَٰهُمۡ حَصِيدًا خَٰمِدِينَ

Sannan waccan (maganar tasu) ba su daina faxar ta ba har Muka mai da su girbabbu, matattu



Surata: Suratul Anbiya

O versículo : 16

وَمَا خَلَقۡنَا ٱلسَّمَآءَ وَٱلۡأَرۡضَ وَمَا بَيۡنَهُمَا لَٰعِبِينَ

Kuma ba Mu halicci sama da qasa da kuma abin da yake tsakaninsu don wasa ba



Surata: Suratul Anbiya

O versículo : 17

لَوۡ أَرَدۡنَآ أَن نَّتَّخِذَ لَهۡوٗا لَّٱتَّخَذۡنَٰهُ مِن لَّدُنَّآ إِن كُنَّا فَٰعِلِينَ

In da Mun yi nufin Mu riqi (abin) da zai shagaltar (mata ko xa), to da sai Mu riqe shi daga waxanda suke a wurinmu, idan har za Mu yi hakan



Surata: Suratul Anbiya

O versículo : 18

بَلۡ نَقۡذِفُ بِٱلۡحَقِّ عَلَى ٱلۡبَٰطِلِ فَيَدۡمَغُهُۥ فَإِذَا هُوَ زَاهِقٞۚ وَلَكُمُ ٱلۡوَيۡلُ مِمَّا تَصِفُونَ

A’a, ba haka ba ne, Muna jefa gaskiya a kan qarya, sai ta yi rugu-rugu da ita, sai (ka gan ta) ta vace vat. Kuma tsananin azaba ya tabbata a gare ku saboda abin da kuke siffanta (Shi da shi)[1]


1- Watau na cewa yana da mata ko xa ko abokin tarayya.


Surata: Suratul Anbiya

O versículo : 19

وَلَهُۥ مَن فِي ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۚ وَمَنۡ عِندَهُۥ لَا يَسۡتَكۡبِرُونَ عَنۡ عِبَادَتِهِۦ وَلَا يَسۡتَحۡسِرُونَ

Duk kuwa waxanda suke sammai da qasa nasa ne, kuma waxanda suke wurinsa ba sa girman kai game da bauta masa, kuma ba sa gajiya



Surata: Suratul Anbiya

O versículo : 20

يُسَبِّحُونَ ٱلَّيۡلَ وَٱلنَّهَارَ لَا يَفۡتُرُونَ

Suna tasbihi dare da rana ba sa qosawa



Surata: Suratul Anbiya

O versículo : 21

أَمِ ٱتَّخَذُوٓاْ ءَالِهَةٗ مِّنَ ٱلۡأَرۡضِ هُمۡ يُنشِرُونَ

Shin ko sun riqi wasu ababen bauta a nan qasa ne waxanda suke raya matattu?



Surata: Suratul Anbiya

O versículo : 22

لَوۡ كَانَ فِيهِمَآ ءَالِهَةٌ إِلَّا ٱللَّهُ لَفَسَدَتَاۚ فَسُبۡحَٰنَ ٱللَّهِ رَبِّ ٱلۡعَرۡشِ عَمَّا يَصِفُونَ

Da ya zamana akwai wasu ababen bauta ba Allah ba a cikinsu (wato sammai da qasa), to da sun lalace. Sai dai tsarki ya tabbata ga Allah Ubangijin Al’arshi game da abin da suke siffata (Shi da shi)



Surata: Suratul Anbiya

O versículo : 23

لَا يُسۡـَٔلُ عَمَّا يَفۡعَلُ وَهُمۡ يُسۡـَٔلُونَ

Ba a tambayar Sa game da abin da yake aikatawa, su dai ne za a tambaye su



Surata: Suratul Anbiya

O versículo : 24

أَمِ ٱتَّخَذُواْ مِن دُونِهِۦٓ ءَالِهَةٗۖ قُلۡ هَاتُواْ بُرۡهَٰنَكُمۡۖ هَٰذَا ذِكۡرُ مَن مَّعِيَ وَذِكۡرُ مَن قَبۡلِيۚ بَلۡ أَكۡثَرُهُمۡ لَا يَعۡلَمُونَ ٱلۡحَقَّۖ فَهُم مُّعۡرِضُونَ

