وَإِذۡ أَخَذۡنَا مِيثَٰقَكُمۡ لَا تَسۡفِكُونَ دِمَآءَكُمۡ وَلَا تُخۡرِجُونَ أَنفُسَكُم مِّن دِيَٰرِكُمۡ ثُمَّ أَقۡرَرۡتُمۡ وَأَنتُمۡ تَشۡهَدُونَ
Kuma ku tuna lokacin da Muka xauki alqawari da ku cewa, ba za ku zubar da jinanenku ba, kuma ba za ku fitar da junanku daga gidajenku ba, sannan kuka tabbatar da hakan, alhalin kuna masu shaida
ثُمَّ أَنتُمۡ هَـٰٓؤُلَآءِ تَقۡتُلُونَ أَنفُسَكُمۡ وَتُخۡرِجُونَ فَرِيقٗا مِّنكُم مِّن دِيَٰرِهِمۡ تَظَٰهَرُونَ عَلَيۡهِم بِٱلۡإِثۡمِ وَٱلۡعُدۡوَٰنِ وَإِن يَأۡتُوكُمۡ أُسَٰرَىٰ تُفَٰدُوهُمۡ وَهُوَ مُحَرَّمٌ عَلَيۡكُمۡ إِخۡرَاجُهُمۡۚ أَفَتُؤۡمِنُونَ بِبَعۡضِ ٱلۡكِتَٰبِ وَتَكۡفُرُونَ بِبَعۡضٖۚ فَمَا جَزَآءُ مَن يَفۡعَلُ ذَٰلِكَ مِنكُمۡ إِلَّا خِزۡيٞ فِي ٱلۡحَيَوٰةِ ٱلدُّنۡيَاۖ وَيَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ يُرَدُّونَ إِلَىٰٓ أَشَدِّ ٱلۡعَذَابِۗ وَمَا ٱللَّهُ بِغَٰفِلٍ عَمَّا تَعۡمَلُونَ
Sannan sai ga ku, ku xin nan kuna kashe junanku, kuma kuna fitar da wata qungiya daga cikinku daga gidajensu, kuma kuna taimaka wa juna wajen cutar da su ta hanyar laifi da zalunci. Idan kuma sun zo muku suna kamammun yaqi sai ku fanshe su, alhali fitar da su haramun ne a gare ku. Yanzu kwa riqa yin imani da sashen Littafi kuma ku riqa kafircewa da wani sashen? To ba komai ne sakamakon wanda yake aikata haka daga cikinku ba face wani wulaqanci a rayuwar duniya, kuma ranar alqiyama a mayar da su zuwa ga mafi tsananin azaba, kuma Allah ba rafkananne ba ne game da abin da kuke aikatawa
أُوْلَـٰٓئِكَ ٱلَّذِينَ ٱشۡتَرَوُاْ ٱلۡحَيَوٰةَ ٱلدُّنۡيَا بِٱلۡأٓخِرَةِۖ فَلَا يُخَفَّفُ عَنۡهُمُ ٱلۡعَذَابُ وَلَا هُمۡ يُنصَرُونَ
Waxannan su ne waxanda suka musanya rayuwar duniya da ta lahira, kuma ba za a sassauta musu azaba ba, kuma ba za a taimaka musu ba
وَلَقَدۡ ءَاتَيۡنَا مُوسَى ٱلۡكِتَٰبَ وَقَفَّيۡنَا مِنۢ بَعۡدِهِۦ بِٱلرُّسُلِۖ وَءَاتَيۡنَا عِيسَى ٱبۡنَ مَرۡيَمَ ٱلۡبَيِّنَٰتِ وَأَيَّدۡنَٰهُ بِرُوحِ ٱلۡقُدُسِۗ أَفَكُلَّمَا جَآءَكُمۡ رَسُولُۢ بِمَا لَا تَهۡوَىٰٓ أَنفُسُكُمُ ٱسۡتَكۡبَرۡتُمۡ فَفَرِيقٗا كَذَّبۡتُمۡ وَفَرِيقٗا تَقۡتُلُونَ
Kuma haqiqa Mun ba wa Musa Littafi, kuma Muka biyo bayansa da manzanni, kuma Mun bai wa Isa xan Maryam hujjoji bayyananu, kuma Mun qarfafe shi da Ruhi mai tsarki. Ashe yanzu duk sa’adda wani manzo ya zo muku da abin da zukatanku ba sa so, sai ku yi girman kai, don haka sai ku qaryata wasu, kuma ku kashe wasu?
