قَالَ ٱلۡمَلَأُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ مِن قَوۡمِهِۦٓ إِنَّا لَنَرَىٰكَ فِي سَفَاهَةٖ وَإِنَّا لَنَظُنُّكَ مِنَ ٱلۡكَٰذِبِينَ
Sai manyan gari waxanda suka kafirce cikin mutanensa suka ce: “Lalle mu tabbas muna ganin ka kana cikin wauta, kuma lalle mu tabbas muna zaton kai kana cikin maqaryata
قَالَ يَٰقَوۡمِ لَيۡسَ بِي سَفَاهَةٞ وَلَٰكِنِّي رَسُولٞ مِّن رَّبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
Sai ya ce: “Ya ku mutanena, babu wata wauta a tare da ni, sai dai ni kawai Manzo ne daga Ubangijin talikai
أُبَلِّغُكُمۡ رِسَٰلَٰتِ رَبِّي وَأَنَا۠ لَكُمۡ نَاصِحٌ أَمِينٌ
“Ina isar muku da saqonnin Ubangijina, kuma ni mai nasiha ne a gare ku, amintacce
أَوَعَجِبۡتُمۡ أَن جَآءَكُمۡ ذِكۡرٞ مِّن رَّبِّكُمۡ عَلَىٰ رَجُلٖ مِّنكُمۡ لِيُنذِرَكُمۡۚ وَٱذۡكُرُوٓاْ إِذۡ جَعَلَكُمۡ خُلَفَآءَ مِنۢ بَعۡدِ قَوۡمِ نُوحٖ وَزَادَكُمۡ فِي ٱلۡخَلۡقِ بَصۜۡطَةٗۖ فَٱذۡكُرُوٓاْ ءَالَآءَ ٱللَّهِ لَعَلَّكُمۡ تُفۡلِحُونَ
“Shin mamaki kuke yi wa’azi ya zo muku daga Ubangijinku a kan (harshen) wani mutum daga cikinku don ya gargaxe ku? Kuma ku tuna yayin da Ya sa kuka zama masu maye gurbi bayan wucewar mutanen Nuhu, kuma Ya qara muku girman halitta; don haka ku tuna ni’imomin Allah, don ku rabauta.”
قَالُوٓاْ أَجِئۡتَنَا لِنَعۡبُدَ ٱللَّهَ وَحۡدَهُۥ وَنَذَرَ مَا كَانَ يَعۡبُدُ ءَابَآؤُنَا فَأۡتِنَا بِمَا تَعِدُنَآ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّـٰدِقِينَ
Sai suka ce: “Yanzu ka zo mana ne don mu bauta wa Allah Shi kaxai, kuma mu qyale abin da iyayenmu suka kasance suna bautata wa? To ka kawo mana abin da kake yi mana alqawarinsa[1] idan ka kasance cikin masu gaskiya.”
1- Watau azabar Allah ().
قَالَ قَدۡ وَقَعَ عَلَيۡكُم مِّن رَّبِّكُمۡ رِجۡسٞ وَغَضَبٌۖ أَتُجَٰدِلُونَنِي فِيٓ أَسۡمَآءٖ سَمَّيۡتُمُوهَآ أَنتُمۡ وَءَابَآؤُكُم مَّا نَزَّلَ ٱللَّهُ بِهَا مِن سُلۡطَٰنٖۚ فَٱنتَظِرُوٓاْ إِنِّي مَعَكُم مِّنَ ٱلۡمُنتَظِرِينَ
Sai ya ce: “Haqiqa azaba da fushi daga Ubangijinku sun faxa a kanku. Yanzu kwa riqa jayayya da ni a kan waxansu sunaye da ku ne kuka qago su da iyayenku[1], alhalin Allah bai saukar da wata hujja a kansu ba? To ku jira (ku gani), lalle ni ma ina nan cikin masu jira tare da ku.”
1- Watau gumakan da suke bauta wa ba Allah ba.
