فَأۡتِيَاهُ فَقُولَآ إِنَّا رَسُولَا رَبِّكَ فَأَرۡسِلۡ مَعَنَا بَنِيٓ إِسۡرَـٰٓءِيلَ وَلَا تُعَذِّبۡهُمۡۖ قَدۡ جِئۡنَٰكَ بِـَٔايَةٖ مِّن رَّبِّكَۖ وَٱلسَّلَٰمُ عَلَىٰ مَنِ ٱتَّبَعَ ٱلۡهُدَىٰٓ
“Sai ku tafi wajensa sannan ku ce (da shi): “Lalle mu manzannin Ubangijinka ne, sai ka sakar mana Banu-Isra’ila, kada kuma ka azabtar da su; haqiqa mun zo maka da aya daga Ubangijinka; aminci kuwa ya tabbata ga wanda ya bi shiriya
إِنَّا قَدۡ أُوحِيَ إِلَيۡنَآ أَنَّ ٱلۡعَذَابَ عَلَىٰ مَن كَذَّبَ وَتَوَلَّىٰ
“Lalle mu an yi mana wahayi cewa, ita azaba lalle tana nan ga wanda ya qaryata ya kuma ba da baya.”
قَالَ فَمَن رَّبُّكُمَا يَٰمُوسَىٰ
(Fir’auna) ya ce: “Wane ne Ubangijin naku ya Musa?”
قَالَ رَبُّنَا ٱلَّذِيٓ أَعۡطَىٰ كُلَّ شَيۡءٍ خَلۡقَهُۥ ثُمَّ هَدَىٰ
(Musa) ya ce: “Ubangijinmu (Shi ne) Wanda Ya bai wa kowane abu surar halittarsa sannan Ya shiryar (da shi yadda zai yi tasarrufi).”
قَالَ فَمَا بَالُ ٱلۡقُرُونِ ٱلۡأُولَىٰ
(Fir’auna) ya ce: “To mene ne halin da al’ummun farko suke ciki?”
قَالَ عِلۡمُهَا عِندَ رَبِّي فِي كِتَٰبٖۖ لَّا يَضِلُّ رَبِّي وَلَا يَنسَى
(Musa) ya ce: “Saninsu yana wurin Ubangijina a cikin Lauhul-Mahafuzu; Ubangijina kuma ba Ya kuskure (cikin iliminsa) kuma ba Ya mantuwa
ٱلَّذِي جَعَلَ لَكُمُ ٱلۡأَرۡضَ مَهۡدٗا وَسَلَكَ لَكُمۡ فِيهَا سُبُلٗا وَأَنزَلَ مِنَ ٱلسَّمَآءِ مَآءٗ فَأَخۡرَجۡنَا بِهِۦٓ أَزۡوَٰجٗا مِّن نَّبَاتٖ شَتَّىٰ
“(Shi ne) Wanda Ya sanya muku qasa a shimfixe, Ya kuma sanya muku hanyoyi na tafiya cikinta, kuma Ya saukar da ruwa daga sama”, sannan Muka fitar da dangogin shuke-shuke iri-iri da shi (ruwa)
كُلُواْ وَٱرۡعَوۡاْ أَنۡعَٰمَكُمۡۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَٰتٖ لِّأُوْلِي ٱلنُّهَىٰ
Ku ci (daga tsirran) kuma ku yi kiwon dabbobinku. Lalle a game da wannan akwai ayoyi ga ma’abota hankula
۞مِنۡهَا خَلَقۡنَٰكُمۡ وَفِيهَا نُعِيدُكُمۡ وَمِنۡهَا نُخۡرِجُكُمۡ تَارَةً أُخۡرَىٰ
Daga ita (qasar) Muka halicce ku, kuma a cikinta za Mu mayar da ku, daga ita kuma za Mu fito da ku a wani karon
وَلَقَدۡ أَرَيۡنَٰهُ ءَايَٰتِنَا كُلَّهَا فَكَذَّبَ وَأَبَىٰ
Kuma haqiqa Mun nuna masa (Fir’auna) ayoyinmu dukkansu, sai ya qaryata kuma ya qi (ba da gaskiya)
قَالَ أَجِئۡتَنَا لِتُخۡرِجَنَا مِنۡ أَرۡضِنَا بِسِحۡرِكَ يَٰمُوسَىٰ
(Fir’auna) ya ce: “Yanzu ka zo mana ne don ka fitar da mu daga qasarmu da sihirinka, ya Musa?