وَقَالُواْ قُلُوبُنَا غُلۡفُۢۚ بَل لَّعَنَهُمُ ٱللَّهُ بِكُفۡرِهِمۡ فَقَلِيلٗا مَّا يُؤۡمِنُونَ
Suka ce kuma: “Zukatanmu rufaffu ne.” A’a ba haka ba ne, Allah dai Ya la’ane su ne saboda kafircinsu, don haka kaxan ne waxanda suke yin imani
وَلَمَّا جَآءَهُمۡ كِتَٰبٞ مِّنۡ عِندِ ٱللَّهِ مُصَدِّقٞ لِّمَا مَعَهُمۡ وَكَانُواْ مِن قَبۡلُ يَسۡتَفۡتِحُونَ عَلَى ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ فَلَمَّا جَآءَهُم مَّا عَرَفُواْ كَفَرُواْ بِهِۦۚ فَلَعۡنَةُ ٱللَّهِ عَلَى ٱلۡكَٰفِرِينَ
Yayin da kuma wani littafi ya zo musu daga Allah, yana mai gaskata abin da yake tare da su, alhali kuma a da sun kasance suna addu’ar neman nasara a kan waxanda suka kafirta (mushrikai). To yayin da abin da suka sani ya zo musu sai suka kafirce masa[1]. Don haka la’anar Allah ta tabbata a kan kafirai
1- Kafin aiko Annabi Muhammadu (), idan faxa ya varke tsaknin Yahudu da Larabawa, Yahudu sukan ce, za a aiko wani annabi, idan ya bayyana za mu bi shi, mu haxa qarfi da shi mu yaqe ku. Yayin da Annabi () ya bayyana ba a cikinsu ba sai suka kafirce masa.
بِئۡسَمَا ٱشۡتَرَوۡاْ بِهِۦٓ أَنفُسَهُمۡ أَن يَكۡفُرُواْ بِمَآ أَنزَلَ ٱللَّهُ بَغۡيًا أَن يُنَزِّلَ ٱللَّهُ مِن فَضۡلِهِۦ عَلَىٰ مَن يَشَآءُ مِنۡ عِبَادِهِۦۖ فَبَآءُو بِغَضَبٍ عَلَىٰ غَضَبٖۚ وَلِلۡكَٰفِرِينَ عَذَابٞ مُّهِينٞ
Tir da wannan abu da suka sayar da kawunansu da shi, wato suka kafirce wa abin da Allah Ya saukar, don hassadar cewa, (don me) Allah zai saukar da falalarsa ga wanda Ya ga dama daga bayinsa, sai suka wayi gari da fushin Allah a kan wani fushin. Kuma azaba ta wulaqanci ta tabbata ga kafirai
وَإِذَا قِيلَ لَهُمۡ ءَامِنُواْ بِمَآ أَنزَلَ ٱللَّهُ قَالُواْ نُؤۡمِنُ بِمَآ أُنزِلَ عَلَيۡنَا وَيَكۡفُرُونَ بِمَا وَرَآءَهُۥ وَهُوَ ٱلۡحَقُّ مُصَدِّقٗا لِّمَا مَعَهُمۡۗ قُلۡ فَلِمَ تَقۡتُلُونَ أَنۢبِيَآءَ ٱللَّهِ مِن قَبۡلُ إِن كُنتُم مُّؤۡمِنِينَ
Idan aka ce da su: “Ku yi imani da abin da Allah Ya saukar”, sai su ce: “Mu muna yin imani ne da abin da aka saukar mana”. Kuma suna kafircewa da duk wani abu da ba shi ba, alhalin shi gaskiya ne, kuma mai gaskata abin da ke tare da su ne. To ka ce: “Me ya sa a da kuke kashe annabawan Allah idan kun kasance muminai?”