فَأَنجَيۡنَٰهُ وَٱلَّذِينَ مَعَهُۥ بِرَحۡمَةٖ مِّنَّا وَقَطَعۡنَا دَابِرَ ٱلَّذِينَ كَذَّبُواْ بِـَٔايَٰتِنَاۖ وَمَا كَانُواْ مُؤۡمِنِينَ
Sai Muka tserar da shi, da waxanda suke tare da shi da rahamarmu, Muka kuma tumvuke tushen waxanda suka qaryata ayoyinmu; kuma ba su kasance muminai ba
وَإِلَىٰ ثَمُودَ أَخَاهُمۡ صَٰلِحٗاۚ قَالَ يَٰقَوۡمِ ٱعۡبُدُواْ ٱللَّهَ مَا لَكُم مِّنۡ إِلَٰهٍ غَيۡرُهُۥۖ قَدۡ جَآءَتۡكُم بَيِّنَةٞ مِّن رَّبِّكُمۡۖ هَٰذِهِۦ نَاقَةُ ٱللَّهِ لَكُمۡ ءَايَةٗۖ فَذَرُوهَا تَأۡكُلۡ فِيٓ أَرۡضِ ٱللَّهِۖ وَلَا تَمَسُّوهَا بِسُوٓءٖ فَيَأۡخُذَكُمۡ عَذَابٌ أَلِيمٞ
Zuwa ga Samudawa kuwa Mun aika xan’uwansu Salihu. Ya ce: “Ya ku mutanena, ku bauta wa Allah, ba ku da wani abin bauta wa da gaskiya sai Shi; haqiqa hujja ta zo muku daga Ubangijinku. Wannan kuma taguwar Allah aya ce a gare ku; don haka ku qyale ta ta ci a bayan qasar Allah; kuma kar ku tava ta da wani mugun abu, sai wata azaba mai raxaxi ta shafe ku
وَٱذۡكُرُوٓاْ إِذۡ جَعَلَكُمۡ خُلَفَآءَ مِنۢ بَعۡدِ عَادٖ وَبَوَّأَكُمۡ فِي ٱلۡأَرۡضِ تَتَّخِذُونَ مِن سُهُولِهَا قُصُورٗا وَتَنۡحِتُونَ ٱلۡجِبَالَ بُيُوتٗاۖ فَٱذۡكُرُوٓاْ ءَالَآءَ ٱللَّهِ وَلَا تَعۡثَوۡاْ فِي ٱلۡأَرۡضِ مُفۡسِدِينَ
“Kuma ku tuna lokacin da Ya sanya ku kuka zama masu maye gurbi bayan Adawa, kuma Ya zaunar da ku a bayan qasa, kuna yin benaye a wurarenta masu taushi, kuma kuna sassaqa gidaje a duwatsu; don haka ku tuna ni’imomin Allah, kada kuma ku yi varna a bayan qasa.”
قَالَ ٱلۡمَلَأُ ٱلَّذِينَ ٱسۡتَكۡبَرُواْ مِن قَوۡمِهِۦ لِلَّذِينَ ٱسۡتُضۡعِفُواْ لِمَنۡ ءَامَنَ مِنۡهُمۡ أَتَعۡلَمُونَ أَنَّ صَٰلِحٗا مُّرۡسَلٞ مِّن رَّبِّهِۦۚ قَالُوٓاْ إِنَّا بِمَآ أُرۡسِلَ بِهِۦ مُؤۡمِنُونَ
Manyan gari waxanda suka yi girman kai daga mutanensa, suka ce wa waxanda suke raunana waxanda suka yi imani daga cikinsu: “Yanzu kun san cewa Salihu Manzo ne daga wajen Ubangijinsa?” Sai suka ce; “Lalle mu dai mun yi imani da abin da aka aiko shi da shi.”
قَالَ ٱلَّذِينَ ٱسۡتَكۡبَرُوٓاْ إِنَّا بِٱلَّذِيٓ ءَامَنتُم بِهِۦ كَٰفِرُونَ
Waxanda suka yi girman kai suka ce: “Lalle mu kuma mun kafirce wa abin da kuka yi imani da shi.”
فَعَقَرُواْ ٱلنَّاقَةَ وَعَتَوۡاْ عَنۡ أَمۡرِ رَبِّهِمۡ وَقَالُواْ يَٰصَٰلِحُ ٱئۡتِنَا بِمَا تَعِدُنَآ إِن كُنتَ مِنَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ
Sai suka soke taguwar, suka kuma yi tsaurin kai game da umarnin Ubangijinsu, kuma suka ce: “Ya Salihu, ka zo mana da abin da kake mana alqawarin zai same mu (na azaba) in ka kasance cikin manzanni.”
فَأَخَذَتۡهُمُ ٱلرَّجۡفَةُ فَأَصۡبَحُواْ فِي دَارِهِمۡ جَٰثِمِينَ
Sai wata girgizar qasa mai tsanani ta auka musu, sai suka wayi gari a gurfane kan gwiwoyinsu, (matattu) a cikin gidajensu
فَتَوَلَّىٰ عَنۡهُمۡ وَقَالَ يَٰقَوۡمِ لَقَدۡ أَبۡلَغۡتُكُمۡ رِسَالَةَ رَبِّي وَنَصَحۡتُ لَكُمۡ وَلَٰكِن لَّا تُحِبُّونَ ٱلنَّـٰصِحِينَ
Sai ya juya ya rabu da su, kuma ya ce: “Ya ku mutanena, lalle haqiqa na isar muku da saqon Ubangijina, kuma na yi muku nasiha, sai dai ku ba kwa son masu nasiha.”
وَلُوطًا إِذۡ قَالَ لِقَوۡمِهِۦٓ أَتَأۡتُونَ ٱلۡفَٰحِشَةَ مَا سَبَقَكُم بِهَا مِنۡ أَحَدٖ مِّنَ ٱلۡعَٰلَمِينَ
Kuma ka tuna Luxu lokacin da ya ce wa mutanensa: “Yanzu kwa riqa aikata mummunan aikin da babu wani mahaluqi a duniya da ya tava aikata irinsa gabaninku?