فَلَنَأۡتِيَنَّكَ بِسِحۡرٖ مِّثۡلِهِۦ فَٱجۡعَلۡ بَيۡنَنَا وَبَيۡنَكَ مَوۡعِدٗا لَّا نُخۡلِفُهُۥ نَحۡنُ وَلَآ أَنتَ مَكَانٗا سُوٗى
“To lalle kuwa za mu zo maka da wani sihirin irinsa; sai ka sanya lokaci na musamman tsakaninmu da kai wanda mu ba za mu sava masa ba, kai ma haka, (ya zama) wuri ne tsaka-tsaki”
قَالَ مَوۡعِدُكُمۡ يَوۡمُ ٱلزِّينَةِ وَأَن يُحۡشَرَ ٱلنَّاسُ ضُحٗى
(Musa) ya ce: “Lokacin (da na sanya) muku shi ne ranar idi, kuma a tattara mutane da hantsi.”
فَتَوَلَّىٰ فِرۡعَوۡنُ فَجَمَعَ كَيۡدَهُۥ ثُمَّ أَتَىٰ
Sai Fir’auna ya juya, sai ya haxa makircinsa, sannan ya zo (wurin da aka shirya)
قَالَ لَهُم مُّوسَىٰ وَيۡلَكُمۡ لَا تَفۡتَرُواْ عَلَى ٱللَّهِ كَذِبٗا فَيُسۡحِتَكُم بِعَذَابٖۖ وَقَدۡ خَابَ مَنِ ٱفۡتَرَىٰ
Musa ya ce da su: “Kaiconku! Kada fa ku qirqira wa Allah qarya, sai Ya hallaka ku da azaba; haqiqa kuwa wanda ya qirqira (masa qarya) to ya tave.”
فَتَنَٰزَعُوٓاْ أَمۡرَهُم بَيۡنَهُمۡ وَأَسَرُّواْ ٱلنَّجۡوَىٰ
Sai suka tattauna al’amarinsu a tsakaninsu, suka kuma gana a asirce
قَالُوٓاْ إِنۡ هَٰذَٰنِ لَسَٰحِرَٰنِ يُرِيدَانِ أَن يُخۡرِجَاكُم مِّنۡ أَرۡضِكُم بِسِحۡرِهِمَا وَيَذۡهَبَا بِطَرِيقَتِكُمُ ٱلۡمُثۡلَىٰ
Suka ce: “Lalle waxannan biyun (Musa da Haruna) tabbas matsafa ne, suna so ne su fitar da ku daga qasarku da tsafinsu, su kuma tafiyar da kyakkyawar hanyarku (ta rayuwa)
فَأَجۡمِعُواْ كَيۡدَكُمۡ ثُمَّ ٱئۡتُواْ صَفّٗاۚ وَقَدۡ أَفۡلَحَ ٱلۡيَوۡمَ مَنِ ٱسۡتَعۡلَىٰ
“Sai ku yiwo shiri haxaxxe sannan ku zo sahu-sahu. Haqiqa yau kam wanda ya yi nasara ya rabauta!”
قَالُواْ يَٰمُوسَىٰٓ إِمَّآ أَن تُلۡقِيَ وَإِمَّآ أَن نَّكُونَ أَوَّلَ مَنۡ أَلۡقَىٰ
Suka ce: “Ya Musa, ko dai ka jefa (naka) ko kuma mu mu fara jefa (namu).”
قَالَ بَلۡ أَلۡقُواْۖ فَإِذَا حِبَالُهُمۡ وَعِصِيُّهُمۡ يُخَيَّلُ إِلَيۡهِ مِن سِحۡرِهِمۡ أَنَّهَا تَسۡعَىٰ
Ya ce: “A’a, ku (fara) jefawa.” To saboda sihirinsu sai ga igiyoyinsu da sandunansu ana suranta masa cewa su (macizai ne) suna sauri
فَأَوۡجَسَ فِي نَفۡسِهِۦ خِيفَةٗ مُّوسَىٰ
Sai Musa ya voye (wani abu) na tsoro a ransa
قُلۡنَا لَا تَخَفۡ إِنَّكَ أَنتَ ٱلۡأَعۡلَىٰ
Muka ce: “Kada ka ji tsoro, lalle kai kake da rinjaye
وَأَلۡقِ مَا فِي يَمِينِكَ تَلۡقَفۡ مَا صَنَعُوٓاْۖ إِنَّمَا صَنَعُواْ كَيۡدُ سَٰحِرٖۖ وَلَا يُفۡلِحُ ٱلسَّاحِرُ حَيۡثُ أَتَىٰ
“Kuma ka jefar da abin da yake hannunka na dama, za ta haxiye abin da suka aikata; lalle abin da suka aikata makircin matsafi ne; matsafi kuwa ba ya rabauta duk ta inda ya zo.”