۞وَلَقَدۡ جَآءَكُم مُّوسَىٰ بِٱلۡبَيِّنَٰتِ ثُمَّ ٱتَّخَذۡتُمُ ٱلۡعِجۡلَ مِنۢ بَعۡدِهِۦ وَأَنتُمۡ ظَٰلِمُونَ
Haqiqa Musa ya zo muka da hujjoji bayyanannu, sannan kuka bauta wa xan maraqi bayansa alhalin kuna azzalumai
وَإِذۡ أَخَذۡنَا مِيثَٰقَكُمۡ وَرَفَعۡنَا فَوۡقَكُمُ ٱلطُّورَ خُذُواْ مَآ ءَاتَيۡنَٰكُم بِقُوَّةٖ وَٱسۡمَعُواْۖ قَالُواْ سَمِعۡنَا وَعَصَيۡنَا وَأُشۡرِبُواْ فِي قُلُوبِهِمُ ٱلۡعِجۡلَ بِكُفۡرِهِمۡۚ قُلۡ بِئۡسَمَا يَأۡمُرُكُم بِهِۦٓ إِيمَٰنُكُمۡ إِن كُنتُم مُّؤۡمِنِينَ
Kuma ku tuna lokacin da Muka xauki alqawari da ku, Muka kuma xaga dutsen Xuri a kanku, Muka ce: “Ku riqi abin da muka ba ku da qarfi, kuma ku saurara”. Sai suka ce: “Mun ji kuma mun sava”. Kuma aka sanya musu tsananin son bautar xan maraqi a zukatansu saboda kafircinsu. Ka ce: “Tir da abin da imaninku yake umartar ku da shi, idan har kun kasance muminai.”
قُلۡ إِن كَانَتۡ لَكُمُ ٱلدَّارُ ٱلۡأٓخِرَةُ عِندَ ٱللَّهِ خَالِصَةٗ مِّن دُونِ ٱلنَّاسِ فَتَمَنَّوُاْ ٱلۡمَوۡتَ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ
Ka ce: “Idan gidan lahira ya kasance kevantacce a gare ku a wurin Allah ku kaxai ban da sauran mutane, to ku yi burin mutuwa idan har ku masu gaskiya ne.”
وَلَن يَتَمَنَّوۡهُ أَبَدَۢا بِمَا قَدَّمَتۡ أَيۡدِيهِمۡۚ وَٱللَّهُ عَلِيمُۢ بِٱلظَّـٰلِمِينَ
Ba za su tava burin mutuwa ba har abada, saboda abin da hannayensu suka aikata. Kuma Allah Masani ne ga azzalumai
وَلَتَجِدَنَّهُمۡ أَحۡرَصَ ٱلنَّاسِ عَلَىٰ حَيَوٰةٖ وَمِنَ ٱلَّذِينَ أَشۡرَكُواْۚ يَوَدُّ أَحَدُهُمۡ لَوۡ يُعَمَّرُ أَلۡفَ سَنَةٖ وَمَا هُوَ بِمُزَحۡزِحِهِۦ مِنَ ٱلۡعَذَابِ أَن يُعَمَّرَۗ وَٱللَّهُ بَصِيرُۢ بِمَا يَعۡمَلُونَ
Kuma lalle za ka same su sun fi kowa kwaxayin tsawon rai, fiye ma da waxanda suka yi shirka. Kowane xayansu yana burin ina ma za a raya shi shekara dubu. Hakan kuma ba zai nesanta shi daga azaba ba don an yi masa tsawon rai. Kuma Allah Mai ganin abin da suka kasance suna aikatawa ne
قُلۡ مَن كَانَ عَدُوّٗا لِّـجِبۡرِيلَ فَإِنَّهُۥ نَزَّلَهُۥ عَلَىٰ قَلۡبِكَ بِإِذۡنِ ٱللَّهِ مُصَدِّقٗا لِّمَا بَيۡنَ يَدَيۡهِ وَهُدٗى وَبُشۡرَىٰ لِلۡمُؤۡمِنِينَ
Ka ce: “Duk wanda ya kasance maqiyi ne ga (Mala’ika) Jibrilu[1], to lalle shi ne ya saukar da shi (Alqur’ani) a kan zuciyarka da izinin Allah yana mai gaskata abin da ya gabace shi (na littattafai), kuma shiriya ne da bushara ga muminai.”
1- Yahudawa sun faxa wa Annabi cewa, Mala'ika Jibrilu maqiyinsu ne, wai domin shi ne yake saukowa da yaqi da kashe-kashe da azaba.