إِنَّكُمۡ لَتَأۡتُونَ ٱلرِّجَالَ شَهۡوَةٗ مِّن دُونِ ٱلنِّسَآءِۚ بَلۡ أَنتُمۡ قَوۡمٞ مُّسۡرِفُونَ
“Lalle ku kuna zaike wa maza don sha’awa maimakon mata. A’a, ku mutane ne mavarnata.”
وَمَا كَانَ جَوَابَ قَوۡمِهِۦٓ إِلَّآ أَن قَالُوٓاْ أَخۡرِجُوهُم مِّن قَرۡيَتِكُمۡۖ إِنَّهُمۡ أُنَاسٞ يَتَطَهَّرُونَ
Ba kuwa amsar da ta fito daga bakin mutanensa sai kawai suka ce: “Ku fitar da su daga garinku; lalle su mutane ne da suke nuna su masu tsarki ne.”
فَأَنجَيۡنَٰهُ وَأَهۡلَهُۥٓ إِلَّا ٱمۡرَأَتَهُۥ كَانَتۡ مِنَ ٱلۡغَٰبِرِينَ
Sai Muka tserar da shi da iyalansa, in ban da matarsa, ita ta kasance cikin waxanda suka rage (a cikin azaba)
وَأَمۡطَرۡنَا عَلَيۡهِم مَّطَرٗاۖ فَٱنظُرۡ كَيۡفَ كَانَ عَٰقِبَةُ ٱلۡمُجۡرِمِينَ
Sai Muka yi musu ruwan azaba; to duba ka ga yaya qarshen masu babban laifi ya kasance?
وَإِلَىٰ مَدۡيَنَ أَخَاهُمۡ شُعَيۡبٗاۚ قَالَ يَٰقَوۡمِ ٱعۡبُدُواْ ٱللَّهَ مَا لَكُم مِّنۡ إِلَٰهٍ غَيۡرُهُۥۖ قَدۡ جَآءَتۡكُم بَيِّنَةٞ مِّن رَّبِّكُمۡۖ فَأَوۡفُواْ ٱلۡكَيۡلَ وَٱلۡمِيزَانَ وَلَا تَبۡخَسُواْ ٱلنَّاسَ أَشۡيَآءَهُمۡ وَلَا تُفۡسِدُواْ فِي ٱلۡأَرۡضِ بَعۡدَ إِصۡلَٰحِهَاۚ ذَٰلِكُمۡ خَيۡرٞ لَّكُمۡ إِن كُنتُم مُّؤۡمِنِينَ
Kuma (Mun) aika wa mutanen Madyana xan’uwansu Shu’aibu, ya ce: “Ya ku mutanena, ku bauta wa Allah, ba ku da wani abin bauta wa da gaskiya sai Shi, haqiqa hujja ta zo muku daga Ubangijinku; don haka ku riqa cika mudu, kuma ku (kiyaye) ma’auni, kuma kada ku tauye wa mutane abubuwansu, kuma kada ku yi varna a bayan qasa bayan an gyara ta. Wannan shi ne mafi alheri a gare ku in kun kasance muminai
وَلَا تَقۡعُدُواْ بِكُلِّ صِرَٰطٖ تُوعِدُونَ وَتَصُدُّونَ عَن سَبِيلِ ٱللَّهِ مَنۡ ءَامَنَ بِهِۦ وَتَبۡغُونَهَا عِوَجٗاۚ وَٱذۡكُرُوٓاْ إِذۡ كُنتُمۡ قَلِيلٗا فَكَثَّرَكُمۡۖ وَٱنظُرُواْ كَيۡفَ كَانَ عَٰقِبَةُ ٱلۡمُفۡسِدِينَ
“Kuma kada ku zauna a kan kowace hanya kuna tsoratar da (mutane), kuma kuna toshe hanyar Allah ga duk wanda ya yi imani da Shi, kuna kuma son ta zama karkatacciya. Kuma ku tuna (ni’imar Allah) lokacin da kuke ‘yan kaxan, sai Ya yawaita ku, kuma ku duba ku ga yaya qarshen mavarnata ya kasance?
وَإِن كَانَ طَآئِفَةٞ مِّنكُمۡ ءَامَنُواْ بِٱلَّذِيٓ أُرۡسِلۡتُ بِهِۦ وَطَآئِفَةٞ لَّمۡ يُؤۡمِنُواْ فَٱصۡبِرُواْ حَتَّىٰ يَحۡكُمَ ٱللَّهُ بَيۡنَنَاۚ وَهُوَ خَيۡرُ ٱلۡحَٰكِمِينَ
“Idan kuma an sami wata qungiya daga cikinku sun yi imani da abin da aka aiko ni da shi, wata qungiyar kuma ba su yi imani ba, to ku yi haquri har Allah Ya yi hukunci a tsakaninmu. Kuma Shi ne Fiyayyen masu hukunci.”