Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 10

وَفِرۡعَوۡنَ ذِي ٱلۡأَوۡتَادِ

Da kuma Fir’auna ma’abocin turaku



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 11

ٱلَّذِينَ طَغَوۡاْ فِي ٱلۡبِلَٰدِ

Waxanda suka yi xagawa a cikin garuruwa



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 12

فَأَكۡثَرُواْ فِيهَا ٱلۡفَسَادَ

Suka kuma yawaita varna a cikinsu



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 13

فَصَبَّ عَلَيۡهِمۡ رَبُّكَ سَوۡطَ عَذَابٍ

Sai Ubangijinka Ya saukar musu azaba mai tsanani



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 14

إِنَّ رَبَّكَ لَبِٱلۡمِرۡصَادِ

Lalle Ubangijinka tabbas Yana nan a madakata[1]


1- Watau yana wurin da yake hangen xaukacin ayyukan bayinsa.


Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 15

فَأَمَّا ٱلۡإِنسَٰنُ إِذَا مَا ٱبۡتَلَىٰهُ رَبُّهُۥ فَأَكۡرَمَهُۥ وَنَعَّمَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّيٓ أَكۡرَمَنِ

Amma kuma mutum idan Ubangijinsa Ya jarrabe shi sai Ya karrama shi, Ya kuma yi masa ni’ima, sai ya ce: “Ubangijina Ya karrama ni.”



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 16

وَأَمَّآ إِذَا مَا ٱبۡتَلَىٰهُ فَقَدَرَ عَلَيۡهِ رِزۡقَهُۥ فَيَقُولُ رَبِّيٓ أَهَٰنَنِ

Amma kuma idan Ya jarrabe shi sai Ya quntata masa a arzikinsa, sai ya ce: “Ubangijina Ya wulaqanta ni.”



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 17

كَلَّاۖ بَل لَّا تُكۡرِمُونَ ٱلۡيَتِيمَ

Faufau, ba haka ba ne; ku ba kwa karrama maraya ne



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 18

وَلَا تَحَـٰٓضُّونَ عَلَىٰ طَعَامِ ٱلۡمِسۡكِينِ

Kuma ba kwa kwaxaitar da juna kan ciyar da miskinai



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 19

وَتَأۡكُلُونَ ٱلتُّرَاثَ أَكۡلٗا لَّمّٗا

Kuma kuna cinye dukiyar gadon marayu mummunan ci



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 20

وَتُحِبُّونَ ٱلۡمَالَ حُبّٗا جَمّٗا

Kuma kuna son dukiya so mai yawa



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 21

كَلَّآۖ إِذَا دُكَّتِ ٱلۡأَرۡضُ دَكّٗا دَكّٗا

Ba haka ne ba, idan aka girgiza qasa matuqar girgiza



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 22

وَجَآءَ رَبُّكَ وَٱلۡمَلَكُ صَفّٗا صَفّٗا

Ubangijinka kuma Ya zo[1] tare da mala’iku sahu-sahu


1- Watau don yin hukunci a tsakanin bayinsa.


Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 23

وَجِاْيٓءَ يَوۡمَئِذِۭ بِجَهَنَّمَۚ يَوۡمَئِذٖ يَتَذَكَّرُ ٱلۡإِنسَٰنُ وَأَنَّىٰ لَهُ ٱلذِّكۡرَىٰ

Aka kuma zo da Jahannama a wannan ranar. To fa a wannan ranar ne mutum zai tuna (sakacinsa), ta yaya wannan tunawar za ta yi masa amfani?



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 24

يَقُولُ يَٰلَيۡتَنِي قَدَّمۡتُ لِحَيَاتِي

Zai ce: “Kaitona, ina ma da na gabatar (da ayyukan alheri) a rayuwata!”



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 25

فَيَوۡمَئِذٖ لَّا يُعَذِّبُ عَذَابَهُۥٓ أَحَدٞ

To a wannan ranar ba wani xaya da zai yi azaba irin azabarsa (watau Allah)



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 26

وَلَا يُوثِقُ وَثَاقَهُۥٓ أَحَدٞ

Ba kuma xaya da zai yi xauri irin xaurinsa



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 27

يَـٰٓأَيَّتُهَا ٱلنَّفۡسُ ٱلۡمُطۡمَئِنَّةُ

(Za a ce): Ya kai wannan rai mai nutsuwa



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 28

ٱرۡجِعِيٓ إِلَىٰ رَبِّكِ رَاضِيَةٗ مَّرۡضِيَّةٗ

Ka koma zuwa ga Ubangijinka kana mai yarda (da sakamako), abin yarda



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 29

فَٱدۡخُلِي فِي عِبَٰدِي

Don haka ka shiga cikin bayina



Capítulo: Suratul Fajr

Verso : 30

وَٱدۡخُلِي جَنَّتِي

Ka kuma shiga Aljannata



Capítulo: Suratul Balad

Verso : 1

لَآ أُقۡسِمُ بِهَٰذَا ٱلۡبَلَدِ

Na rantse da wannan gari (na Makka)



Capítulo: Suratul Balad

Verso : 2

وَأَنتَ حِلُّۢ بِهَٰذَا ٱلۡبَلَدِ

Alhali kuwa kai an halatta maka wannan gari[1]


1- Watau an halatta masa kashe wanda ya cancanci kisa a garin Makka. Ko kuma ana nufin Allah ya yi rantsuwa da Makka musamman lokacin da Annabi () yake zaune a cikinta.


Capítulo: Suratul Balad

Verso : 3

وَوَالِدٖ وَمَا وَلَدَ

(Na rantse) da mahaifi da abin da ya haifa[1]


1- Watau Annabi Adamu () da zurriyarsa. Ko kuma duk wani mahaifi da duk wani wanda aka haifa.


Capítulo: Suratul Balad

Verso : 4

لَقَدۡ خَلَقۡنَا ٱلۡإِنسَٰنَ فِي كَبَدٍ

Haqiqa Mun halicci mutum cikin wahala



Capítulo: Suratul Balad

Verso : 5

أَيَحۡسَبُ أَن لَّن يَقۡدِرَ عَلَيۡهِ أَحَدٞ

Yanzu mutum yana tsammanin cewa wani ba zai sami iko a kansa ba?



Capítulo: Suratul Balad

Verso : 6

يَقُولُ أَهۡلَكۡتُ مَالٗا لُّبَدًا

Yana cewa: “Na vatar da dukiya mai ximbin yawa.”



Capítulo: Suratul Balad

Verso : 7

أَيَحۡسَبُ أَن لَّمۡ يَرَهُۥٓ أَحَدٌ

Shin yana tsammanin cewa ba wanda ya gan shi?



Capítulo: Suratul Balad

Verso : 8

أَلَمۡ نَجۡعَل لَّهُۥ عَيۡنَيۡنِ

Shin ba Mu sanya masa idanuwa biyu ba ne?



Capítulo: Suratul Balad

Verso : 9

وَلِسَانٗا وَشَفَتَيۡنِ

Da harshe da kuma lavva biyu?