مَن كَانَ عَدُوّٗا لِّلَّهِ وَمَلَـٰٓئِكَتِهِۦ وَرُسُلِهِۦ وَجِبۡرِيلَ وَمِيكَىٰلَ فَإِنَّ ٱللَّهَ عَدُوّٞ لِّلۡكَٰفِرِينَ
Duk wanda ya kasance maqiyi ne ga Allah da mala’ikunsa da manzanninsa da Jibrilu da Mika’ilu, to lalle Allah maqiyin kafirai ne
وَلَقَدۡ أَنزَلۡنَآ إِلَيۡكَ ءَايَٰتِۭ بَيِّنَٰتٖۖ وَمَا يَكۡفُرُ بِهَآ إِلَّا ٱلۡفَٰسِقُونَ
Kuma haqiqa Mun saukar maka da ayoyi bayyanannu, babu kuma mai kafirce musu sai fasiqai
أَوَكُلَّمَا عَٰهَدُواْ عَهۡدٗا نَّبَذَهُۥ فَرِيقٞ مِّنۡهُمۚ بَلۡ أَكۡثَرُهُمۡ لَا يُؤۡمِنُونَ
Yanzu ashe duk sa’adda suka qulla wani alqawari sai wani vangare daga cikinsu ya yi watsi da shi?! Bari! Yawancinsu ba sa yin imani
وَلَمَّا جَآءَهُمۡ رَسُولٞ مِّنۡ عِندِ ٱللَّهِ مُصَدِّقٞ لِّمَا مَعَهُمۡ نَبَذَ فَرِيقٞ مِّنَ ٱلَّذِينَ أُوتُواْ ٱلۡكِتَٰبَ كِتَٰبَ ٱللَّهِ وَرَآءَ ظُهُورِهِمۡ كَأَنَّهُمۡ لَا يَعۡلَمُونَ
Yayin da wani manzo daga Allah ya zo musu yana mai gaskata abin da yake tare da su (na Littafin Attaura), sai wani vangare daga cikinsu suka jefar da littafin Allah a bayansu kamar ba su san komai ba
وَٱتَّبَعُواْ مَا تَتۡلُواْ ٱلشَّيَٰطِينُ عَلَىٰ مُلۡكِ سُلَيۡمَٰنَۖ وَمَا كَفَرَ سُلَيۡمَٰنُ وَلَٰكِنَّ ٱلشَّيَٰطِينَ كَفَرُواْ يُعَلِّمُونَ ٱلنَّاسَ ٱلسِّحۡرَ وَمَآ أُنزِلَ عَلَى ٱلۡمَلَكَيۡنِ بِبَابِلَ هَٰرُوتَ وَمَٰرُوتَۚ وَمَا يُعَلِّمَانِ مِنۡ أَحَدٍ حَتَّىٰ يَقُولَآ إِنَّمَا نَحۡنُ فِتۡنَةٞ فَلَا تَكۡفُرۡۖ فَيَتَعَلَّمُونَ مِنۡهُمَا مَا يُفَرِّقُونَ بِهِۦ بَيۡنَ ٱلۡمَرۡءِ وَزَوۡجِهِۦۚ وَمَا هُم بِضَآرِّينَ بِهِۦ مِنۡ أَحَدٍ إِلَّا بِإِذۡنِ ٱللَّهِۚ وَيَتَعَلَّمُونَ مَا يَضُرُّهُمۡ وَلَا يَنفَعُهُمۡۚ وَلَقَدۡ عَلِمُواْ لَمَنِ ٱشۡتَرَىٰهُ مَا لَهُۥ فِي ٱلۡأٓخِرَةِ مِنۡ خَلَٰقٖۚ وَلَبِئۡسَ مَا شَرَوۡاْ بِهِۦٓ أَنفُسَهُمۡۚ لَوۡ كَانُواْ يَعۡلَمُونَ
Sai suka bi abin da shexanu suke karantawa a (zamanin) mulkin Sulaimanu; kuma Sulaimanu bai kafirta ba, sai dai shexanun su ne suka kafirta; suna koya wa mutane tsafi da abin da aka saukar wa mala’iku biyu, Haruta da Maruta, a garin Babila. Kuma ba sa koya wa wani (tsafin) har sai sun faxa masa cewa: “Mu fa jarraba ce, don haka kada ka kafirta”. Sai (mutane) suka riqa koyo daga wajensu su biyu abin da suke raba tsakanin miji da matarsa da shi. Kuma ba za su iya cutar da wani da shi ba sai da izinin Allah. Sai su koyi abin da zai cutar da su kuma ba zai amfane su ba. Kuma haqiqa sun san cewa, tabbas duk wanda ya zavi (sihiri) ba shi da wani rabo a lahira. Kuma lalle tir da abin da suka sayar da kawunansu da shi, da a ce sun san (haqiqanin makomarsu)