فَأُلۡقِيَ ٱلسَّحَرَةُ سُجَّدٗا قَالُوٓاْ ءَامَنَّا بِرَبِّ هَٰرُونَ وَمُوسَىٰ
Sai matsafan suka faxi suna sujjada[1] suka ce: “Mun yi imani da Ubangijin Haruna da Musa!”
1- Watau bayan sun fahimci cewa abin da Musa () ya zo da shi ba tsafi ba ne, wani abu ne daga Allah.
قَالَ ءَامَنتُمۡ لَهُۥ قَبۡلَ أَنۡ ءَاذَنَ لَكُمۡۖ إِنَّهُۥ لَكَبِيرُكُمُ ٱلَّذِي عَلَّمَكُمُ ٱلسِّحۡرَۖ فَلَأُقَطِّعَنَّ أَيۡدِيَكُمۡ وَأَرۡجُلَكُم مِّنۡ خِلَٰفٖ وَلَأُصَلِّبَنَّكُمۡ فِي جُذُوعِ ٱلنَّخۡلِ وَلَتَعۡلَمُنَّ أَيُّنَآ أَشَدُّ عَذَابٗا وَأَبۡقَىٰ
(Fir’auna) ya ce: “Yanzu kwa yi imani da shi tun kafin in yi muku izini? Lalle shi ne babbanku wanda ya koya muku tsafi; to lalle zan yayyanke hannayenku da qafafuwanku a tarnaqe (wato hannun dama da qafar hagu), kuma tabbas zan gicciye ku a kan kututturen dabino, lalle kuma tabbas za ku san wane ne tsakanin ni da shi wanda ya fi tsananin azaba kuma ta fi xorewa
قَالُواْ لَن نُّؤۡثِرَكَ عَلَىٰ مَا جَآءَنَا مِنَ ٱلۡبَيِّنَٰتِ وَٱلَّذِي فَطَرَنَاۖ فَٱقۡضِ مَآ أَنتَ قَاضٍۖ إِنَّمَا تَقۡضِي هَٰذِهِ ٱلۡحَيَوٰةَ ٱلدُّنۡيَآ
Suka ce: “Ba za mu fifita ka ba a kan abin da ya zo mana na (ayoyi) mabayyana, da kuma a kan wanda Ya halicce mu. Sai ka hukunta duk abin da za ka hukunta; za ka yi hukunci ne kawai a wannnan rayuwar ta duniya
إِنَّآ ءَامَنَّا بِرَبِّنَا لِيَغۡفِرَ لَنَا خَطَٰيَٰنَا وَمَآ أَكۡرَهۡتَنَا عَلَيۡهِ مِنَ ٱلسِّحۡرِۗ وَٱللَّهُ خَيۡرٞ وَأَبۡقَىٰٓ
“Lalle mu kam mun yi imani da Ubangijinmu don Ya gafarta mana laifukanmu da kuma abin da ka tilasta mu a kansa na tsafi. Allah kuwa Shi ne Mafi alherin (sakamako), kuma Shi ne Mafi dawwamar (azaba).”
إِنَّهُۥ مَن يَأۡتِ رَبَّهُۥ مُجۡرِمٗا فَإِنَّ لَهُۥ جَهَنَّمَ لَا يَمُوتُ فِيهَا وَلَا يَحۡيَىٰ
Lalle duk wanda ya zo wa Ubangijinsa yana mai babban laifi[1] to lalle yana da (sakamakon) Jahannama, ba zai mutu a cikinta ba, ba kuma zai rayu ba (rayuwa mai daxi)
1- Watau kafirce wa Allah da haxa wani da shi a wajen bauta.
وَمَن يَأۡتِهِۦ مُؤۡمِنٗا قَدۡ عَمِلَ ٱلصَّـٰلِحَٰتِ فَأُوْلَـٰٓئِكَ لَهُمُ ٱلدَّرَجَٰتُ ٱلۡعُلَىٰ
Wanda kuwa ya zo masa yana mumini ya zamana ya yi aiki na gari, to waxannan suna da (sakamakon samun) darajoji maxaukaka
جَنَّـٰتُ عَدۡنٖ تَجۡرِي مِن تَحۡتِهَا ٱلۡأَنۡهَٰرُ خَٰلِدِينَ فِيهَاۚ وَذَٰلِكَ جَزَآءُ مَن تَزَكَّىٰ
(Watau) gidajen Aljanna na dawwama waxanda qoramu suke gudana ta qarqashinsu, masu dawwama ne a cikinsu. Wannan kuwa shi ne sakamakon wanda ya tsarkaka (daga savo)