Ko kuma sun riqi wasu ababen bauta ne ba Shi ba? Ka ce (da su): “To ku kawo dalilinku (a kan haka). Ga wa’azin waxanda suke tare dani (watau Alqur’ani), ga kuma wa’azin waxanda suka gabace ni (watau littattafan annabawa sai ku duba).” A’a, yawancinsu dai ba sa sanin gaskiya sannan kuma masu bijire (mata) ne



Surata: Suratul Anbiya

O versículo : 25

وَمَآ أَرۡسَلۡنَا مِن قَبۡلِكَ مِن رَّسُولٍ إِلَّا نُوحِيٓ إِلَيۡهِ أَنَّهُۥ لَآ إِلَٰهَ إِلَّآ أَنَا۠ فَٱعۡبُدُونِ

Kuma ba wani manzo da Muka aiko gabaninka face sai Mun yi masa wahayi cewa, babu wani abin bauta da gaskiya sai Ni; to sai ku bauta min[1]


1- Duk manzannin da Allah ya aiko sun zo ne da saqon a bauta wa Allah shi kaxai ba tare da shirka ba.


Surata: Suratul Anbiya

O versículo : 26

وَقَالُواْ ٱتَّخَذَ ٱلرَّحۡمَٰنُ وَلَدٗاۗ سُبۡحَٰنَهُۥۚ بَلۡ عِبَادٞ مُّكۡرَمُونَ

Suka kuma ce wai Allah Ya riqi xa (daga cikin mala’iku)! Tsarki ya tabbata a gare Shi. A’a, su bayi dai ne ababen girmamawa



Surata: Suratul Anbiya

O versículo : 27

لَا يَسۡبِقُونَهُۥ بِٱلۡقَوۡلِ وَهُم بِأَمۡرِهِۦ يَعۡمَلُونَ

Ba sa rigayar Sa da magana, su kuma da umarninsa suke aiki



Surata: Suratul Anbiya

O versículo : 28

يَعۡلَمُ مَا بَيۡنَ أَيۡدِيهِمۡ وَمَا خَلۡفَهُمۡ وَلَا يَشۡفَعُونَ إِلَّا لِمَنِ ٱرۡتَضَىٰ وَهُم مِّنۡ خَشۡيَتِهِۦ مُشۡفِقُونَ

Yana sane da ayyukansu da suka gabatar da na nan gaba, ba kuma za su yi ceto ba sai ga wanda Ya yarda (daga bayinsa), suna kuwa masu kaffa-kaffa don tsoron Sa



Surata: Suratul Anbiya

O versículo : 29

۞وَمَن يَقُلۡ مِنۡهُمۡ إِنِّيٓ إِلَٰهٞ مِّن دُونِهِۦ فَذَٰلِكَ نَجۡزِيهِ جَهَنَّمَۚ كَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلظَّـٰلِمِينَ

Daga cikinsu kuwa duk wanda ya ce: “Ni abin bauta ne ba shi (Allah) ba,” to wannan za Mu saka masa da (wutar) Jahannama. Kamar haka kuwa Muke saka wa azzalumai



Surata: Suratul Anbiya

O versículo : 30

أَوَلَمۡ يَرَ ٱلَّذِينَ كَفَرُوٓاْ أَنَّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ كَانَتَا رَتۡقٗا فَفَتَقۡنَٰهُمَاۖ وَجَعَلۡنَا مِنَ ٱلۡمَآءِ كُلَّ شَيۡءٍ حَيٍّۚ أَفَلَا يُؤۡمِنُونَ

Yanzu waxanda suka kafirta ba sa ganin cewa a da can sammai da qasa a haxe suke, sannan Muka raba su[1]; Muka kuma halicci duk wani abu mai rai daga ruwa? To me ya sa ba za su yi imani ba?


1- Watau Allah () ya fara halittar sammai da qasa a manne da juna daga bisani ya raba tsakaninsu.