وَلَوۡ أَنَّهُمۡ ءَامَنُواْ وَٱتَّقَوۡاْ لَمَثُوبَةٞ مِّنۡ عِندِ ٱللَّهِ خَيۡرٞۚ لَّوۡ كَانُواْ يَعۡلَمُونَ
Da a ce su sun yi imani kuma sun yi taqawa, haqiqa da sakamakon (da za su samu) daga Allah shi ne mafi alheri, da a ce sun sani
يَـٰٓأَيُّهَا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ لَا تَقُولُواْ رَٰعِنَا وَقُولُواْ ٱنظُرۡنَا وَٱسۡمَعُواْۗ وَلِلۡكَٰفِرِينَ عَذَابٌ أَلِيمٞ
Ya ku waxanda suka yi imani kada ku ce, ra’ina, (watau kula da mu), sai dai ku ce, dakata mana[1], kuma ku saurara. Kafirai kuma suna da wata azaba mai raxaxi
1- Sahabban Annabi () sun kasance idan yana biya musu karatu sukan nemi ya xan dakata musu kaxan domin su fahimta sosai, to sai sukan yi amfani da kalmar ‘ra’ina’. A harshen Yahudawa kuma kalmar tana kusa da wata kalma da take da ma’anar ‘daqiqi’, to sai su ma suka riqa fakewa da wannan kalmar suna zagin Annabi (). Sai Allah ya hana sahabbai amfani da kalmar, a maimakonta ya ce su yi amfani da kalmar ‘unzurna’ wadda take nufin ‘dakata mana’.
مَّا يَوَدُّ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ مِنۡ أَهۡلِ ٱلۡكِتَٰبِ وَلَا ٱلۡمُشۡرِكِينَ أَن يُنَزَّلَ عَلَيۡكُم مِّنۡ خَيۡرٖ مِّن رَّبِّكُمۡۚ وَٱللَّهُ يَخۡتَصُّ بِرَحۡمَتِهِۦ مَن يَشَآءُۚ وَٱللَّهُ ذُو ٱلۡفَضۡلِ ٱلۡعَظِيمِ
Waxanda suka kafirta daga ma’abota littafi da mushrikai ba sa qaunar a saukar muku da wani alheri daga Ubangijinku, sai dai Allah kuwa Yana kevance wanda Ya ga dama da rahamarsa, Allah kuma Mai babbar falala ne
۞مَا نَنسَخۡ مِنۡ ءَايَةٍ أَوۡ نُنسِهَا نَأۡتِ بِخَيۡرٖ مِّنۡهَآ أَوۡ مِثۡلِهَآۗ أَلَمۡ تَعۡلَمۡ أَنَّ ٱللَّهَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٌ
Babu wata aya da za Mu shafe ko Mu mantar da kai ita, sai Mun kawo wadda ta fi ta alheri ko kwatankwacinta. Ashe ba ka san cewa, lalle Allah Mai iko ne a kan komai ba?
أَلَمۡ تَعۡلَمۡ أَنَّ ٱللَّهَ لَهُۥ مُلۡكُ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِۗ وَمَا لَكُم مِّن دُونِ ٱللَّهِ مِن وَلِيّٖ وَلَا نَصِيرٍ
Kuma ba ka sani ba cewa, lalle mulkin sammai da qasa na Allah ne, kuma ba ku da wani majivinci ko wani mai taimako ba Allah ba?
