Capítulo: Suratul Kahf 

Verso : 70

قَالَ فَإِنِ ٱتَّبَعۡتَنِي فَلَا تَسۡـَٔلۡنِي عَن شَيۡءٍ حَتَّىٰٓ أُحۡدِثَ لَكَ مِنۡهُ ذِكۡرٗا

Ya ce, “To idan ka bi ni kada ka tambaye ni game da kowane abu har sai na ba ka labari game da shi.”



Capítulo: Suratul Kahf 

Verso : 71

فَٱنطَلَقَا حَتَّىٰٓ إِذَا رَكِبَا فِي ٱلسَّفِينَةِ خَرَقَهَاۖ قَالَ أَخَرَقۡتَهَا لِتُغۡرِقَ أَهۡلَهَا لَقَدۡ جِئۡتَ شَيۡـًٔا إِمۡرٗا

Sai suka tafi, har lokacin da suka shiga cikin jirgin ruwa, to sai ya huda shi; sai (Musa) ya ce: “Yanzu ka huda shi ne don ka nutsar da waxanda suke cikinsa? Haqiqa ka zo da babban abu.”



Capítulo: Suratul Kahf 

Verso : 72

قَالَ أَلَمۡ أَقُلۡ إِنَّكَ لَن تَسۡتَطِيعَ مَعِيَ صَبۡرٗا

Ya ce: “Ban faxa maka ba cewa kai ba za ka iya haquri da ni ba?”



Capítulo: Suratul Kahf 

Verso : 73

قَالَ لَا تُؤَاخِذۡنِي بِمَا نَسِيتُ وَلَا تُرۡهِقۡنِي مِنۡ أَمۡرِي عُسۡرٗا

(Musa) ya ce: “Kada ka kama ni da abin da na manta, kada kuma ka xora mini abu mai wahala game da al’amarina.”



Capítulo: Suratul Kahf 

Verso : 74

فَٱنطَلَقَا حَتَّىٰٓ إِذَا لَقِيَا غُلَٰمٗا فَقَتَلَهُۥ قَالَ أَقَتَلۡتَ نَفۡسٗا زَكِيَّةَۢ بِغَيۡرِ نَفۡسٖ لَّقَدۡ جِئۡتَ شَيۡـٔٗا نُّكۡرٗا

Sai suka ci gaba da tafiya har dai suka gamu da wani yaro, to sai ya kashe shi, (Musa) ya ce: “Yanzu ka kashe rai tsarkakakke ba tare da (ya kashe) wani rai ba? Haqiqa ka zo da wani abu mummuna!”