أَمۡ تُرِيدُونَ أَن تَسۡـَٔلُواْ رَسُولَكُمۡ كَمَا سُئِلَ مُوسَىٰ مِن قَبۡلُۗ وَمَن يَتَبَدَّلِ ٱلۡكُفۡرَ بِٱلۡإِيمَٰنِ فَقَدۡ ضَلَّ سَوَآءَ ٱلسَّبِيلِ
Ko kuma kuna nufin za ku tambayi Manzonku kamar yadda aka yi wa Musa tambaya a da? Kuma duk wanda ya canza imani da kafirci to haqiqa ya vace wa hanya tsakatsakiya
وَدَّ كَثِيرٞ مِّنۡ أَهۡلِ ٱلۡكِتَٰبِ لَوۡ يَرُدُّونَكُم مِّنۢ بَعۡدِ إِيمَٰنِكُمۡ كُفَّارًا حَسَدٗا مِّنۡ عِندِ أَنفُسِهِم مِّنۢ بَعۡدِ مَا تَبَيَّنَ لَهُمُ ٱلۡحَقُّۖ فَٱعۡفُواْ وَٱصۡفَحُواْ حَتَّىٰ يَأۡتِيَ ٱللَّهُ بِأَمۡرِهِۦٓۗ إِنَّ ٱللَّهَ عَلَىٰ كُلِّ شَيۡءٖ قَدِيرٞ
Da yawa daga cikin ma’abota littafi sun yi burin ina ma a ce su mayar da ku kafirai bayan imaninku, saboda hassada daga zukatansu, bayan kuma gaskiya ta bayyana a gare su. Don haka ku yi afuwa ku kawar da kai har sai Allah Ya zo da al’amarinsa. Lalle Allah Mai iko ne a kan komai
وَأَقِيمُواْ ٱلصَّلَوٰةَ وَءَاتُواْ ٱلزَّكَوٰةَۚ وَمَا تُقَدِّمُواْ لِأَنفُسِكُم مِّنۡ خَيۡرٖ تَجِدُوهُ عِندَ ٱللَّهِۗ إِنَّ ٱللَّهَ بِمَا تَعۡمَلُونَ بَصِيرٞ
Kuma ku tsayar da salla ku kuma ba da zakka; kuma duk abin da kuka aikata na alheri domin kawunanku za ku same shi a wajen Allah. Lalle Allah Mai ganin abin da kuke aikatawa ne
وَقَالُواْ لَن يَدۡخُلَ ٱلۡجَنَّةَ إِلَّا مَن كَانَ هُودًا أَوۡ نَصَٰرَىٰۗ تِلۡكَ أَمَانِيُّهُمۡۗ قُلۡ هَاتُواْ بُرۡهَٰنَكُمۡ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ
Kuma (Yahudawa da Nasara) suka ce: “Babu mai shiga Aljanna sai wanda ya kasance Bayahude ko Banasare”. Waxannan burace-buracensu ne. Ka ce: “Ku kawo hujjarku idan kun kasance masu gaskiya”
بَلَىٰۚ مَنۡ أَسۡلَمَ وَجۡهَهُۥ لِلَّهِ وَهُوَ مُحۡسِنٞ فَلَهُۥٓ أَجۡرُهُۥ عِندَ رَبِّهِۦ وَلَا خَوۡفٌ عَلَيۡهِمۡ وَلَا هُمۡ يَحۡزَنُونَ
E! Wanda ya miqa fuskarsa ga Allah alhali yana mai kyautata aikinsa, to yana da ladansa a wajen Ubangijinsa, kuma babu tsoro a tare da su kuma ba za su yi baqin ciki ba
وَقَالَتِ ٱلۡيَهُودُ لَيۡسَتِ ٱلنَّصَٰرَىٰ عَلَىٰ شَيۡءٖ وَقَالَتِ ٱلنَّصَٰرَىٰ لَيۡسَتِ ٱلۡيَهُودُ عَلَىٰ شَيۡءٖ وَهُمۡ يَتۡلُونَ ٱلۡكِتَٰبَۗ كَذَٰلِكَ قَالَ ٱلَّذِينَ لَا يَعۡلَمُونَ مِثۡلَ قَوۡلِهِمۡۚ فَٱللَّهُ يَحۡكُمُ بَيۡنَهُمۡ يَوۡمَ ٱلۡقِيَٰمَةِ فِيمَا كَانُواْ فِيهِ يَخۡتَلِفُونَ
Yahudawa suka ce: “Nasara ba a kan komai suke ba”, su ma Nasara suka ce: “Yahudawa ba a kan komai suke ba”, alhalin dukkansu suna karanta Littafi. Kamar haka ne waxanda ba su da ilimi suka yi irin maganarsu. Kuma Allah zai yi hukunci a tsakaninsu ranar Alqiyama a kan abin da suka kasance suna savani a cikinsa